Gwamnatin Zamfara Ta Yaba Da Cigaban Ayyukan Tituna A Jihar
Published: 11th, April 2025 GMT
Gwamnatin jihar Zamfara ta bayyana gamsuwarta da yadda ake ci gaba da gudanar da ayyukan gina tituna da gyare-gyare a fadin jihar.
Kwamishinan ayyuka da samar da ababen more rayuwa na jihar Alhaji Lawal Barau Bungudu ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Gusau babban birnin jihar.
Alhaji Lawal Barau Bungudu ya bayyana cewa, tun bayan hawan Gwamna Dauda Lawal mulki, gwamnatin ta ba da fifiko wajen samar da ababen more rayuwa, musamman gine-gine da sake gina tituna, a wani bangare na babban shirinta na sabunta birane da nufin kawo sauyi a jihar da kuma saukaka zirga-zirgar ababen hawa.
Ya ce gwamnatin jihar ta dukufa wajen fadada hanyoyin jihar domin ingantawa da bunkasa harkokin tattalin arziki, inda ya bayyana cewa ana gudanar da ayyukan da ake gudanarwa a daidai lokacin da aka amince da su.
Alhaji Lawal Barau Bungudu ya kuma bayyana cewa, an riga an kammala ayyukan tituna da dama, yayin da wasu da dama kuma suke mataki daban-daban na kammala su.
Ya ba da tabbacin cewa, gwamnatin jihar za ta ci gaba da sanya ido a kan ci gaban da aka samu don tabbatar da isar da kayayyakin aiki a kan lokaci ba tare da tsaiko ba.
Kwamishinan ya jaddada cewa, gwamnatin jihar Zamfara ta mayar da hankali wajen gyara tsofaffin tituna, da suka lalace da kuma gina sabbi domin bude yankunan karkara da birane.
Alhaji Barau Bungudu ya yi nuni da cewa, ana aiwatar da dukkanin ayyukan tituna da ake yi tare da bin ka’ida mai inganci, yana mai jaddada cewa, ‘yan kwangilar an ba su aikin samar da ababen more rayuwa masu dorewa da za su tsaya tsayin daka.
Ya yi kira ga mazauna yankin da su goyi bayan kokarin gwamnati ta hanyar kiyaye ababen more rayuwa da kuma hada kai da ‘yan kwangila a yayin gudanar da ayyukan.
Kwamishinan ya nanata kudirin gwamnatin na mayar da jihar Zamfara abin koyi wajen samar da ababen more rayuwa a yankin Arewa maso Yamma.
COV/AMINU DALHATU
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Zamfara samar da ababen more rayuwa gwamnatin jihar Barau Bungudu
এছাড়াও পড়ুন:
Rikicin ADC: Sanata Nenadi ta zama shugaba a Kaduna
Rikicin Jam’iyyar ADC na Jihar Kaduna ya ɗauki sabon salo, bayan da uwar jam’iyyar ta nada tsohuwar Ministar Kuɗi, Sanata Nenadi Usman, a matsayin Shugabar Hadakar Jam’iyyar a jihar.
Haka kuma jam’iyyar ta nada tsohon Kwamishinan Kudi na Jihar Kaduna, Bashir Sa’idu, na hannun daman tsohon gwamnan jihar, Mallam Nasir El-Rufa’i, a matsayin Mataimakin Shugaban Haɗakar.
Da yake jawabi yayin taron manema labarai, Mataimakin Shugaban Jam’iyyar na Kasa (Arewa maso Yamma), Ja’afaru Sani, ya bayyana cewa manufar ADC ita ce haɗa kan shugabannin jam’iyyun adawa a Kaduna domin ƙarfafa dimokuradiyya da shigar kowa cikin harkokin siyasa.
Ya ce shugabannin Haɗakar sun ƙuduri aniyar sake farfaɗo da jam’iyyar da kuma haɗa kan jama’a don kawo ƙarshen abin da ya kira “mulkin danniya na Jam’iyyar APC a jihar da ƙasa baki ɗaya.”
Tinubu ya gana da sabbin hafsoshin tsaro Alassane Ouattara ya lashe zaɓen Ivory Coast karo na huɗu“A bisa wannan tsari na sake gina jam’iyyar da samar da shugabanci mai tsari, mun tabbatar da naɗin Sanata Nenadi Usman a matsayin Shugabar Hadakar ADC a Jihar Kaduna, tare da Alhaji Bashir Sa’idu a matsayin Mataimakinta.
“Da wannan mataki, ita ce za ta zama ginshiƙin hada kai da shirya ayyukan Haɗakar jam’iyyar a jihar,” in ji shi.
Ja’afaru Sani ya zargi jam’iyyar APC mai mulki da ƙoƙarin raba kawunan shugabannin jam’iyyun adawa a jihar, amma ya ce ADC za ta tsaya tsayin daka wajen kare haɗin kanta.
“Mun lura cewa a ƙoƙarinsu na kawo rabuwar kai, wasu ’yan siyasa da ake amfani da su sun ɗauki nauyin wasu mutane don kai ƙara kotu a kan wasu shugabannin Haɗakar, ciki har da Mallam Nasir El-Rufa’i da ni kaina,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa, shugabannin Haɗakar sun cimma matsaya ɗaya ta kora da hana shiga ayyukan jam’iyya ga dukkan mambobin da ke da hannu ƙarar da aka shigar a kotu kan El-Rufa’i da sauran shugabannin jam’iyyar.