Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-11-26@05:11:27 GMT

Gwamnatin Zamfara Ta Yaba Da Cigaban Ayyukan Tituna A Jihar

Published: 11th, April 2025 GMT

Gwamnatin Zamfara Ta Yaba Da Cigaban Ayyukan Tituna A Jihar

Gwamnatin jihar Zamfara ta bayyana gamsuwarta da yadda ake ci gaba da gudanar da ayyukan gina tituna da gyare-gyare a fadin jihar.

 

Kwamishinan ayyuka da samar da ababen more rayuwa na jihar Alhaji Lawal Barau Bungudu ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Gusau babban birnin jihar.

 

Alhaji Lawal Barau Bungudu ya bayyana cewa, tun bayan hawan Gwamna Dauda Lawal mulki, gwamnatin ta ba da fifiko wajen samar da ababen more rayuwa, musamman gine-gine da sake gina tituna, a wani bangare na babban shirinta na sabunta birane da nufin kawo sauyi a jihar da kuma saukaka zirga-zirgar ababen hawa.

 

Ya ce gwamnatin jihar ta dukufa wajen fadada hanyoyin jihar domin ingantawa da bunkasa harkokin tattalin arziki, inda ya bayyana cewa ana gudanar da ayyukan da ake gudanarwa a daidai lokacin da aka amince da su.

 

Alhaji Lawal Barau Bungudu ya kuma bayyana cewa, an riga an kammala ayyukan tituna da dama, yayin da wasu da dama kuma suke mataki daban-daban na kammala su.

 

Ya ba da tabbacin cewa, gwamnatin jihar za ta ci gaba da sanya ido a kan ci gaban da aka samu don tabbatar da isar da kayayyakin aiki a kan lokaci ba tare da tsaiko ba.

 

Kwamishinan ya jaddada cewa, gwamnatin jihar Zamfara ta mayar da hankali wajen gyara tsofaffin tituna, da suka lalace da kuma gina sabbi domin bude yankunan karkara da birane.

 

Alhaji Barau Bungudu ya yi nuni da cewa, ana aiwatar da dukkanin ayyukan tituna da ake yi tare da bin ka’ida mai inganci, yana mai jaddada cewa, ‘yan kwangilar an ba su aikin samar da ababen more rayuwa masu dorewa da za su tsaya tsayin daka.

 

Ya yi kira ga mazauna yankin da su goyi bayan kokarin gwamnati ta hanyar kiyaye ababen more rayuwa da kuma hada kai da ‘yan kwangila a yayin gudanar da ayyukan.

 

Kwamishinan ya nanata kudirin gwamnatin na mayar da jihar Zamfara abin koyi wajen samar da ababen more rayuwa a yankin Arewa maso Yamma.

 

COV/AMINU DALHATU

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Zamfara samar da ababen more rayuwa gwamnatin jihar Barau Bungudu

এছাড়াও পড়ুন:

An rufe duk makarantu a Kebbi

Gwamnatin Jihar Kebbi ta ba da umarnin rufe dukkan makarantun sakandire na gwamnati da na masu zaman kansu nan take.

Haka kuma, gwamnatin ta rufe dukkan manyan makarantun gaba da sakandire a faɗin jihar, banda Kwalejin Nazarin Aikin Jinya da Ungozoma da ke Birnin Kebbi.

An gano wurin da ’yan bindiga ke tsare da ɗalibai 25 da aka sace a Kebbi Ma’aikatan lantarki na shirin shiga yajin aiki a faɗin Najeriya 

Wannan dai na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da Kwamishinan Ilimi na manyan makarantu, Alhaji Issa Abubakar-Tunga, tare da Kwamishiyar Ilimin Firamare da Sakandare, Dokta Halima Bande, suka fitar a Birnin Kebbi, ranar Lahadi.

Sanarwar ta ce an ɗauki wannan mataki ne sakamakon barazanar hare-haren da ake samu a wasu sassan jihar a kwanakin nan.

Manyan makarantu da abin ya shafa sun haɗa da Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Dakingari, Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Kebbi (KSUSTA) da ke Aliero, Kwalejin Kiwon Lafiya ta Jega, da kuma Kwalejin Ilimi ta Argungu.

Sanarwar ta ce Kwalejin Nazarin Aikin Jinya da Ungozoma da ke Birnin Kebbi ba ta cikin jerin makarantun da aka rufe.

Gwamnati ta buƙaci hukumomin dukkan makarantun da su yi wa wannan umarni biyayya, tare da kwantar da hankalin al’umma, tana mai bayyana cewa nan gaba kaɗan za a ayyana ranar komawa makarantun da zarar komai ya daidaita.

Aminiya ta ruwaito yadda a bayan nan jihohi da dama musamman a Arewacin suka bayar da umarnin rufe makarantu saboda fargabar matsalar tsaro da ake ci gaba da samu a kwanakin nan.

Wasu daga cikin jihohin da suka rufe makarantu sun haɗa da Kwara, Neja, Katsina, Taraba, Yobe da kuma Filato.

Wannan dai na zuwa ne bayan ’yan bindiga sun sace ɗalibai 25 a wata Makarantar Sakandire ta Maga da ke Jihar Kebbi.

Sai kuma harin da aka samu a wani coci da ke Jihar Kwara da kuma sace fiye da ɗalibai 300 da ’yan ta’adda suka yi a wata makarantar St Mary da ke Jihar Neja.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Yi Wa Yara Miliyan 1.5 Rigakafin Cutar Shan Inna
  • An buɗe wasu makarantu domin ci gaba da jarawaba a Katsina
  • An rufe duk makarantu a Jihar Bauchi saboda matsalar tsaro
  • Matsalar tsaro: Gwamnatin Yobe ta rufe duk makarantun sakandaren kwana
  • An rufe duk makarantu a Jihar Bauchi na saboda matsalar tsaro
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 162
  • An ceto mutum 38 da aka sace a cocin Kwara — Tinubu
  • Gwamnatin Kebbi Ta Bayar da Umarnin Rufe Makarantu a Jihar
  • An rufe duk makarantu a Kebbi
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 161