Gwamnatin Zamfara Ta Yaba Da Cigaban Ayyukan Tituna A Jihar
Published: 11th, April 2025 GMT
Gwamnatin jihar Zamfara ta bayyana gamsuwarta da yadda ake ci gaba da gudanar da ayyukan gina tituna da gyare-gyare a fadin jihar.
Kwamishinan ayyuka da samar da ababen more rayuwa na jihar Alhaji Lawal Barau Bungudu ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Gusau babban birnin jihar.
Alhaji Lawal Barau Bungudu ya bayyana cewa, tun bayan hawan Gwamna Dauda Lawal mulki, gwamnatin ta ba da fifiko wajen samar da ababen more rayuwa, musamman gine-gine da sake gina tituna, a wani bangare na babban shirinta na sabunta birane da nufin kawo sauyi a jihar da kuma saukaka zirga-zirgar ababen hawa.
Ya ce gwamnatin jihar ta dukufa wajen fadada hanyoyin jihar domin ingantawa da bunkasa harkokin tattalin arziki, inda ya bayyana cewa ana gudanar da ayyukan da ake gudanarwa a daidai lokacin da aka amince da su.
Alhaji Lawal Barau Bungudu ya kuma bayyana cewa, an riga an kammala ayyukan tituna da dama, yayin da wasu da dama kuma suke mataki daban-daban na kammala su.
Ya ba da tabbacin cewa, gwamnatin jihar za ta ci gaba da sanya ido a kan ci gaban da aka samu don tabbatar da isar da kayayyakin aiki a kan lokaci ba tare da tsaiko ba.
Kwamishinan ya jaddada cewa, gwamnatin jihar Zamfara ta mayar da hankali wajen gyara tsofaffin tituna, da suka lalace da kuma gina sabbi domin bude yankunan karkara da birane.
Alhaji Barau Bungudu ya yi nuni da cewa, ana aiwatar da dukkanin ayyukan tituna da ake yi tare da bin ka’ida mai inganci, yana mai jaddada cewa, ‘yan kwangilar an ba su aikin samar da ababen more rayuwa masu dorewa da za su tsaya tsayin daka.
Ya yi kira ga mazauna yankin da su goyi bayan kokarin gwamnati ta hanyar kiyaye ababen more rayuwa da kuma hada kai da ‘yan kwangila a yayin gudanar da ayyukan.
Kwamishinan ya nanata kudirin gwamnatin na mayar da jihar Zamfara abin koyi wajen samar da ababen more rayuwa a yankin Arewa maso Yamma.
COV/AMINU DALHATU
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Zamfara samar da ababen more rayuwa gwamnatin jihar Barau Bungudu
এছাড়াও পড়ুন:
Juyin Mulki: ECOWAS ta ayyana dokar ta-baci a kasashenta
Kungiyar Raya Tattalin Arzikin Kasashen Yammacin Afirka (ECOWAS) ta ayyana dokar ta-baci a yankin, kwana biyu bayan yunkurin juyin mulki da bai yi nasara ba a kasar Jamhuriyar Benin.
Shugaban Hukumar ECOWAS, Omar Touray, ne ya sanar da haka a yayin zaman majalisar tsaro ta hukumar karo na 55 a Abua.
Touray ya ce daukar matakin ya zama dole domin shawo kan barazanar da juyin mulki ke wa tsarin dimokuradiyya a yankin, wanda ke bukatar matakan zuba jari na gagagwa domin tabbatar da tsaron al’umma.
A yayin jawabinsa ga ministoci da manyan jami’an gwamnati da ke halartar taron, ya bayyana yadda yawaitar samun juyin mulki a Yammacin Afirka ke barazana ga tsaro da zaman lafiya a yankin.
Sojoji sun kashe ’yan bindiga 13, sun ceto ’yan kasuwa a Sakkwato HOTUNA: Yadda dalibai 100 da aka sace a Neja suka dawoYa ce, “Babban barazana ga yankinmu sun haɗa da ci gaba da katsalandan na sojoji (kamar yadda aka gani kwanan nan a Guinea-Bissau da Jamhuriyar Benin); rashin bin ka’idojin sauyin mulki a Guinea inda shugaban soja ke ƙoƙarin zama farar hula; raguwar damar shiga zabe a ƙasashe da dama; ƙara karfin ’yan ta’adda, kungiyoyi masu laifi da ke dauke da makamai; da kuma matsin lamba na siyasar duniya da ke shafar diflomasiyya da haɗin kan ƙasashen mambobi.”
Touray ya jaddada cewa “zabe ya zama babban abin da ke tayar da rikici a cikin al’ummarmu.”
Ya kuma ambaci yunƙurin juyin mulki da aka yi kwanan nan da tattaunawa da ƙasashen AES (Burkina Faso, Mali da Nijar) da suka fice daga ECOWAS, yana mai nanata bukatar gaggawa ta haɗin gwiwar yankin wajen yaki da ta’addanci da laifukan da ke ketare iyaka.
Ya bayyana lamarin a matsayin abin da bai taɓa faruwa ba, yana gargadi da cewa, “Idan aka dubi wannan hali, ya dace mu bayyana cewa al’ummarmu tana cikin yanayin gaggawa.”
Touray ya bukaci a riƙa yin taron Majalisar Sulhu da Tsaro akai-akai a shekara mai zuwa, yana mai cewa ECOWAS dole ta “haɗa ƙarfi da ƙarfi don fuskantar barazanar ta’addanci da ’yan fashi, waɗanda ba sa mutunta iyakokin ƙasashe.”
Ya kuma bayyana muhimman wuraren da ministoci za su riƙa kula da su, ciki har da rikicin Guinea-Bissau, tafiyar da sauyin mulki, magance ƙara yawaitar cire mutane daga siyasa, da kuma kare haɗin kan yankin daga matsin lamba na waje.