Gwamnatin Zamfara Ta Yaba Da Cigaban Ayyukan Tituna A Jihar
Published: 11th, April 2025 GMT
Gwamnatin jihar Zamfara ta bayyana gamsuwarta da yadda ake ci gaba da gudanar da ayyukan gina tituna da gyare-gyare a fadin jihar.
Kwamishinan ayyuka da samar da ababen more rayuwa na jihar Alhaji Lawal Barau Bungudu ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Gusau babban birnin jihar.
Alhaji Lawal Barau Bungudu ya bayyana cewa, tun bayan hawan Gwamna Dauda Lawal mulki, gwamnatin ta ba da fifiko wajen samar da ababen more rayuwa, musamman gine-gine da sake gina tituna, a wani bangare na babban shirinta na sabunta birane da nufin kawo sauyi a jihar da kuma saukaka zirga-zirgar ababen hawa.
Ya ce gwamnatin jihar ta dukufa wajen fadada hanyoyin jihar domin ingantawa da bunkasa harkokin tattalin arziki, inda ya bayyana cewa ana gudanar da ayyukan da ake gudanarwa a daidai lokacin da aka amince da su.
Alhaji Lawal Barau Bungudu ya kuma bayyana cewa, an riga an kammala ayyukan tituna da dama, yayin da wasu da dama kuma suke mataki daban-daban na kammala su.
Ya ba da tabbacin cewa, gwamnatin jihar za ta ci gaba da sanya ido a kan ci gaban da aka samu don tabbatar da isar da kayayyakin aiki a kan lokaci ba tare da tsaiko ba.
Kwamishinan ya jaddada cewa, gwamnatin jihar Zamfara ta mayar da hankali wajen gyara tsofaffin tituna, da suka lalace da kuma gina sabbi domin bude yankunan karkara da birane.
Alhaji Barau Bungudu ya yi nuni da cewa, ana aiwatar da dukkanin ayyukan tituna da ake yi tare da bin ka’ida mai inganci, yana mai jaddada cewa, ‘yan kwangilar an ba su aikin samar da ababen more rayuwa masu dorewa da za su tsaya tsayin daka.
Ya yi kira ga mazauna yankin da su goyi bayan kokarin gwamnati ta hanyar kiyaye ababen more rayuwa da kuma hada kai da ‘yan kwangila a yayin gudanar da ayyukan.
Kwamishinan ya nanata kudirin gwamnatin na mayar da jihar Zamfara abin koyi wajen samar da ababen more rayuwa a yankin Arewa maso Yamma.
COV/AMINU DALHATU
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Zamfara samar da ababen more rayuwa gwamnatin jihar Barau Bungudu
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Siriya Zata Samar Da Huldar Jakadanci Da HKI A Dai-Dai Lokacinda Ya Dace
Shugaban rikon kwarya na kasar Siriya Ahmed Al-sharaa ya bayyana cewa gwamnatinsa a shirye take ta samar da hulda da HKI a dai-dai lokacinda ya dace.
Jaridar Middle East Eye ta kasar Burtaniya ta nakalto Ahmed Sharaa yana fadar haka a wata wasikar da ya rubutawa shugaba Donal Trump
Har’ila yau shugaba Al-sharaa ya fadawa wani dan majalisar dokokin kasar Amurka kan cewa gwamnatinsa zata samar da huldar jakadanci da HKI a lokacinda ya dace, sannan a bangaren kasar Siriya kuma tana bukatar da farko a dagewa kasar takunkuman da aka dora mata, sannan yana son a yi maganar yankunan kasar Siriya wadanda HKI ta mamaye bayan juyin mulkin da aka yi a kasar.
Dan majalisar dokokin kasar ta Amurka Cory Mills na hannun daman Trump ya ziyarci kasar Siriya a makon da ya gabata inda ya gana da shugaban, na kimani minti 90, don tattaunawa wadannan al-amura
Mill dai wanda ziyarci kasar ta tare naukar nauyin yan kasar Siriya a Amurka ya bayyana kamfanin dillancin labaran Bloomberg kan cewa ya fadawa shugaban matakan da yakamata ya dauka don ganin an daukewa kasar takunkuman tattalin arziki.
Ya kuba bukaci shugaban wargaza sauran masana’antun makaman guba a kasar, ya shiga cikin kasashen yankin masu yaki da ayyukan ta’addanci, ya kuma san yadda zai yi da yan kasashen waje wadanda suke cikin HTS, wanda suka taimaka masa ya sami damar kifar da gwamnatin Bashar al-asad. Sannan dole ne ya amintar da HKI kan cewa ba zai kai mata hari ba.