Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-12-10@10:21:11 GMT

Gwamnatin Zamfara Ta Yaba Da Cigaban Ayyukan Tituna A Jihar

Published: 11th, April 2025 GMT

Gwamnatin Zamfara Ta Yaba Da Cigaban Ayyukan Tituna A Jihar

Gwamnatin jihar Zamfara ta bayyana gamsuwarta da yadda ake ci gaba da gudanar da ayyukan gina tituna da gyare-gyare a fadin jihar.

 

Kwamishinan ayyuka da samar da ababen more rayuwa na jihar Alhaji Lawal Barau Bungudu ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Gusau babban birnin jihar.

 

Alhaji Lawal Barau Bungudu ya bayyana cewa, tun bayan hawan Gwamna Dauda Lawal mulki, gwamnatin ta ba da fifiko wajen samar da ababen more rayuwa, musamman gine-gine da sake gina tituna, a wani bangare na babban shirinta na sabunta birane da nufin kawo sauyi a jihar da kuma saukaka zirga-zirgar ababen hawa.

 

Ya ce gwamnatin jihar ta dukufa wajen fadada hanyoyin jihar domin ingantawa da bunkasa harkokin tattalin arziki, inda ya bayyana cewa ana gudanar da ayyukan da ake gudanarwa a daidai lokacin da aka amince da su.

 

Alhaji Lawal Barau Bungudu ya kuma bayyana cewa, an riga an kammala ayyukan tituna da dama, yayin da wasu da dama kuma suke mataki daban-daban na kammala su.

 

Ya ba da tabbacin cewa, gwamnatin jihar za ta ci gaba da sanya ido a kan ci gaban da aka samu don tabbatar da isar da kayayyakin aiki a kan lokaci ba tare da tsaiko ba.

 

Kwamishinan ya jaddada cewa, gwamnatin jihar Zamfara ta mayar da hankali wajen gyara tsofaffin tituna, da suka lalace da kuma gina sabbi domin bude yankunan karkara da birane.

 

Alhaji Barau Bungudu ya yi nuni da cewa, ana aiwatar da dukkanin ayyukan tituna da ake yi tare da bin ka’ida mai inganci, yana mai jaddada cewa, ‘yan kwangilar an ba su aikin samar da ababen more rayuwa masu dorewa da za su tsaya tsayin daka.

 

Ya yi kira ga mazauna yankin da su goyi bayan kokarin gwamnati ta hanyar kiyaye ababen more rayuwa da kuma hada kai da ‘yan kwangila a yayin gudanar da ayyukan.

 

Kwamishinan ya nanata kudirin gwamnatin na mayar da jihar Zamfara abin koyi wajen samar da ababen more rayuwa a yankin Arewa maso Yamma.

 

COV/AMINU DALHATU

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Zamfara samar da ababen more rayuwa gwamnatin jihar Barau Bungudu

এছাড়াও পড়ুন:

Dalilin yawaitar juyin mulki a Afirka ta Yamma

Masana harkokin siyasa, jakadu da ƙungiyoyin fararen hula sun bayyana cewa rashin shugabanci nagari da son mulki na dogon lokaci su ne manyan dalilan da ke haddasa yawaitar juyin mulki a yankin Afirka ta Yamma.

Wannan na zuwa ne bayan yunƙurin juyin mulki da aka yi a Jamhuriyar Benin a ranar Lahadi, wanda ya jefa ƙasar cikin rudani.

Gwamnatin Benin ta ce ta shawo kan lamarin bayan wasu sojoji sun bayyana a talabijin na ƙasar cewa sun kifar da Shugaba Patrice Talon. Wannan na zuwa ne makonni kaɗan bayan juyin mulki a ƙasar Guinea-Bissau.

Majiyoyin tsaro sun tabbatar da kama sojoji kusan 12, ciki har da shugabannin yunƙurin da bai yi nasara ba. Talon, tsohon ɗan kasuwa mai shekaru 67, na shirin miƙa mulki a watan Afrilu mai zuwa bayan shekaru 10 a kan karagar mulki da ake ganin ya kawo ci gaban tattalin arziki da kuma ƙaruwar hare-haren masu iƙirarin jihadi.

Juyin mulki: An kama sojojin da suka yi yunƙurin kwace mulki a Benin Yadda muka daƙile yunƙurin juyin mulki a Benin — Sojin Saman Najeriya

Sojojin da suka kira kansu Kwamitin Soja na Sake Tsarawa (CMR) sun bayyana a talabijin cewa sun yanke hukuncin cire Talon daga mulki.

Sai dai daga baya fadar shugaban ƙasa ta tabbatar da cewa Talon yana cikin koshin lafiya, ya ƙ bayyana masu yunƙurin a matsayin “ƙananan mutane da suka mamaye talabijin kawai.”

Ra’ayin masana

Jakadan Najeriya a ƙasashen yankin, Ambasada Suleiman Ɗahiru, ya ce juyin mulki na yawaita ne saboda raunin dimokuradiyya da kuma rashin nagartar shugabanci.

“Dimokuradiyya ba ta kafa tushe yadda ya kamata a Afirka ta Yamma. Shugabanni da aka zaɓa ba sa tafiyar da ƙasashensu yadda ya dace, hakan ya haifar da ƙin yarda daga jama’a,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa zaɓe ya rasa amincewa a ƙasashe da dama, inda shugabanni ke ƙin sauka daga mulki. Ya kawo misali da Kamaru, inda shugaban ƙasa mai shekaru 92 ya ci zaɓe, da Gambiya, inda shugabanni ke nuna rashin niyyar sauka daga mulki.

Suleiman Ɗahiru ya ce sai shugabanni sun yi mulki da gaskiya da adalci, in ba haka ba, juyin mulki zai ci gaba da dawowa.

Ƙalubalen ECOWAS

Tsohon jakadan Najeriya, M.K Ibrahim, ya bayyana cewa yawaitar juyin mulki babban koma baya ne ga yankin da kuma ƙungiyar ECOWAS.

Ya ce tun bayan kafa ECOWAS a 1975, an samu aƙalla juyin mulki 45 a yankin, sai dai tsakanin 2000 zuwa 2008 ne kawai aka samu zaman lafiya ba tare da juyin mulki ba.

Ibrahim ya ce yunƙurin da bai yi nasara ba a Benin ya sake bayyana raunin dimokuradiyya a yankin. Yanzu ƙasashe huɗu na ECOWAS ke ƙarƙashin mulkin soja, kuma idan Benin ta faɗi, da za a ce sun zama biyar.

Ya ce Najeriya na da nauyi na musamman wajen tabbatar da ci gaba da rayuwar ECOWAS, duk da matsalolinta na siyasa da tattalin arziki.

Ra’ayoyi kan matakan ECOWAS

Ibrahim ya bayyana cewa akwai ra’ayoyi biyu a cikin ƙungiyar:
– Wasu na ganin dole a tsaya kan ka’idojin dimokuraɗiyyar da nagartar shugabanci, ko da hakan zai sa ƙasashe su fice daga ECOWAS.
– Wasu kuma na ganin ka’idojin sun yi tsauri, suna ba da shawarar tattaunawa maimakon fitar da ƙasa nan take.

Sai dai Ibrahim ya bayyana matsayinsa: “ECOWAS ba za ta ci gaba ba ta hanyar juyin mulki. Dimokuraɗiyya da nagartar shugabanci ne kawai za su tabbatar da haɗin kai da ci gaba.”

Dalilan yawaitar juyin mulki

Ya ce raunin dimokuraɗiyyar, talauci, rashin tsaro da matsalolin Sahel na daga cikin manyan dalilan da ke sa jama’a su rungumi alkawarin sojoji duk da rashin tabbas.“Ba za a iya cewa akwai wata ƙasa a Afirka da ta tsallake barazanar juyin mulki ba,” in ji shi.

 

Daga: Sagir Kano Saleh, Joshua Odeyemi, Baba Martins, Dalhatu Liman (Abuja) & Salim Umar Ibrahim (Kano)

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnan Jihar Ribas ya sauya sheka zuwa APC
  • Juyin Mulki: ECOWAS ta ayyana dokar ta-baci a kasashenta
  • Gwamnonin Arewa Za Su Zuba Biliyoyin Naira Don Yaki da Matsalar Tsaro
  • Zaben 2027: NNPP Ta Sha Alwashin Maye Gurbin Tinubu da Radda
  • ASUU-SSU Ta Zargi VC Da KaryDokokin Jami’ar Jihar Sakkwato
  • Najeriya: Gwamnatin Tarayya Ta Bada Sanarwan Kubutar Da Yan Makaranta 100 Da Aka Sace
  • Rashin Tsaro: Gwamnatin Tarayya ta gaza — Kwankwaso
  • Dalilin yawaitar juyin mulki a Afirka ta Yamma
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan(a) 168
  • Kissoshin rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 167