Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-11-25@17:35:18 GMT

Gwamnatin Zamfara Ta Yaba Da Cigaban Ayyukan Tituna A Jihar

Published: 11th, April 2025 GMT

Gwamnatin Zamfara Ta Yaba Da Cigaban Ayyukan Tituna A Jihar

Gwamnatin jihar Zamfara ta bayyana gamsuwarta da yadda ake ci gaba da gudanar da ayyukan gina tituna da gyare-gyare a fadin jihar.

 

Kwamishinan ayyuka da samar da ababen more rayuwa na jihar Alhaji Lawal Barau Bungudu ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Gusau babban birnin jihar.

 

Alhaji Lawal Barau Bungudu ya bayyana cewa, tun bayan hawan Gwamna Dauda Lawal mulki, gwamnatin ta ba da fifiko wajen samar da ababen more rayuwa, musamman gine-gine da sake gina tituna, a wani bangare na babban shirinta na sabunta birane da nufin kawo sauyi a jihar da kuma saukaka zirga-zirgar ababen hawa.

 

Ya ce gwamnatin jihar ta dukufa wajen fadada hanyoyin jihar domin ingantawa da bunkasa harkokin tattalin arziki, inda ya bayyana cewa ana gudanar da ayyukan da ake gudanarwa a daidai lokacin da aka amince da su.

 

Alhaji Lawal Barau Bungudu ya kuma bayyana cewa, an riga an kammala ayyukan tituna da dama, yayin da wasu da dama kuma suke mataki daban-daban na kammala su.

 

Ya ba da tabbacin cewa, gwamnatin jihar za ta ci gaba da sanya ido a kan ci gaban da aka samu don tabbatar da isar da kayayyakin aiki a kan lokaci ba tare da tsaiko ba.

 

Kwamishinan ya jaddada cewa, gwamnatin jihar Zamfara ta mayar da hankali wajen gyara tsofaffin tituna, da suka lalace da kuma gina sabbi domin bude yankunan karkara da birane.

 

Alhaji Barau Bungudu ya yi nuni da cewa, ana aiwatar da dukkanin ayyukan tituna da ake yi tare da bin ka’ida mai inganci, yana mai jaddada cewa, ‘yan kwangilar an ba su aikin samar da ababen more rayuwa masu dorewa da za su tsaya tsayin daka.

 

Ya yi kira ga mazauna yankin da su goyi bayan kokarin gwamnati ta hanyar kiyaye ababen more rayuwa da kuma hada kai da ‘yan kwangila a yayin gudanar da ayyukan.

 

Kwamishinan ya nanata kudirin gwamnatin na mayar da jihar Zamfara abin koyi wajen samar da ababen more rayuwa a yankin Arewa maso Yamma.

 

COV/AMINU DALHATU

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Zamfara samar da ababen more rayuwa gwamnatin jihar Barau Bungudu

এছাড়াও পড়ুন:

An buɗe wasu makarantu domin ci gaba da jarawaba a Katsina

Hukumar kula da makarantun firamare da sakandare ta Jihar Katsina ta sanar da sake buɗe wasu makarantu domin ci gaba da jarabawar zangon farko na shekarar karatu.

A wata sanarwa da Jami’in Hulɗa da Jama’a na hukumar, Sani Danjuma Suleman, ya fitar a madadin Shugaban hukumar, ta ce makarantun firamare, sakandiren je-ka-ka-dawo da kuma makarantu masu zaman kansu za su buɗe daga yau Talata domin ci gaba da jarabawar zangon farko.

Sanarwar ta ƙara da cewa, sauran makarantun kwana za su ci gaba da kasancewa a rufe har sai lokacin da hali ya ba da dama.

Aminiya ta ruwaito cewa, a bayan nan ne Gwamnatin Katsina ta rufe makarantun bayan ƙaruwar hare-haren sace ɗalibai da masu garkuwa da mutane suka sake farfaɗowa da su a wasu yankuna.

Gwamnatin ta ce ta ɗauki matakin ne da nufin daƙile matsalar tsaro da kuma sa ido a kan al’amura.

A ƙarshe, hukumar ta roƙi haɗin kan iyaye da masu kula da ɗalibai domin su ci gaba da ba wa shirin goyon baya tare da ƙarfafa ɗaliban su dage da karatu wajen rubuta jarabawar da suke yi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An buɗe wasu makarantu domin ci gaba da jarawaba a Katsina
  • An rufe duk makarantu a Jihar Bauchi saboda matsalar tsaro
  • Matsalar tsaro: Gwamnatin Yobe ta rufe duk makarantun sakandaren kwana
  • An rufe duk makarantu a Jihar Bauchi na saboda matsalar tsaro
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 162
  • An ceto mutum 38 da aka sace a cocin Kwara — Tinubu
  • Gwamnatin Kebbi Ta Bayar da Umarnin Rufe Makarantu a Jihar
  • An rufe duk makarantu a Kebbi
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 161
  • Gwamnatin Yobe ta ba da umarnin rufe makarantun kwana a jihar