Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-12-05@03:07:36 GMT

Gwamnatin Zamfara Ta Yaba Da Cigaban Ayyukan Tituna A Jihar

Published: 11th, April 2025 GMT

Gwamnatin Zamfara Ta Yaba Da Cigaban Ayyukan Tituna A Jihar

Gwamnatin jihar Zamfara ta bayyana gamsuwarta da yadda ake ci gaba da gudanar da ayyukan gina tituna da gyare-gyare a fadin jihar.

 

Kwamishinan ayyuka da samar da ababen more rayuwa na jihar Alhaji Lawal Barau Bungudu ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Gusau babban birnin jihar.

 

Alhaji Lawal Barau Bungudu ya bayyana cewa, tun bayan hawan Gwamna Dauda Lawal mulki, gwamnatin ta ba da fifiko wajen samar da ababen more rayuwa, musamman gine-gine da sake gina tituna, a wani bangare na babban shirinta na sabunta birane da nufin kawo sauyi a jihar da kuma saukaka zirga-zirgar ababen hawa.

 

Ya ce gwamnatin jihar ta dukufa wajen fadada hanyoyin jihar domin ingantawa da bunkasa harkokin tattalin arziki, inda ya bayyana cewa ana gudanar da ayyukan da ake gudanarwa a daidai lokacin da aka amince da su.

 

Alhaji Lawal Barau Bungudu ya kuma bayyana cewa, an riga an kammala ayyukan tituna da dama, yayin da wasu da dama kuma suke mataki daban-daban na kammala su.

 

Ya ba da tabbacin cewa, gwamnatin jihar za ta ci gaba da sanya ido a kan ci gaban da aka samu don tabbatar da isar da kayayyakin aiki a kan lokaci ba tare da tsaiko ba.

 

Kwamishinan ya jaddada cewa, gwamnatin jihar Zamfara ta mayar da hankali wajen gyara tsofaffin tituna, da suka lalace da kuma gina sabbi domin bude yankunan karkara da birane.

 

Alhaji Barau Bungudu ya yi nuni da cewa, ana aiwatar da dukkanin ayyukan tituna da ake yi tare da bin ka’ida mai inganci, yana mai jaddada cewa, ‘yan kwangilar an ba su aikin samar da ababen more rayuwa masu dorewa da za su tsaya tsayin daka.

 

Ya yi kira ga mazauna yankin da su goyi bayan kokarin gwamnati ta hanyar kiyaye ababen more rayuwa da kuma hada kai da ‘yan kwangila a yayin gudanar da ayyukan.

 

Kwamishinan ya nanata kudirin gwamnatin na mayar da jihar Zamfara abin koyi wajen samar da ababen more rayuwa a yankin Arewa maso Yamma.

 

COV/AMINU DALHATU

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Zamfara samar da ababen more rayuwa gwamnatin jihar Barau Bungudu

এছাড়াও পড়ুন:

Tsaro: Gwamnonin Arewa na shirin dakatar da haƙar ma’adinai

Gwamnonin Arewaci, na shirin dakatar da haƙar ma’adinai a wasu yankuna da ake fama da matsalar tsaro, domin daƙile ayyukan ’yan bindiga da sauran ƙungiyoyin ta’addanci.

Wannan batu ya fito ne daga taron haɗin gwiwa na Gwamnonin Arewa da Majalisar Sarakunan Gargajiya da aka yi a Kaduna daga 1 zuwa 2 ga watan Disamba, 2025.

’Yan sanda sun kama mutum 28 kan zargin lalata mata da yara a Yobe Tsaro: Gwamnatin Kano za ta fara amfani da jirage marasa matuƙa a iyakokinta

Shugaban ƙungiyar gwamnonin, Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya na Jihar Gombe, ya ce lamarin tsaro ya kai wani mataki da ke buƙatar ɗaukar matakin gaggawa.

Ya bayyana cewa wuraren haƙar ma’adinai sun zama mafakar ’yan bindiga, masu garkuwa da mutane da ƙungiyoyin ta’addanci, inda suke tara kuɗi da shirya hare-hare.

Ya ce ’yan ta’adda suna amfani da waɗannan wurare wajen ɓoye makamai da tsara kai hare-hare.

“Dkatar da haƙar ma’adinai ne zai kawo zaman lafiya, dole mu ɗauki wannan mataki.”

Gwamnan ya ce Arewa na fuskantar matsaloli da dama; garkuwa da mutane, Boko Haram, rikice-rikicen karkara da talauci, wanda ke ƙara dagula tsaron yankin.

Ya ce dole a inganta tsaro tare da magance tushen matsalolin.

Ya kuma goyi bayan tsarin ’yan sandan jihohi, inda ya bayyana cewa bai kamata siyasa ta hana ɗaukar matakan tsaro ba.

Taron ya buƙaci Sarakunan Gargajiya da malamai su ƙara ƙoƙarin wanzar da zaman lafiya da fahimtar juna.

Hakazalika, an tattauna yawan yaran da ba sa zuwa makaranta da buƙatar inganta ilimi da sauran ɓangarorin tattalin arziƙi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  An Kira Yi Gwamnatin Canada Da Ta Kama Olmert Da Livini Na “Isra’ila
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar da Wutar Lantarki a Yankunan Kananan Hukumomin Jihar
  • Mutum 6 sun rasu, 13 sun jikkata a hatsarin mota a Kogi
  • Tsaro: Gwamnonin Arewa na shirin dakatar da haƙar ma’adinai
  • Kungiyar Guinness Ta Rigistan Ayyukan Bajinta Ta Duniya Ta Dakatar Da Karban Daga HKI
  • Tsaro: Gwamnatin Kano za ta fara amfani da jirage marasa matuƙa a iyakokinta
  • Rikicin Kungiyoyin Asiri Ya Yi Sanadiyyar Mutuwar Wani Matashi A Jihar Kwara
  • Gwamnatin Nasarawa Za Ta Gurfanar da Iyayen Yaran da Ba Sa Zuwa Makaranta
  • Mutane 9,854 na ɗauke da cutar AIDS a Yobe 
  • ’Yan ta’adda sun kashe ɗan sanda a gidan DPO a Jigawa