UBEC Ta Bayyana Jihar Jigawa A Matsayin Abin Kuyi A Fannin Ilimi
Published: 11th, April 2025 GMT
Hukumar ilimin bai daya ta kasa wato UBEC ta yabawa Gwamna Umar Namadi na Jihar Jigawa bisa jajircewar sa wajen inganta ilimi a matakin farko a Jihar.
Shugabar Hukumar, Hajiya Aisha Garba, ta bayyana hakan a yayin ziyarar gwamnan zuwa hedikwatar UBEC a Abuja.
Hajiya Aisha Garba ta bayyana jihar Jigawa a matsayin abin koyi ga sauran jihohin kasar nan.
Kazalika, ta jaddada irin yadda gwamnati ta zage damtse wajen zuba jari a harkar ilmi, tana mai cewa Jihar ta karɓi fiye da Naira biliyan 21 daga tallafin UBEC tun daga shekarar 2004, wanda ya sanya ta cikin jihohin da suka fi cika sharudan samun tallafin UBEC.
Ta kuma lissafa wasu daga cikin nasarorin da aka cimma a ƙarƙashin Gwamna Namadi wadanda suka hada da gina fiye da ajujuwa 3,000 da rijiyoyi 500 da daukar malaman makaranta fiye da 7,000.
Tace Gwamnatin ta kuma horas da malamai sama da 17,000 da kaddamar da Kungiyoyin Iyaye Mata da Ƙarfafa Kwamitocin Gudanarwar Makarantu wato SBMC da kuma kulla haɗin gwiwa da wani kamfani a shirin Jigawa UNITES.
A nasa jawabin, Gwamna Umar Namadi ya jaddada cewar, gwamnatin sa ta himmatu wajen sauya tsarin karatu da inganta sakamako ta hanyar amfani da bayanai da kuma haɗa kai da al’umma.
Usman Mohammed Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamna Radda ya miƙa wa mataimakinsa ragamar mulkin Katsina
Gwamnan Katsina, Dikko Umaru Radda, ya sanar da miƙa wa mataimakinsa, Malam Faruk Jobe, ragamar mulkin jihar, inda shi kuma zai tafi hutun mako uku domin duba lafiyarsa.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da kwamishinan yaɗa labaran jihar, Bala Salisu Zango, ya fitar a ranar Alhamis.
Sanarwar ta bayyana cewa hutun zai fara ne daga ranar Litinin, 18 ga watan Agusta, 2025.
An zabi sabuwar firaminista a Luthuania Mun shirya wa zaben ciki gurbi a Kano —INECA cewar Gwamna Radda, hutun zai ba shi damar samun kulawar likitoci da kuma tabbatar da cewa zai ci gaba da gudanar da ayyukansa cikin koshin lafiya.
“Cikin matakan da nake ɗauka don kula da lafiyata da kuma ganin na yi aiki cikin yanayi mai kyau, na ɗauki wannan matakin tafiya hutu, kuma zan dawo da zarar likitoci sun gama duba ni,” in ji gwamnan a cikin sanarwar.
A watan Yuli ne gwamnan ya gamu da hatsarin mota a kan hanyar Katsina zuwa Daura, lamarin da ya jawo damuwa a tsakanin jama’a.