Cutar Kwastomomi: NERC ta ci kamfanonin rarraba lantarki tarar N628m
Published: 11th, April 2025 GMT
Hukumar Kula Wutar Lantarki ta Ƙasa (NERC) ta ci kamfanonin rarraba lantarki tarar naira miliyan 628 kan laifin karɓar kuɗin wuta fiye da kima daga hannun kwastomomi marasa mita.
Hukumar ta kuma ba wa kamfanonin rarraba lantarkin da hakan ta shafa wa’adin ranar 15 ga watan Mayu, 2025, sun tabbatar sun biya kwastomomin da suka canza fiye da kima, ta hanyar ba su wuta daidai da abin da suka ƙware su.
NERC ta bayyana cewa ɗaukar wannan mataki ya zama dole saboda kamfanonin sun yi kunnen ƙashi bayan umarnin da ta ba su, wanda ya ƙayyade kuɗin da su caji kwastomomi da ba su da mita.
Ta ce waɗanda aka ci tarar sun haɗa da Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Kaduna (Kaduna Electric) da Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Kano (KEDCO) da Kamfanin Rarraba Lantarki na Abuja (AEDC), Kamfanin Rarraba Lantarki na Jos da kuma Kamfanin Rarraba Lantarki na Yola.
Sauran su ne Kamfanin Rarraba Lantarki na Legas da takwarorinsa na Enugu da kuma Ikeja.
Sanarwar da Hukumar NERC ta fitar ta ce wannan tarar ta shafi kamfanonin guda takwas ne daga watan Yuli zuwa Satumbar shekarar 2024.
Ta bayyana cewa binciken da ta gudanar ya nuna kamfanonin sun yi watsi da umarnin nata da ya ƙayyade cazar kwastomomi marasa mita da ke kan layin lantarki guda a duk wata.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Kwastomomi Lantarki marasa mita
এছাড়াও পড়ুন:
Da amincewar hukumomi nake tattaunawa da ’yan bindiga — Sheikh Gumi
Sheikh Ahmad Gumi ya yi martani kan kiraye-kirayen da ake yi na kama shi, inda ya ce masu yin kiran na yi ne domin kawar da rawar da yake takawa wajen magance matsalar ’yan bindiga a Arewa.
Gumi, ya ce duk ganawar da yake yi da ’yan bindiga yana yi ne domin samar da zaman lafiya, kuma hukumomin tsaro sun san da komai.
Ɗan Najeriya ya kashe mahaifinsa, ya yanki ƙannensa da wuƙa a Amurka Tsaro: Na kan yi kuka duk lokacin da na ji an kashe wani — AkpabioMaganar ta sake fitowa fili ne bayan da ya sake jaddada cewa tattaunawa hanya ce da za ta iya kawo ƙarshen tashin hankali a karkara.
A cikin dogon saƙon da ya wallafa a Facebook a ranar Lahadi, Gumi ya soki masu cewa ya kamata a kama shi saboda ya ganawar da ya yi da shugabannin ’yan bindiga.
Ya bayyana kiran a matsayin don rai la’akari da irin ƙoƙarin da ya yi a baya domin daƙile matsalar tsaro a Arewa.
Ya ce ba shi niyyar goyon bayan masu laifi; kawai yana ƙoƙari rage tashin hankali da kuma shawo kan ’yan bindiga su miƙa wuya.
Gumi, ya ce ya yi muhimmin zama da mahara a Janairun 2021 a dajin Sabon Garin Yadi da ke Ƙaramar Hukumar Giwa a Jihar Kaduna.
Kuma ya ce tare da Kwamishinan ’Yan Sandan Kaduna ya je a lokacin d aka yi ganawar, wanda ya wakilci Sufeton ’Yan Sanda na Ƙasa.
Ya ce taron ya samu halartar ’yan bindiga da shugabanninsu sama da 600, kuma sun yi alƙawarin daina kai hare-hare idan gwamnati ta samar musu da wasu muhimman abubuwa.
“Na je dajin Sabon Garin Yadi tare da Kwamishinan ’Yan Sandan Kaduna.”
“Wannan zama ɓangare ne na aikin samar da zaman lafiya, inda muka yi wa ’yan bindiga sama da 600 da shugabanninsu wa’azi, suka kuma amince za su ajiye makamai idan gwamnati ta samar musu da tsaro da ingantaccen rayuwa,” in ji shi.
Gumi, ya ce duk abin da ya yi bisa ƙa’ida ya yi sa, kuma hukumomi sun san da komai.
Ya ce maimakon mutane su kai su soke shi, kamata ya yi su tambayi dalilin da ya sa gwamnati ba ta yi buƙatun ’yan bindiga ba.
Sheikh Gumi ya kuma tambayi dalilin da ya sa wasu ke son a kama shi, alhali manufarsa ita ce kawo ƙarshen tashin hankali a Najeriya.
“To me zai sa kama ni? Domin na yi kira su ajiye makamai… ko saboda na faɗakar da al’umma game da labarin ’yan bindiga?”.
Gumi ya zargi masu sukarsa da nuna wariya, inda ya tunatar da su cewa kundin tsarin mulki ya bai wa kowa damar faɗin albarkacin bakinsa.
“Shin faɗin ra’ayi ba haƙƙinmu ba ne na kundin tsarin mulki ba? Shin kira da suke yi na a kama ni ba nuna son rai ba ne kuma zai iya haifar da tashin hankali?”.
Ya bayyana cewa buƙatun ’yan bindigar suka nema waɗanda suka haɗa da ababen more rayuwa, kariya daga kame ba bisa ƙa’ida ba, da hanankai musu hari ba idan sun miƙa wuya.
Ya ce babu ɗaya daga cikin waɗannan abubuwan da aka aiwatar, wanda hakan ya wargatsa tattaunawar.
Gumi, ya ce kamata ya yi mutane su mayar da hankali kan mafita a aikace, ba zagi da fushi ba.