Cutar Kwastomomi: NERC ta ci kamfanonin rarraba lantarki tarar N628m
Published: 11th, April 2025 GMT
Hukumar Kula Wutar Lantarki ta Ƙasa (NERC) ta ci kamfanonin rarraba lantarki tarar naira miliyan 628 kan laifin karɓar kuɗin wuta fiye da kima daga hannun kwastomomi marasa mita.
Hukumar ta kuma ba wa kamfanonin rarraba lantarkin da hakan ta shafa wa’adin ranar 15 ga watan Mayu, 2025, sun tabbatar sun biya kwastomomin da suka canza fiye da kima, ta hanyar ba su wuta daidai da abin da suka ƙware su.
NERC ta bayyana cewa ɗaukar wannan mataki ya zama dole saboda kamfanonin sun yi kunnen ƙashi bayan umarnin da ta ba su, wanda ya ƙayyade kuɗin da su caji kwastomomi da ba su da mita.
Ta ce waɗanda aka ci tarar sun haɗa da Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Kaduna (Kaduna Electric) da Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Kano (KEDCO) da Kamfanin Rarraba Lantarki na Abuja (AEDC), Kamfanin Rarraba Lantarki na Jos da kuma Kamfanin Rarraba Lantarki na Yola.
Sauran su ne Kamfanin Rarraba Lantarki na Legas da takwarorinsa na Enugu da kuma Ikeja.
Sanarwar da Hukumar NERC ta fitar ta ce wannan tarar ta shafi kamfanonin guda takwas ne daga watan Yuli zuwa Satumbar shekarar 2024.
Ta bayyana cewa binciken da ta gudanar ya nuna kamfanonin sun yi watsi da umarnin nata da ya ƙayyade cazar kwastomomi marasa mita da ke kan layin lantarki guda a duk wata.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Kwastomomi Lantarki marasa mita
এছাড়াও পড়ুন:
Hukumar Gidan Yarin Kano Ta Tabbatar Da Dauke Abduljabbar Zuwa Abuja
Sanarwar ta ce: “Sauya wurin da aka yi wa fursuna Malam Abduljabbar Nasiru Kabara zuwa daya daga cikin cibiyoyin tsarewa da ke karkashin ikon tarayya hanya ce ta gudanar da aiki ta yau da kullum wacce aka yi bisa ga dokokin aiki da ka’idojin hukumar.”
Ta kara da bayanin cewa motsa fursunoni daga cibiyar tsarewa zuwa wata musamman wadanda ke da matakan tsaro daban-daban na daga cikin ayyukan da kundin tsarin mulki ya dora wa hukumar domin tabbatar da ingantaccen tafiyar da fursunoni, gyarawa da kuma dawo da su kan turba.
Sanarwar ta kara da cewa: “Canjawa ko sauya wurin fursuna zuwa wata cibiyar gyaran hali mai matakin tsaro daban da wacce ake tsare da shi a baya na daga cikin ayyukan da kundin tsarin mulki ya ba Hukumar Kula da Gidajen Yari, kamar yadda Dokar Hukumar ta 2019 ta tanada.”
Sanarwar ta ce: “Ana yanke irin wadannan shawara ne bisa la’akari da abubuwa da dama, ciki har da tsaro, tsarin rarraba fursunoni, samun wurin da ya dace a cibiyoyi, da kuma bukatun gyarawa da farfado da fursuna.”
CSC Musbahu ya tabbatar wa jama’a cewa duk da wannan sauya wuri, ana ci gaba da kiyaye dukkan hakkokin Malam Abduljabbar.
Ya ce: “An tabbatar wa jama’a cewa walwala da dukkan hakkokin shari’a na Malam Abduljabbar suna nan daram karkashin kariyar doka.”
Sanarwar ta kara da cewa: “Wannan sauya wuri ba ya shafar matsayinsa na shari’a, hakkinsa na daukaka kara ko samun damar tuntubar lauyansa.”
Jami’in hulda da jama’a ya sake jaddada kudirin hukumar na tabbatar da tsare fursunoni cikin aminci, gyarawa da farfado da su, domin tabbatar da tsaron jiha da kare rayukan jama’a.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA