Cutar Kwastomomi: NERC ta ci kamfanonin rarraba lantarki tarar N628m
Published: 11th, April 2025 GMT
Hukumar Kula Wutar Lantarki ta Ƙasa (NERC) ta ci kamfanonin rarraba lantarki tarar naira miliyan 628 kan laifin karɓar kuɗin wuta fiye da kima daga hannun kwastomomi marasa mita.
Hukumar ta kuma ba wa kamfanonin rarraba lantarkin da hakan ta shafa wa’adin ranar 15 ga watan Mayu, 2025, sun tabbatar sun biya kwastomomin da suka canza fiye da kima, ta hanyar ba su wuta daidai da abin da suka ƙware su.
NERC ta bayyana cewa ɗaukar wannan mataki ya zama dole saboda kamfanonin sun yi kunnen ƙashi bayan umarnin da ta ba su, wanda ya ƙayyade kuɗin da su caji kwastomomi da ba su da mita.
Ta ce waɗanda aka ci tarar sun haɗa da Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Kaduna (Kaduna Electric) da Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Kano (KEDCO) da Kamfanin Rarraba Lantarki na Abuja (AEDC), Kamfanin Rarraba Lantarki na Jos da kuma Kamfanin Rarraba Lantarki na Yola.
Sauran su ne Kamfanin Rarraba Lantarki na Legas da takwarorinsa na Enugu da kuma Ikeja.
Sanarwar da Hukumar NERC ta fitar ta ce wannan tarar ta shafi kamfanonin guda takwas ne daga watan Yuli zuwa Satumbar shekarar 2024.
Ta bayyana cewa binciken da ta gudanar ya nuna kamfanonin sun yi watsi da umarnin nata da ya ƙayyade cazar kwastomomi marasa mita da ke kan layin lantarki guda a duk wata.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Kwastomomi Lantarki marasa mita
এছাড়াও পড়ুন:
Abba ya naɗa Ahmed Musa a matsayin Babban Manajan Kano Pillars
Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya sauya shugabancin ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillars.
Ya naɗa tsohon kyaftin ɗin Super Eagles, Ahmed Musa, a matsayin sabon Babban Manajan ƙungiyar.
An gano wasu bama-bamai 56 da ISWAP suka binne a Borno “ADC za ta fuskanci matsala wajen zaɓen wanda zai yi mata takarar shugaban ƙasa”Wannan mataki na daga cikin ƙoƙarin gwamnatin jihar na sake gina ƙungiyar kafin tunkarar kakar wasa ta 2025-2026 a Gasar Firimiyar Najeriya (NPFL).
A cewar sanarwar da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar a ranar Juma’a, an yanke hukuncin ne bayan tattaunawa da masu ruwa da tsaki a harkar kwallon ƙafa.
Gwamnatin ta rushe tawagar hukumar wasanni ta jihar tare da naɗa wasu sabbi, wadda ke da mambobi 17; Ali Muhammad Umar (Nayara) ne jagorance ta.
Sauran mambobin sun haɗa da Salisu Mohammed Kosawa, Yusuf Danladi (Andy Cole), Idris Malikawa Garu, Nasiru Bello, Muhammad Ibrahim (Hassan West), Hamza Abdulkarim Audi Chara.
Akwai Muhammad Danjuma Gwarzo, Mustapha Usman Darma, Umar Dankura, Ahmad Musbahu, Gambo Salisu Shuaibu Kura, Rabiu Abdullahi, Aminu Ma’alesh da Safiyanu Abdu.
Abubakar Isah Dandago Yamalash ya ci gaba da zama Daraktan Harkokin Watsa Labarai, sannan Ismail Abba Tangalash ya ci gaba da riƙe matsayin Daraktan Labarai na II.
A wani muhimmin mataki, hukumar ta zaɓi Ahmed Musa a matsayin sabon Babban Manajan ƙungiyar.
Ahmed Musa, wanda ya taɓa buga wa Kano Pillars wasanni kuma ya taka rawar gani a duniya, ana sa ran zai kawo sauyi, tsari da kuma ɗaukaka ƙungiyar.
Gwamna Abba, ya bayyana cewa yana da yaƙinin sabuwae tawagar hukumar za ta ci gaba da samo nasarori.
“Naɗin Ahmed Musa na nuna yadda muke ƙoƙarin samar da ƙwarewa da gogewa a harkar ƙwallon kafa.
“Muna da yaƙinin cewa kasancewarsa a ƙungiyar zai ƙara wa ‘yan wasa ƙwarin gwiwa, ya ja hankalin masu zuba jari, sannan ya faranta ran magoya baya,” inji sanarwar.
Kano Pillars, na ɗaya daga cikin fitattun ƙungiyoyin kwallon kafa a Najeriya, ana sa ran za a samu sauye-sauye ƙarƙashin sabon shugabancin.