HausaTv:
2025-10-24@15:39:10 GMT

Tawagogin gwamnatin Kongo da kungiyar M23 sun isa  Doha domin tattaunawa

Published: 11th, April 2025 GMT

Jami’an Kongo da masu shiga tsakani na M23 sun isa Qatar domin tattaunawa don cimma yarjejeniyar tsagaita wuta.

Jami’an Kongo da masu shiga tsakani na kungiyar M23 sun isa Doha babban birnin kasar Qatar domin tattaunawa da nufin cimma tsagaita bude wuta da kuma kawo karshen fadan da aka shafe watanni ana gwabzawa a yankin, kamar yadda wasu majiyoyi hudu suka shaida wa kamfanin dillancin labarai na Reuters a jiya Alhamis.

Wakilan tawagogin biyu sun tabbatar da kasancewarsu a babban birnin kasar Qatar, kuma sun ce za a yi ganawar ido-da-ido a ranar Laraba, amma har yanzu suna tattaunawa kan tsarin tattaunawar.

Dukkanin majiyoyi – jami’an gwamnati biyu da wakilan ‘yan tawaye – sun bukaci a sakaya sunansu saboda masu shiga tsakani na Qatar sun nemi kada su yi magana da manema labarai.

Qatar ta yi wata ganawa a watan da ya gabata tsakanin shugaban kasar Congo Felix Tshisekedi da takwaransa na Rwanda Paul Kagame. Wannan ita ce ganawa ta farko da shugabannin biyu suka yi tun bayan da kungiyar ta kaddamar da hari a ranar 23 ga watan Maris din da ya gabata. Yunkurin yin shawarwarin zaman lafiya na baya-bayan nan shi ne yunkurin kawo karshen rikicin da aka kwashe shekaru ana yi, wanda ya samo asali daga kisan kiyashin da aka yi a kasar Rwanda a shekara ta 1994.

Wata majiya da ke da masaniya kan shiga tsakani na Qatar ta shaidawa kamfanin dillacin labarai na Reuters cewa bangarorin biyu sun yi wata ganawar sirri a birnin Doha a farkon wannan wata domin shirya tattaunawar sulhu. Sai dai har yanzu tattaunawar da aka shirya fara a ranar Laraba na fuskantar cikas.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

An gano sauro a karon farko na tarihin ƙasar Iceland

A karon farko a tarihi, an gano sauro a ƙasar Iceland, tare da gano samfura guda uku a wannan watan a Kjos, wani yanki mai ƙwari a kusa da Hvalfjordur.

Wani mai sha’awar ƙwari, Bjorn Hjaltason ne ya fara ba da rahoton ganowar a cikin wani zaure na Facebook mai suna Skordyr a Islandi (wato ƙwari a Iceland), kamar yadda Hukumar Watsa Labarai ta Iceland ta faɗa a ranar Litinin.

Gwamnatin Borno rufe makarantun jihar saboda rigakafin ƙyanda da Polio Masu kwacen waya sun kashe ma’aikaciyar lafiya a Zariya

An miƙa samfuran ga Cibiyar Tarihin Halittu ta Iceland domin bincike, inda masanin ilimin halitta Matthias Alfredsson ya tabbatar da cewa lalle sauro ne.

An bayyana samfurin a matsayin Culiseta annulata, sauro mai jure sanyi da ake samu a arewacin Turai.

“Da alama sauron ba zai taɓa barin wajen ba,” in ji Matthias.

“Yana son ci gaba da samun ɗumi a lokacin hunturu a wurare masu inuwa kamar ɗakunan ajiya da gidajen dabbobi.”

Duk da cewa sauro na zuwa kasar Iceland a wasu lokuta a cikin tayoyin jiragen sama, wannan shi ne karon farko da aka gano sun samu wajen zama a kasar.

Masana kimiyya sun daɗe suna hasashen cewa sauro na iya samun kansa a Iceland.

Gano sauro a kasar ya jaddada yadda yanayi da sauyin muhalli ke iya faɗaɗa kewayon nau’in ƙwari masu jure sanyi fiye da kowane lokaci.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Jihar Sokoto Ta Amince da Sauya Amfani da Naira Biliyan 526 a Kasafin Kuɗin 2025
  • AGILE Kano Ta Tattauna da Malamai da Limamai Don Ƙarfafa Goyon Bayan Ilimin ’Yan Mata
  • Ministan Leken Asiri: Iran Bata Da Tabbacin Kare Maslaharta A Tattaunawa Da Amurka.
  • Araqchi: Akwai Sharuddan Da Iran Ta Gindaya Kafin Sake Komawa Kan Teburin Tattaunawa Da Amurka
  • An gano sauro a karon farko na tarihin ƙasar Iceland
  • Babaganaru Ya Zama Sabon Kocin Kano Pillars
  • Birtaniya Ta Cire Kungiyar Tahrirush -Sham Daga Jerin Yan Ta’adda
  • Gwamnatin Borno rufe makarantun jihar saboda rigakafin ƙyanda da Polio
  • Masu kwacen waya sun kashe ma’aikaciyar lafiya a Zariya
  • Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya