Namibiya ta janye bizar shiga ga wasu manyan kasashe na duniya
Published: 11th, April 2025 GMT
Namibiya ta janye bayar da biza ga Amurka, Burtaniya, da wasu kasashe sama da 30.
Matakin, wanda majalisar ministocin Namibiya ta yanke tun a watan Yuli, ya fara aiki ne a ranar 1 ga Afrilu.
Ya zuwa yanzu, galibin kasashen Turai, ciki har da Jamus, babbar tushen yawon bude ido a Namibiya, sun ci gajiyar shigowa kasar ba tare da biza ba.
Sabuwar shugabar Namibiya da aka rantsar, Netumbo Nandi-Ndaitwah, tana ci gaba da shirye-shiryen soke bizar shiga kasar ga wasu Karin kasashe, ta yadda ‘yan kasashen za su iya shiga Namibia ba tare da biz aba.
Manufar hakan dai ita ce kafafa harkokin kasuwanci da yawon bude ido a kasar ga yan kasashen ketare, da kuma karfafa kawance da sauran kasashe.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Kyaftin Traoré : Yau Burkina ta zama misali a duniya
Shugaban kasar Burkina Faso, Kyaftin Ibrahim Traoré, ya bayyana cewa kasarsa ta zama abin misali a duniya, saboda sauyin da jama’a suka bukata tun lokacin da ya hau mulki a 2022.
“Domin cimma cikakken ‘yancin kai, ya zama dole a bi juyin juya halin inji shi a wani jwabi ta gidan talabijin a jajaribin cika shekaru 65 na samun ‘yancin kai na kasar.
Burkina Faso a yau ta zama misali, abin koyi, kuma tana kan hanya madaidaiciya.
Duniya na kallonmu, kuma ba mu da wani zabi illa mu yi nasara,” in ji Traoré.
A fannin yaki da ta’addanci, shugaban kasar Burkina Faso ya dage cewa sojojin kasar sun kaddamar da hare-hare masu karfi a cikin shekarar da ta gabata a yankunan da a da ake daukar su a matsayin wuraren da abokan gaba ke iko.
An kwace yankuna da dama a cikin wata guda, inda sojojinmu suka kafa sansani.
“Waɗannan masu laifi waɗanda suka mamaye yankunan ƙasarmu, suna ganin cewa mafakarsu ce, an kore su kuma suna tserewa daga Burkina Faso.
Amma muna gaya musu cewa yanzu suna da zaɓi biyu kawai: su gudu daga Burkina Faso ko su mutu saboda sojojinmu suna kan daga.
Traoré ya yi kira ga mutanen Burkina da su hadu waje daya don tunkarar kalubalen da suka shafi ci gaban kasar, musamman masana’antu da ci gaban tattalin arziki da zamantakewa don amfanin al’ummar kasar baki ɗaya.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Ayatollah Khamenei : Iran na samun ci gaba duk da kalubale da dama December 11, 2025 Iran da Kazakhstan Sun rattaba hannun kan yarjeniyoyi da dama a tsakaninsu December 11, 2025 Hamas : Isra’ila ta gaza cika alkawarin da ta dauka kan yarjejeniyar tsagaita wuta December 11, 2025 Kasashen ECOWAS sun rage kudin sufirin jiragan sama a tsakaninsu December 11, 2025 Dakarun IRGC 3 Sun Yi Shahada A wani Harin Ta’addanci A Kudancin Kasar Iran December 11, 2025 Hamas: HKI Tana Ci Gaba Da Keta Bangaren Farko Na Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza December 11, 2025 Iran Ta Yi Tir Da Yanke Tallafin Da MDD Take Bawa Yan Gudun Hijiran Afganistan December 11, 2025 Ansarallah: Dole Ne Kasar Yemen Ta Tsarin Musulunci Na Kaiwa Ga Daukaka December 11, 2025 Shugaban Iran Ya Isa Astana Babban Birnin Kazakhstan December 11, 2025 ECOWAS ta bukaci waware batutuwa na siyasa ta hanyoyin lumana a yammacin Afirka December 11, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci