HausaTv:
2025-04-26@05:52:24 GMT

Namibiya ta janye bizar shiga ga wasu manyan kasashe na duniya

Published: 11th, April 2025 GMT

Namibiya ta janye bayar da biza ga Amurka, Burtaniya, da wasu kasashe sama da 30.

Matakin, wanda majalisar ministocin Namibiya ta yanke tun a watan Yuli, ya fara aiki ne a ranar 1 ga Afrilu.

Ya zuwa yanzu, galibin kasashen Turai, ciki har da Jamus, babbar tushen yawon bude ido a Namibiya, sun ci gajiyar shigowa kasar ba tare da biza ba.

Sabuwar shugabar Namibiya da aka rantsar, Netumbo Nandi-Ndaitwah, tana ci gaba da shirye-shiryen soke bizar shiga kasar ga wasu Karin kasashe, ta yadda ‘yan kasashen za su iya shiga Namibia ba tare da biz aba.

Manufar hakan dai ita ce kafafa harkokin kasuwanci da yawon bude ido a kasar ga yan kasashen ketare, da kuma karfafa kawance da sauran kasashe.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

DAGA LARABA: Dalilan Rashin Wutar Lantarki A Wasu Jihohin Arewa

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Wutar lantarki ta zama tamkar gwal a wasu sassan Arewacin Najeriya, inda a wasu yankuna aka ba da rahoton samun ta sa’o’i biyu kawai a rana, wasu kuma ba sa samun ko daidai da dakika ɗaya.

Masu ƙananan sana’o’i suna kallon rayuwarsu da kasuwancinsu suna durƙushewa yayin da kayan sana’arsu suke lalacewa saboda rashin wuta.

NAJERIYA A YAU: Matsayin Mataimakin Shugaban Ƙasa A Tsarin Mulkin Najeriya? DAGA LARABA: Dalilan Ɓaraka A Tsakanin Iyayen Riƙo Da Ƴaƴan Riƙo

Shirin Daga Laraba na wannan makon zai yi nazari ne a kan wannan matsala da yadda take taɓa rayuwar al’umma da hanyoyin magance ta.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Bude Taron Dandalin Tattaunawar Afirka Ta Yamma Karo Na Farko A Senegal
  • Duniyarmu A Yau: Shiri Kasashen Yamma Na Kashe Dukkan Falasdinwa A Gaza
  • Tabbas Amurka Za Ta Cije A Yakin Haraji Da Ta Kaddamar A Duniya
  • 2027: Baba-Ahmed Ya Bukaci Tinubu Ya Janye, Ya Bar Matasa Su Yi Takara 
  • Iran ta jinjinawa Sin da Rasha a matsayin kawayenta na kut-da-kut
  • Jiragen yakin Amurka sun kara kai hari kan kasar Yemen
  • Xi: Yake-yaken Haraji Da Kasuwanci Na Tauye Hakkoki Da Muradun Dukkan Kasashe
  • Iran Ta Sami Lambobin Yabo  8 A Wasan Taekwondo Na Duniya
  • Rage Mace-Macen Mata Da Jarirai: Kasar Sin Ta Ba Da Kyakkyawan Misali Ga Kasashe Masu Tasowa
  • DAGA LARABA: Dalilan Rashin Wutar Lantarki A Wasu Jihohin Arewa