HausaTv:
2025-06-15@15:37:33 GMT

Namibiya ta janye bizar shiga ga wasu manyan kasashe na duniya

Published: 11th, April 2025 GMT

Namibiya ta janye bayar da biza ga Amurka, Burtaniya, da wasu kasashe sama da 30.

Matakin, wanda majalisar ministocin Namibiya ta yanke tun a watan Yuli, ya fara aiki ne a ranar 1 ga Afrilu.

Ya zuwa yanzu, galibin kasashen Turai, ciki har da Jamus, babbar tushen yawon bude ido a Namibiya, sun ci gajiyar shigowa kasar ba tare da biza ba.

Sabuwar shugabar Namibiya da aka rantsar, Netumbo Nandi-Ndaitwah, tana ci gaba da shirye-shiryen soke bizar shiga kasar ga wasu Karin kasashe, ta yadda ‘yan kasashen za su iya shiga Namibia ba tare da biz aba.

Manufar hakan dai ita ce kafafa harkokin kasuwanci da yawon bude ido a kasar ga yan kasashen ketare, da kuma karfafa kawance da sauran kasashe.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda mota ta kashe mutum 8 ’yan gida daya bayan dawowa daga yawon Sallah a Kaduna

Wani mummunan hatsarin mota a hanyar Kaduna zuwa Zariya ya yi sanadin mutuwar mutum takwas ’yan gida daya, yayin da wasu mutum biyu ke can kwance a asibiti rai a hannun Allah.

Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne wajen misalin karfe 6:00 na yammacin ranar Litinin a garin Barakallahu da ke kan hanyar Kaduna zuwa Zariya, ana tsaka da bukukuwan Babbar Sallah.

A cewar rahotannin, lamarin ya faru ne lokacin da wata mota da ke tsala gudu ta kwace sannan ta danne mutanen da ke tsaye a gefen hanya bayan dawowarsu daga yawon sallah.

Sojoji sun kashe kasurguman ’yan bindiga 3 a Zamfara Mutum ɗaya ya tsira da ransa cikin 242 a hatsarin jirgin India

A cewar mahaifin mamatan, Malam Jamilu Usman Maiyadi, wata mota kirar GLK Marsandi mai ruwan toka ce ta take iyalan nasa, kuma wani yaro ne yake tuka ta.

Sai da a cewarsa, yaron wanda suka yi ittifakin dan gidan wani fitaccen dan siyasa ne a yankin, ya cika wandonsa da iska bayan faruwar lamarin.

Ya ce, “Mun rasa iyalai takwas ’yan gida daya a rana daya. Daga ciki akwai matata Khadija Umar da ’ya’yana su biyu sai kuma kanne da yayyen matar tawa da kuma wata gwaggonsu, duk sun mutu.

“A jimlance, mutum takwas kenan motar ta take; takwas sun mutu nan take, biyu kuma har yanzu suna asibiti,” in ji shi.

Malam Jamilu ya ce iyalan nasa na tsaye ne a bakin hanya suna jiran su sami motar da za ta kai su gida lokacin da motar ta kwace daga kan titi ta afka musu.

Ya kuma ce, “Tabbas motar na gudun wuce sa’a lokacin faruwar lamarin saboda kafar matata ta yi karayar da ba za a iya gyarawa ba, sannan sai jami’an hukumar kiyaye hadura ne ma daga baya suka gano wasu sassan jikin dana Sadiq,” Malam Jamilu ya fada fuskarsa cike da alhini.

‘Har da mai cikin wata takwas da za ta haifi tagwaye a cikin wadanda suka mutu’

Daga cikin wadanda suka rasu har da Zainab Muhammad wacce ke dauke da juna-biyun wata takwas da za ta haifi tagwaye.

Mijin marigayiyar, Sulaiman Abdulkadir Mai Shinkafa, wanda malamin addini ne a Hayin Rigasa, ya bayyana lamarin a cikin alhini.

Ya ce, “Ta kusa haihuwa. Mun riga mun sayi duk kayan jarirai muna shirye-shiryen haihuwar. Har mun ma sanya wa jariran sunan Hassan da Hussaini. Sannan akwai danmu mai shekara shida mai suna Khalid da aka kashe.

“An take matar tawa, sannan dana sai da muka kankaro namansa da katako kafin a yi musu jana’iza. Abu ne da babu wanda zai yi fatan ya gani a rayuwarsa.”

‘Ko uffan iyalan yaron da ya take mu ba su ce mana ba’

Kamar sauran masu alhinin, Malam Sulaiman ya nuna takaici kan yadda ya ce iyalan yaron da gwamnati sun yi watsi da su ko uffan ba su ce musu ba.

“Babu wani daga cikin iyalan yaron, wanda dan wani fitaccen dan siyasa ne a yankin da ya tuka motar, ko kuma daga gwamnatin jihar Kaduna da ya zo ya yi mana ta’aziyya.

“Ko uffan ba su ce mana ba. hatta mahaifin direban motar bai zo ba, sai ka ce yaruwar iyalan namu ba ta da wani amfani,” in ji shi.

Hukumar Kiyaye Hadura ta Kasa (FRSC) ta tabbatar da faruwar lamarin inda ta alakanta shi da gudun wuce sa’a da kuma kwacewar mota a kan hanyar da ba a jima da dauke ruwan sama ba.

Kwamandan shiyya na hukumar a Kaduna, Tijjani Iliyasu ne ya tabbatar da hakan.

Sai dai ya ce sun mika lamarin zuwa hannun ’yan sanda domin fadada bincike a kai.

Kazalika, duk kokarin wakilinmu na jin ta bakin rundunar ’yan sandan Kaduna da gwamnatin jihar sun ci tura saboda sun ki cewa komai a kai.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wutar lantarki ta kashe mutum 5, ta jikkata 13 a Gombe
  • Sin Ta Harba Tauraron Dan Adam Na Lura Da Yanayin Bala’u
  • Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi
  • DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci
  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Bude Kofofin Jahannama Ga Yahudawan Sahayoniyya
  • Taron Koli Na Sin Da Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu Zai Ingiza Manufar Kara Dunkulewar Sassan Yankin
  • Kamfanonin Waje Sun Ce Dole Ne Su Shiga A Dama Da Su A Cikin Kasuwar Kasar Sin
  • Nijeriya Ce Ta 3 A Manyan Kasashe Masu Karfin Masana’antu 10 Na Afirka
  • Yadda mota ta kashe mutum 8 ’yan gida daya bayan dawowa daga yawon Sallah a Kaduna
  • Ranar Tattaunawa Tsakanin Wayewar Kan Kasa Da Kasa: Sabon Tunani Don Wanzar Da Zaman Lafiya Da Daidaito A Duniya