Shugaban kasar Amurka Donal Trump yayi barazanar karwa kasar China kasha 50% na kudaden fiton da zata karba daga kayakin kasar China da zasu shiga kasar, idan har bata janye maida martanin da tayi na kasha 34% dai dai karin kudin fito da Amurka ta kara mat aba.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto shugaban yana fadar haka a shafinsa na yanar gizo wato ‘Trump Social”.

Kafin haka dai shugaban kasar Amurka ya karawa kasashen duniya da dama wadanda suke huldar kasuwanci da ita kudaden fito na kayakin da suke shigo da su Amurka daga cikin har da kasar China inda Trump ya kara mata kasha 34% na dukkan kayakin China da suke shiga Amurka. Amma kwana guda bayan haka kasar China ta maida martani da kasha 34% na dukkan kayakin Amurka da suke shiga kasar China.

Amma Trump ya bawa kasar China zuwa jiya litinin 8 ga watan Afrilu da muke cikin, na ta janye karin da ta yi wa kayakin Amurka masu shiga China ko kuma ya kara wa kasar ta China kasha 50% kari kan nafarko kan kayakin kasar China masu shigowa Amurka.

Banda yake Trump yace zai dakatar da duk wata tattaunawa da kasar China kan wannan batun. Amma zata bude tattaunawa da sauran kasashen da basu maida martani ba.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasar China

এছাড়াও পড়ুন:

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu ya rattaba hannu kan sababbin dokokin haraji
  • Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada
  • Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Ba Da Gudunmuwa Ga Habakar Tattalin Arzikin Duniya
  • Afirka CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwa Kan Kiwon Lafiya Da Kasar Sin
  • Sin Ta Sha Alwashin Rarraba Fasahohinta Na Ainihi Da Dabarunta Na Kirkire-Kirkire Tare Da Sauran Sassan Kasa Da Kasa
  • Za mu ci gaba da tattaunawa da Iran kan yarjejeniyar nukiliya — Trump
  • Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?
  • Gwamnatin Nijeriya ta yi wa Amurka martani kan barazanar tsaro a Abuja
  • Trump ya soki Iran da Isra’ila kan saɓa wa yarjejeniyar tsagaita wuta
  • An tura ’yan China 6 kurkuku kan laifin ta’addanci a Nijeriya