Pezeshkian: Dole ne Amurka ta tabbatar da cewa da gaske take yi a game da tattaunawa
Published: 8th, April 2025 GMT
Shugaban Iran Masoud Pezeshkian ya ce kasarsa ta yi imani da tattaunawa, amma ba a karkashin wulakanci da kaskanci ba.” Ya jaddada cewa Iran ba ta neman yaki, ko tada zaune tsaye, ko kuma mallakar makamin nukiliya, yana mai kira ga kasashen duniya da su amince da hakan.
Pezeshkian ya bayyana hakan ne a yammacin Lahadin da ta gabata, yayin wata ganawa da wakilan jam’iyyun siyasa da manyan kungiyoyi a kasar, inda ya tattauna batutuwan da suka shafi sauye-sauyen harkokin mulki, da manufofin harkokin waje, da kalubalen tattalin arziki da zamantakewar kasar.
Da yake magana game da kalubalen gudanar da harkokin mulki, shugaban na Iran ya bayyana cewa, ba za a iya cimma gyara halayen kungiyoyi da bangarorin gwamnati ta hanyar canza daidaikun mutane ba, sai dai hakan yana bukatar “sauyi na dabi’un hukumomi na dogon lokaci,” yana mai jaddada cewa, “sauyi na hakika yana daukar shekaru goma.
Dangane da batutuwan da suka shafi zamantakewa, Pezeshkian ya jaddada cewa ba za a iya magance rikice-rikice ta hanyar ba da umarni kadai ba, yana mai bayanin cewa gwamnati na da shirye-shirye don magance matsalolin da suka hada da karancin makarantu, tsadar rayuwa, rashin aikin yi, da rashin daidaiton tattalin arziki, amma “bai takaitu ga samar da shirye-shirye kawai ba.
Dangane da manufofin ketare kuwa, ya yi nuni da cewa, Iran ta tattauna da dukkan shugabannin kasashen yankin a daidai lokacin da ake gudanar da bukukuwan Sallah, inda ya jaddada cewa, dangantakar da ke tsakaninta da kasashen da ke makwabtaka da ita ta inganta idan aka kwatanta da baya.
Amma ya kara da cewa, “Tattaunawa da Amurka wani lamari ne na daban,” yana mai bayanin cewa, “Lokacin da Washington ta matsa mana lamba kuma ta ci gaba da barazanarta, ta yaya za mu yi shawarwari da ita?”
Shugaban na Iran ya yi nuni da cewa, matsayin kasarsa na lumana kan amfani da makamashin nukiliya, ba wai kawai maganganun siyasa ba ne, a’a, a maimakon haka a kan wata fatawa ta addini da Jagoran juyin juya halin Musulunci ya fitar ne, wadda ta haramta amfani da makamashin nukiliya ta hanyoyi da ba na ayyukan farar hula ba.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: jaddada cewa
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Najeriya Ta Yi Allawadai Da Harin Da “Isra’ila” Ta Kawo Wa Iran
A wata sanarwa da ma’aikatar harkokin wajen Najeriya ta fitar, ta yi tir da harin na Isra’ila akan Iran tare da bayyana cewa, ya haifar da rikici a tsakanin bangarorin biyu da kuma musayar harba makamai masu linzami.
Gwamnatin ta Najeriya ta nuna bakin cikinta akan abinda ya faru, tare da kuma da yin kiran a tsagaita wutar yaki da gaggawa, da kai zuciya nesa.
Har ila yau, sanarwar ma’aikatar harkokin wajen ta Nigeria wacce kakakinta Kimiebi Imomotimi Ebienfa ya rattabawa hannu a yau Asabar,14 ga watan Yuni 2025, ta jaddada cewa; yaki ba zai maye gurbin tattaunawa ba, kuma hanyar diplomasiyya ce za ta kai ga samar da zaman lafiya mai dorewa, girmama juna da aiki da dokokin kasa da kasa.,