Shugaban Iran Masoud Pezeshkian ya ce kasarsa ta yi imani da tattaunawa, amma ba a karkashin wulakanci da kaskanci ba.” Ya jaddada cewa Iran ba ta neman yaki, ko tada zaune tsaye, ko kuma mallakar makamin nukiliya, yana mai kira ga kasashen duniya da su amince da hakan.

Pezeshkian ya bayyana hakan ne a yammacin Lahadin da ta gabata, yayin wata ganawa da wakilan jam’iyyun siyasa da manyan kungiyoyi a kasar, inda ya tattauna batutuwan da suka shafi sauye-sauyen harkokin mulki, da manufofin harkokin waje, da kalubalen tattalin arziki da zamantakewar kasar.

Da yake magana game da kalubalen gudanar da harkokin mulki, shugaban na Iran ya bayyana cewa, ba za a iya cimma gyara halayen kungiyoyi da bangarorin gwamnati ta hanyar canza daidaikun mutane ba, sai dai hakan yana bukatar “sauyi na dabi’un hukumomi na dogon lokaci,” yana mai jaddada cewa, “sauyi na hakika yana daukar shekaru goma.

Dangane da batutuwan da suka shafi zamantakewa, Pezeshkian ya jaddada cewa ba za a iya magance rikice-rikice ta hanyar ba da umarni kadai ba, yana mai bayanin cewa gwamnati na da shirye-shirye don magance matsalolin da suka hada da karancin makarantu, tsadar rayuwa, rashin aikin yi, da rashin daidaiton tattalin arziki, amma “bai takaitu ga samar da shirye-shirye kawai ba.

Dangane da manufofin ketare kuwa, ya yi nuni da cewa, Iran ta tattauna da dukkan shugabannin kasashen yankin a daidai lokacin da ake gudanar da bukukuwan Sallah, inda ya jaddada cewa, dangantakar da ke tsakaninta da kasashen da ke makwabtaka da ita ta inganta idan aka kwatanta da baya.

Amma ya kara da cewa, “Tattaunawa da Amurka wani lamari ne na daban,” yana mai bayanin cewa, “Lokacin da Washington ta matsa mana lamba kuma ta ci gaba da barazanarta, ta yaya za mu yi shawarwari da ita?”

Shugaban na Iran ya yi nuni da cewa, matsayin kasarsa na lumana kan amfani da makamashin nukiliya, ba wai kawai maganganun siyasa ba ne, a’a, a maimakon haka a kan wata fatawa ta addini da Jagoran juyin juya halin Musulunci ya fitar ne, wadda ta haramta amfani da makamashin nukiliya ta hanyoyi da ba na ayyukan farar hula ba.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: jaddada cewa

এছাড়াও পড়ুন:

Ana zargin mace da kashe ’yar uwarta a kan N800 din barkono

Rundunar ’Yan Sanda ta Jihar Ondo ta tabbatar da kama wata mata mai suna Iluyemi Bosede bisa zargin kashe yayarta, Tewogboye Omowumi, a Akure, babban birnin jihar.

A cewar sanarwar da Jami’in Hulɗa da Jama’a na rundunar, Olayinka Ayanlade, ya fitar a ranar Talata, ya ce lamarin ya faru ne a ranar shida ga Satumba, 2025, bayan wata sa’insa da ta kaure tsakanin matar da marigayiyar kan Naira 800.

Tun Tinubu yana Gwamna ba abin da ya fi shahara da shi kamar tara haraji – Adebayo DAGA LARABA: Dalilan Tashin Farashin Doya A Wasu Kasuwannin Najeriya

Jami’in ya bayyana cewa Bosede ta ture ’yar uwarta har ta faɗi ƙasa, lamarin da ya haifar da mutuwarta.

Ya ce, “Binciken farko ya nuna cewa Iluyemi Bosede ta je wurin yayar tata, Tewogboye Omowumi mai shekaru 35, domin karbar bashinta na N800 na kudin tumatir da barkono. Sai dai tankiyar da ta fara a matsayin ƙaramin sabani ta rikide zuwa tashin hankali, inda ake zargin Bosede ta riƙe kayan marigayiyar har ta faɗi ƙasa.”

“Abin takaici, duk da an garzaya da marigayiyar asibiti don samun kulawar gaggawa, likitoci sun tabbatar da mutuwarta tun kafin a fara ba ta taimako. Wannan lamari ya nuna yadda ƙaramin sabani zai iya rikidewa zuwa mummunar husuma idan ba a magance shi cikin lumana ba.”

Bayan faruwar lamarin, rundunar ta ce ta kama wadda ake zargi kuma tana tsare da ita a halin yanzu, yayin da bincike ke ci gaba.

Rundunar ta kuma tabbatar da cewa za a gurfanar da wadda ake zargin a gaban kotu bayan kammala bincike, domin ta girbi abin da ta shuka.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu bai shirya gudanar da sahihin zaɓe ba a 2027 – Buba Galadima
  • Iran da Saudiyya sun bukaci hadin Musulmi game da halin da ake ci a yankin
  • Ana zargin mace da kashe ’yar uwarta a kan N800 din barkono
  • Najeriya Na Asarar Dala Biliyan 10 Bayan Girbi Duk Shekara- Gwamnatin Tarayya
  • Pezeshkian: Saudiyya Na Iya Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Samar Da Hadin Kan Kasashen Musulmi
  • Pezeshkian: Ya kamata kasashen musulmi su yanke alaka da gwamnatin sahyoniya tare da kiyaye hadin kai
  • Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu
  • Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin
  • Dole sai mun tantance wa’azi kafin a yi —Gwamnan Neja
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Qatar, Turkiyya, Pakistan Da Labanon A Doha