Nijar ta ayyana harshen Hausa a matsayin na kasa
Published: 8th, April 2025 GMT
Jamhuriyar Nijar ta ayyana harshen Hausa a matsayin na kasa, yayin da Faransanci ya zama harshen aiki mai sauki, don haka, Faransanci ba yaren hukuma ne ba.
Matakin dai ya dogara ne da shawarwarin da babban taron kasar ya gabatart a watan Fabrairu, wanda kuma shugaban kasar Janar Abdourahamane Tiani ya amince da shi a ranar 26 ga Maris.
A yanzu sabon kundin tsarin mulkin kasar ya jera harsuna goma sha daya da ake magana da su na Nijar, inda ya amince da Hausa a matsayin harshen kasa.
Harshen Hausa dai shi ne yaren da aka fi amfani da shi a duk fadin Nijar.
A kwanakin baya sabbin hukumomin kasar da ke da suka raba gari da kasar faransa wacce ta yi wa kasar mulkin mallaka, ta fice daga kungiyar bunkasa harshen faransaci ta OIF.
Sannan kuma a baya-bayan nan kasar ta sauya sunayen wasu tituna a birnin Yamai masu dauke da sunayen Faransanci, a wani mataki na kawo karshen duk wata alama ta mulkin mallaka na turawan faransa.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Sin Na Maraba Da Karin Abokai Daga Kasa Da Kasa Su Ziyarci Kasar
Guo Jiakun ya bayyana cewa, a ranar 26 ga wannan wata, hukumomin Sin masu ruwa da tsaki sun gabatar da sabbin matakan mayar da kudin haraji ga baki masu yawon bude ido, lamarin da ya kyautata manufar mayar da kudin haraji tun daga lokacin sayayya da kawo sauki ga baki masu sayayya. (Zainab Zhang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp