Nijar ta ayyana harshen Hausa a matsayin na kasa
Published: 8th, April 2025 GMT
Jamhuriyar Nijar ta ayyana harshen Hausa a matsayin na kasa, yayin da Faransanci ya zama harshen aiki mai sauki, don haka, Faransanci ba yaren hukuma ne ba.
Matakin dai ya dogara ne da shawarwarin da babban taron kasar ya gabatart a watan Fabrairu, wanda kuma shugaban kasar Janar Abdourahamane Tiani ya amince da shi a ranar 26 ga Maris.
A yanzu sabon kundin tsarin mulkin kasar ya jera harsuna goma sha daya da ake magana da su na Nijar, inda ya amince da Hausa a matsayin harshen kasa.
Harshen Hausa dai shi ne yaren da aka fi amfani da shi a duk fadin Nijar.
A kwanakin baya sabbin hukumomin kasar da ke da suka raba gari da kasar faransa wacce ta yi wa kasar mulkin mallaka, ta fice daga kungiyar bunkasa harshen faransaci ta OIF.
Sannan kuma a baya-bayan nan kasar ta sauya sunayen wasu tituna a birnin Yamai masu dauke da sunayen Faransanci, a wani mataki na kawo karshen duk wata alama ta mulkin mallaka na turawan faransa.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo
ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma October 30, 2025
Daga Birnin Sin Babban Daraktan Sakatariyar APEC: Sin Tana Ba Da Gudummawar Ba Da Jagoranci A APEC October 30, 2025
Daga Birnin Sin Kasar Sin Ce Ke Da Sama Da Rabin Muhimman Makaloli Na Duniya October 30, 2025