HausaTv:
2025-08-06@22:03:33 GMT

Ana Ci Gaba Da Kai Ruwa Rana Takanin Amurka Da China Kan Batun Harajin Fito

Published: 6th, April 2025 GMT

Gwamnatin kasar Sin ta yi kakkausar suka da bayyana adawarta ga matakin Amurka na kakaba “harajin fito na ramuwar gayya.”

A cikin wata sanarwar da ta fitar, ta yi Allah-wadai da matakin na Amurka, wanda ya kasance daukar mataki bisa radin kai, da kuma kariyar cinikayya da cin zarafin tattalin arziki.

Sanarwar ta kara da cewa, ta hanyar fakewa da abin da take kira “ramuwar gayya” da “adalci,” a zahiri dai Amurka ta tsunduma a aiwatar da dabarun danniya da babakere, tana neman cimma manufarta ta “Amurka na gaba da komai” da kuma “Amurka ta fi kowace kasa.” Har ila yau, Amurka na amfani da harajin fito don kawo cikas ga tsarin tattalin arziki da cinikayya na kasa da kasa, tare da fifita muradun Amurka sama da moriyar bai daya ta duniya, tare kuma da sadaukar da halaltattun muradun kasashen duniya don cimma burin Amurka.

A ranar Laraba ne dai shugaban Amurka Donald Trump ya sanar da wani sabon tsarin haraji, inda ya sanya mafi kankantar harajin fito kashi 10 cikin dari kan kayayyakin da ake shigowa da su daga dukkan kasashe abokan huldar cinikayyarta da kuma karin sama da hakan kan waasu kasashen. Bayan matakin na Amurka, a ranar Juma’a kasar Sin ta sanar da cewa, za ta sanya karin harajin fito kashi 34 cikin dari kan dukkan kayayyakin da ake shigowo da su daga Amurka daga ranar 10 ga watan Afrilu, wanda ya yi daidai da harajin fito na ramuwar gayya da Amurka ta kakaba kan kayayyakin da ake shigowa da su kasar Sin.

A cikin sanarwar da gwamnatin kasar Sin ta fitar yau Asabar ta ce, kasar Sin ta dauki kuma za ta ci gaba da daukar kwararan matakai don kiyaye ‘yancinta, da tsaro, da muradunta na samun ci gaba.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasar Sin ta harajin fito

এছাড়াও পড়ুন:

Rasha Zata Kara Kyautata Dangantaka BRICS don Magance Takunkuman Amurka A Kanta

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Rasha ta bayyana cewa kasar Rasha tana shirin kara dankon zumunci da kungiyar Brics saboda fuskantar takunkuman tattalin arziki wadanda kasar Amurka ta daura mata.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Maria Zakharova kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Rasha tana fadar haka, ta kuma kara da cewa, kungiyar BRICS kungiya ce wace kasar Rasha ta dogara da ita don magance irin wadannan matsaloli. Sannan kasashen iya magance takunkuman tattalin arzikin da kasashen yamma musamman Amurka suke dorawa kasar Rasha.

Zakharova, ta kara da cewa kasashen Global south da BRICS sune kawayen Rasha a kan abinda ya mshafi matsalolin takunkuman tattalin arziki da kuma kawayenta a cikin harkokin siyasar duniya.

Zakharova ta kara da cewa “Kudaden fito wadanda Amurka take  dorawa kasashen duniya musamman kasashen Global South yana tauye kasancewarsu kasashen masu yenci kuma kokari ne na shishigi a cikin harkokin gida na wadannan kasashe.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Gagarumar Zanga-Zang A birnin Paris Na kasar Faransa Saboda Killace Gaza August 5, 2025 Burtaniya Zata Fara maida yan Gudun Hijira Zuwa Faransa Bisa Wata Sabuwar Yarjeniya August 5, 2025 Borrell: Rashin tabuka komai daga Turai ya karfafa gwiwar Isr’ila wajen aikata laifuka August 5, 2025 UNICEF: Akalla yara 28 ne ke mutuwa a kowace rana a Gaza sakamakon harin Isra’ila da yunwa August 5, 2025 Baghaei : Ziyarar Pezeshkian a Pakistan ta bude wani sabon Shafin alaka August 5, 2025 Afirka ta Kudu ta zayyana matakan tallafi ga ‘yan kasuwa na cikin gida a matsayin martani ga harajin Trump August 5, 2025 Hamas ta musanta kalaman Witkoff game da batun mika makamanta August 5, 2025 Araqchi: Namijin kokarin al’ummar Iran abin yabawa ne August 4, 2025 Khatibzadeh: Iran ba za ta amince da saryar da hakkokinta ba a duk wata tattaunawa da Amurka August 4, 2025 Rahotonni: Agajin Jin kai Da Ake Jefawa Ta Sama A Gaza Ba Shi Da Tasiri August 4, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Ta Samar Da Yuan Biliyan Daya Domin Ayyukan Jin Kai Sakamakon Ibtila’in Ambaliyar Ruwa
  • Batun Ceto Wanda Ake Zargi Da Kwaya: Kwamishinan Kano Ya Yi Murabus
  • Rasha Zata Kara Kyautata Dangantaka BRICS don Magance Takunkuman Amurka A Kanta
  • UNICEF: Akalla yara 28 ne ke mutuwa a kowace rana a Gaza sakamakon harin Isra’ila da yunwa
  • Afirka ta Kudu ta zayyana matakan tallafi ga ‘yan kasuwa na cikin gida a matsayin martani ga harajin Trump
  • Kasar Iran Ko Da Zata Sake Tattaunawa Da Amurka Zata Kasance Dauke Da Makamai Cikin Shirin
  • Cinikin Kamfanoni a Kasar Sin Ya Ci Gaba Da Habaka Cikin Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Bana 
  • Wasu Kungiyoyi Sun Yi Kira Ga Dan Majalisa Aminu Sani Jaji Ya Fito Takarar Gwamnan Zamfara 
  • Rasha da China sun fara wani gagarumin atisayen soji na hadin gwiwa a tekun Japan
  • Gwamnatin Jigawa Ta Dauki Manyan Matakan Kare Jihar Daga Ambaliyar Ruwa