Amurka ta sanar da soke duk wata takardar izinin shiga kasar wato (visa) da kasar ta baiwa duk wani dan Sudan ta Kudu.

Matakin a cewar Amurka na da nasaba ne da yadda Sudan ta Kudun ta ki karbar ‘yan kasarta da aka kora daga kasar.

A cikin wata sanarwa da sakataren harkokin wajen Amurka Marco Rubio ya fitar, ya ce ‘’ma’aikatar harkokin wajen Amurka ta soke duk bizar kasar da ‘yan Sudan ta Kudu ke rike da a nan take.

Wannan shi ne irin matakin farko da aka dauka kan wasu ‘yan kasa a duniya tun bayan da Donald Trump ya koma kan karagar mulki a ranar 20 ga watan Janairu, a tsauraran manufofinsa na yaki da bakin haure.

Babban jami’in diflomasiyyar na Amurka ya kara da cewa lokaci ya yi da gwamnatin rikon kwaryar Sudan ta Kudu za ta daina samun wani tagomashi daga Amurka.

Kaddamar da dokar ta shige da fice na kasarmu yana da matukar mahimmanci ga tsaron kasa da amincin jama’a na Amurka.

Dole ne kowace kasa ta amince ta karbi yan kasarta da aka kora nan da nan inji gwamnatin ta Amurka inji shi.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Talata ce ɗaya ga watan Zhul Qi’ida — Sarkin Musulmi

Sarkin Musulmi, Alhaji Abubakar Muhammad Sa’ad, ya bayyana cewa gobe Talata, 30 ga watan Afrilun 2025, ita ce za ta kasance 1 ga watan Zhul Qi’ida na shekarar 1446 ta Hijiriyya.

Wata sanarwa da shugaban kwamatin ganin wata na fadar, Farfesa Sambo Wali ya fitar ta ce an ɗauki matakin ne saboda ba a ga jinjirin watan ba a ranar Lahadi.

Yadda matar gwamna ta sa mata gasar haihuwar ’yan uku Rasha ta ayyana tsagaita wuta ita kaɗai a yakinta da Ukraine

Hakan na nufin yau Litinin, 28 ga watan Afrilu ne 30 ga watan Ƙaramar Sallah na Shawwal.

A ƙa’idar kalandar Musulunci, kowane wata yana yin kwana 29 ne, amma idan ba a ga jaririn watan ba sai a cika shi zuwa kwana 30.

Aminiya ta ruwaito cewa tun a ranar Asabar da ta gabata ce Fadar Sarkin Musulmin ta ba da umarnin duban watan na Zhul Qi’ida.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Xi Ya Jaddada Muhimmancin Tsara Nagartaccen Shirin Raya Tattalin Arziki Da Zamantakewar Al’umma Tsakanin 2026-2030
  • Nazarin CGTN: Ana Kara Bayyana Rashin Gamsuwa Da Sabuwar Gwamnatin Amurka Daga Ciki Da Wajen Kasar
  • Jaridar The Guardian Mafi Yawan ‘Yan Gudun Hijiran Sudan Ne A Gidan Yarin Kasar Girka
  • Wani abin fashewa ya kashe mutum 26 a Borno
  • Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya
  • Babu Wata Tattaunawa Tsakanin Sin Da Amurka Game Da Batun Haraji
  • Sin Na Maraba Da Karin Abokai Daga Kasa Da Kasa Su Ziyarci Kasar
  • Talata ce ɗaya ga watan Zhul Qi’ida — Sarkin Musulmi
  • Tawagar ‘Yan Sama Jannati Na Shenzhou 19 Za Su Dawo Doron Kasa A Ranar Talata
  • Kasar Sin Za Ta Samar Da Dokar Da Ta Shafi Raya Kasa