Rasha za ta bude ofishin jakadanci a Nijar nan ba da jimawa ba
Published: 6th, April 2025 GMT
Ministan harkokin wajen kasar Nijar ya sanar da cewa nan ba da jimawa ba za a Rasha za ta aika tawagar diflomasiyya a Nijar.
Nijar ta tabbatar da aniyar ta na karbar bakuncin ofishin jakadancin Rasha a karon farko cikin sama da shekaru talatin, in ji ministan harkokin wajen kasar ta yammacin Afirka, Bakari Yaou Sangare a ranar Alhamis.
Bayanin ya fito ne yayin wani taron manema labarai na hadin gwiwa a birnin Moscow bayan tattaunawa tsakanin ministan harkokin wajen Rasha Sergey Lavrov da takwarorinsa na kasashen Nijar, Mali, da Burkina Faso.
M. Sangare ya bayyana cewa, a halin yanzu Nijar na neman wurin da ya dace domin gina ofishin jakadanci na tawagar diflomasiyyar Rasha a kasar, ya kara da cewa Yamai na fatan nan ba da jimawa ba Moscow za ta nada jakada.
‘’Mun rufe ofishin jakadancinmu a Rasha a cikin 1990s, amma daga baya mun gane cewa wannan kuskure ne,” in ji shi.
Lavrov ya tabbatar da cewa kasashen biyu suna kan hanyar dawo da wakilcin diflomasiyya. “A nan gaba kadan, tare da taimakon ku, za mu kammala dukkan ayyukan don dawo da ofishin jakadancinmu.
Kuma tabbas za mu yi hakan a cikin shekarar nan ta 2025,” in ji ministan harkokin wajen Rasha.
A farkon wannan shekara, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Rasha Maria Zakharova ta tabbatar da cewa, Moscow na da niyyar bude sabbin ofisoshin jakadanci a kasashen Afirka da dama da suka hada da Nijar, Saliyo, da Sudan ta Kudu.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: harkokin wajen
এছাড়াও পড়ুন:
An Fara Baje Kolin Kayakin Da Ake Kerawa A Iran Tare Da Taron Iran Da Afirka Karo Na Uku
An fara kasuwar baje koli na kayakin kasuwancin da ake samarwa a cikin Iran ko IRAN EXPO 2025, karo na 3 a nan Tehran.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa kasuwar baje koli na Iran EXPO 2025 zai jawa masu zuna jari daga kasashen Afirka.
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya fadawa kamfanin dillancin labaran IP kan cewa Kasuwar ta bana dai, za ta tara kamfanonin masu samar da kayaki daga yankuna daban daban na kasar Iran da dama, kuma akwai fatan cewa wannan kasuwar ta zama mabudi ga kyautatuwan tattalin arzikin kasar.
EXPO dai ita ce kasuwar baje koli na kayakin kasar Iran mafi girma wanda ake gudanarwa a ko wace shekara, sannan daga nan take samun kasuwa a kasashen duniya. Kuma yan kasuwa daga kasahe fiya da 100 ne suka shigo kasar don halattan kasuwar.
Esma’il Bakaee, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ya ce ya na fatan a wannan kasuwar, kasashen Afirka da Iran za su amfani juna a harkokin kasuwancin da ake bunkasa a tsakaninsu.