Guteress : ba wadan zai ci ribar yakin cinikayya
Published: 6th, April 2025 GMT
Sakatare janar na majalisar dinkin duniya ya ce ba wanda zai ci ribar yakin cinikayya a yayin da ake ta cacar baka kan harajin fito da shugaban Amurka Donald Trump ya lafta wa duniya.
Antonio Guitess ya yi wannan gargadin ta bakin kakakinsa inda ya yake bayyana cewa, “ba wanda ke yin nasara a yakin na cinikayya.
” Yana mai cewa, a yayin da ake samun karuwar adawa daga sassa daban daban, shugaban Amurka Donal Trump a ranar Laraba ya rattaba hannu kan wani umarnin zartarwa kan abin da yake kira “harajin fito na ramuwar gayya,” wanda ya sanya kashi 10 cikin dari na mafi karancin harajin fito, da karin sama da haka kan wasu abokan cinikayyar kasar.
A wani batun kuma, taron MDD kan cinikayya da ci gaba wato UNCTAD, ya yi gargadi a cikin wata sanarwa a ranar Juma’a cewa, harajin fito da Amurka ta sanya zai cutar da kasashe masu rauni, kana “tsarin cinikayya na duniya ya shiga wani mataki, wanda ke yin barazana ga ci gaba, da zuba hannun jari, musamman ga kasashe masu rauni,” yayin da manyan kasashe masu karfin tattalin arziki ke shirin sanya sabbin harajin fito a nasu bangare a matsayin ramuwar gayya ga matakin na shugaban Amurka.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: harajin fito
এছাড়াও পড়ুন:
Lebanon: Isra’ila Ta Kai Hari Akan Unguwar Dhahiya A Birnin Beirut
Jiragen yakin HKI sun kai hari a yankin Hangara dake unguwar “Dhahiya” a cikin birnin Beirut. Yankin da jiragen yakin na ‘yan sahayoniya su ka kai wa harin, yana cike da mutane da kuma makarantu biyu.
Jiragen yakin na HKI sun harba makamai masu linzami 3, da hakan ya haddasa tashin gobara.
A sanadiyyar wannan harin, an sami shahidi daya,yayin da wasu da dama su ka jikkata.
A ranar 1 ga watan Aprilu ma dai sojojin HKI sun kai wani harin a unguwar Dhahiya wanda ya yi sanadiyyar shahadar mutane 4 da kuma jikkata wasu da dama.
Tun bayan tsagaita wutar yaki a ranar 27 ga watan Aprilu 2025, HKI ta keta wutar yakin fiye da 2000.