Najeriya Da Ghana Sun Jaddada Aniyarrsu Wajen Kara Fadada Alakarsu A Dukkanin Bangarori
Published: 28th, March 2025 GMT
Shugaba Bola Tinubu da takwaransa na Ghana, John Mahama, sun tattauna batutuwa da dama domin karfafa alakar da ke tsakanin kasashen yammacin Afirka.
An gudanar da ganawar ne a Abuja bayan da Mahama ya kai wa Tinubu ziyarar ban girma domin yabawa da halartar shugaban Najeriya a yayin bikin rantsar da shi a Accra, babban birnin Ghana.
Wannan dai ya zo ne watanni biyu bayan rantsar da Mahama bayan day a sake komawa kan karagar shugabancin kasar Ghana.
Daga cikin muhimman batutuwa da shugabannin kasashen na Najeriya da Ghana suka yi dubi a kansu, hard a yadda za a kara karfafa alakoki a dukkanin bangaroria tsakanin kasashen biyu.
Baya ga haka kuma sun tabo batun rarrabuwar kawuna da aka samua tsakanin mabobin kungiyar ECOWAS, da kuma matakan day a kamata a dauka domin dinke wannan baraka, da hakan ya hada hard a shiga tattaunawa da kasashen da suka balle suka kafa nasu kawancen, wato Nijar, Burkina Faso da kuma Mali, domin samun fahimtar juna da kuma yin aike tare domin ci gaban yankin da al’ummominsa.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Wang Yi: Sin Na Maraba Da Dukkanin Matakai Na Dawo Da Zaman Lafiya A Gaza
Ministan wajen na Sin, ya kuma jaddada muhimmancin goyon bayan manufar kafa kasashe biyu masu cin gashin kai. Ya ce Sin a shirye take ta yi aiki tare da sassan kasa da kasa, ciki har da Switzerland, ta yadda za a kai ga cimma nasarar aiwatar da sahihan matakan wanzar da zaman lafiya da daidaito a Gabas ta Tsakiya. (Mai fassara: Saminu Alhassan)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA