Aminiya:
2025-06-15@11:39:58 GMT

Sallah: Hadimin gwamnan Sakkwato ya bai wa magoya bayan APC kyautar N22m

Published: 28th, March 2025 GMT

Mai Bai Wa Gwamnan Sakkwato Shawara kan Harkokin Karkara, Malami Muhammad Galadanchi (Bajare), ya bai wa magoya bayan jam’iyyar APC a jihar, kyautar Naira miliyan 22 domin gudanar da shagalin Sallah Karamar.

Yayin bayar da kyautar a ranar Alhamis, Bajare ya ce ya yi hakan ne domin nuna godiyarsa ga jagoran APC a jihar, Sanata Aliyu Magatakarda Wamakko, da Gwamna Ahmad Aliyu, bisa damar da suka ba shi don ba da gudunmawarsa ga ci gaban jihar.

An kashe ƙasurgumin ɗan bindiga Isuhu Yellow a Zamfara Hadimin Gwamnan Kano Tanka Galadanci ya rasu

“Wannan tallafi saƙon godiya ne daga shugabanninmu zuwa gare ku. Idan ba su ba mu dama ba, ba za mu iya wannan ba.

“Kuma muna shirye mu ƙara tallafawa a duk lokacin da buƙata hakan ta taso,” in ji shi.

Ya jinjina wa al’ummar Ƙaramar Hukumar Sakkwato ta Arewa, bisa sadaukarwar da suka yi wajen ganin jam’iyyar APC ta yi nasara, inda ya ce hakan ne ya sa suka cancantar a yi masu hidima.

Bajare, ya tabbatar da cewa zai ci gaba da tallafa wa magoya bayan jam’iyyar lokaci zuwa lokaci domin tabbatar da ci gaban tafiyar siyasarsu.

Dangane da tsarin rabon tallafin, ya ce kowane mutum da aka zaɓa zai amfana da kuɗi tsakanin Naira 100,000 zuwa miliyan ɗaya, ya danganta da matsayinsa.

Haka kuma ya yi fatan al’umma za su gudanar da shagalin sallah cikin lumana da kwanciyar hankali.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Kyautar Kuɗi Magoya Baya Sakkwato

এছাড়াও পড়ুন:

Mahara sun kashe mutum 26 a sabon hari a Binuwai

Aƙalla mutum 26 ne suka rasu sakamakon wasu sabbin hare-haren da aka kai wasu ƙauyuka a Jihar Binuwai.

Hare-haren sun faru ne a yankunan Ƙaramar Hukumar Makurdi da Katsina-Ala tsakanin ƙarfe 12 na dare zuwa 2 na daren ranar Alhamis.

Farashin fetur ya tashi a kasuwar duniya bayan harin Isra’ila a Iran An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasu

A Ƙaramar Hukumar Makurdi, wasu ’yan bindiga sun kai hari ƙauyukan Mtswenem da Akondotyough Bawa, inda suka kashe mutum 25.

Haka kuma, an kashe mutum ɗaya a wani hari daban da aka kai ƙauyukan Kenvanger da Agbami a Ƙaramar Hukumar Katsina-Ala.

Wasu mazauna yankin sun ce ’yan bindigar sun shiga gidajen mutane suna harbin su yayin da suke barci, suna amfani da bindigogi da adduna.

Wani wanda ya tsira mai suna Iorpuu, ya ce mata da yara suna cikin waɗanda aka kashe, kuma har yanzu ana neman wasu da suka ɓace.

Ya ƙara da cewa wasu sun mutu ne a kan hanyarsu ta zuwa asibiti.

Wani ganau ya ce an fara kai harin ne wani ƙauye kusa da Jami’ar Noma da Fasaha ta Makurdi, inda aka kashe mutane huɗu.

Daga nan suka wuce wani ƙauye a kusa da unguwar Low Cost suka ci gaba da kashe mutane har adadin gawarwakin ya kai 25.

A Katsina-Ala, ’yan bindigar sun kai hari ƙauyukan Kenvanger da Agbami da misalin ƙarfe 1 na dare.

An ce sun yi yunƙurin yi wa wasu matan da suka haihu fyaɗe, amma mazan ƙauyen suka kai musu ɗauki.

Wannan ya haifar da rikici inda ’yan bindigar suka buɗe wuta, suka kashe mutum ɗaya tare da raunata wasu.

A ƙauyen Agbami kuma, sun yi wa mutane da yawa dukan kawo wuƙa amma babu wanda ya mutu.

Kakakin rundunar ’yan sandan jihar, DSP Udeme Edet, ya tabbatar da cewa an tura jami’an tsaro zuwa yankunan da abin ya faru a Makurdi.

Ya ce za su ci gaba da bai wa ’yan jarida bayanai, amma har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, babu wani ƙarin bayani.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wutar lantarki ta kashe mutum 5, ta jikkata 13 a Gombe
  • Damina: NiMet ta gargaɗi jihohi 13 kan barazanar ambaliyar ruwa
  • Kula Da Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi
  • Mahara sun kashe mutum 26 a sabon hari a Binuwai
  • Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya
  • Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya
  • Pogba Na Shirin Komawa Monaco Bayan Dakatar Da Shi
  • An kama ’yar Najeriya da laifin safarar ɗalibai 15 a Australia
  • Gwamnan Gombe Ya Yi Allah Wadai Da Kisan Da ‘Yan Daba Suka Yi Wa Amadi Kasiran
  • Yadda mota ta kashe mutum 8 ’yan gida daya bayan dawowa daga yawon Sallah a Kaduna