Sallah: Hadimin gwamnan Sakkwato ya bai wa magoya bayan APC kyautar N22m
Published: 28th, March 2025 GMT
Mai Bai Wa Gwamnan Sakkwato Shawara kan Harkokin Karkara, Malami Muhammad Galadanchi (Bajare), ya bai wa magoya bayan jam’iyyar APC a jihar, kyautar Naira miliyan 22 domin gudanar da shagalin Sallah Karamar.
Yayin bayar da kyautar a ranar Alhamis, Bajare ya ce ya yi hakan ne domin nuna godiyarsa ga jagoran APC a jihar, Sanata Aliyu Magatakarda Wamakko, da Gwamna Ahmad Aliyu, bisa damar da suka ba shi don ba da gudunmawarsa ga ci gaban jihar.
“Wannan tallafi saƙon godiya ne daga shugabanninmu zuwa gare ku. Idan ba su ba mu dama ba, ba za mu iya wannan ba.
“Kuma muna shirye mu ƙara tallafawa a duk lokacin da buƙata hakan ta taso,” in ji shi.
Ya jinjina wa al’ummar Ƙaramar Hukumar Sakkwato ta Arewa, bisa sadaukarwar da suka yi wajen ganin jam’iyyar APC ta yi nasara, inda ya ce hakan ne ya sa suka cancantar a yi masu hidima.
Bajare, ya tabbatar da cewa zai ci gaba da tallafa wa magoya bayan jam’iyyar lokaci zuwa lokaci domin tabbatar da ci gaban tafiyar siyasarsu.
Dangane da tsarin rabon tallafin, ya ce kowane mutum da aka zaɓa zai amfana da kuɗi tsakanin Naira 100,000 zuwa miliyan ɗaya, ya danganta da matsayinsa.
Haka kuma ya yi fatan al’umma za su gudanar da shagalin sallah cikin lumana da kwanciyar hankali.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Kyautar Kuɗi Magoya Baya Sakkwato
এছাড়াও পড়ুন:
Mun yi asarar shanu 340 a hannun ɓarayi a Yuli — Miyetti Allah
Kungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah ta Nijeriya reshen Jihar Benuwe, a ranar Alhamis, ta bayyana cewa aƙalla shanu 340 na mambobinta ne aka sace a cikin watan Yuli na 2025.
Hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da sakataren ƙungiyar na jiha, Ibrahim Galma ya fitar kuma aka rabawa manema labarai a Makurdi.
Tinubu ya tsawaita wa’adin aikin shugaban hukumar Kwastam Mutum 9 sun rasu a hatsarin kwale-kwale a JigawaA cewar sanarwar, lamarin ya faru ne a garin Agatu da wasu sassan Ƙaramar hukumar Guma da ke Jihar Benuwe.
Galma ya kuma yi zargin cewa, ɓarayin shanu da ke afkawa jama’a a Ƙaramar hukumar Agatu sun faɗaɗa hare-harensu zuwa sassan Jihar Kogi.
“A ranar 19 ga Yuli, 2025 wasu da ake zargin ’yan ƙabilar unguwar Eguma ne a ƙaramar hukumar Agatu sun sace shanu 73 na wani Sale Abubakar (makiyayi Fulani), kuma har ya zuwa yanzu ba a ƙwato shanun ba.
“A ranar 21/7/2025 wani gungun masu aikata laifuka daga unguwar Agatu sun yi awon gaba da shanu 80 na Ardo Sarkin Fulanin Bagana, an yi awon gaba da shanun ne a Jihar Kogi, kusa da kan iyaka da ƙaramar hukumar Agatu ta Jihar Benuwe.
Ɓarayin sun kwashe shanun zuwa ƙauyukan Agatu. Daga baya kuma, an ƙwato shanu 30 daga cikin 80 a Agatu, inda ba a iya gano 50 ba.
“A ranar 24 ga Yuli, 2025 wasu miyagu matasa ‘yan garin Agatu sun yi awon gaba da wasu shanu 213 na Garah Mobaba, hakan kuma ya faru ne a kan iyaka tsakanin Jihar Kogi da Ƙaramar hukumar Agatu ta Jihar Benuwe, haka kuma lamarin na faruwa a wasu sassan Ƙaramar hukumar Guma ta Jihar Benuwe, inda aka samu rahotannin sace-sacen shanu da kuma kashe-kashen makiyaya.”
Shanun mallakin Sale Abubakar (makiyayin Fulani), kuma har ya zuwa yanzu, ba a ƙwato shanun da aka sace ba.