Sanƙarau ta kashe mutum 55 saboda rashin tsafta a Kebbi
Published: 20th, March 2025 GMT
Aƙalla mutum 55 ne suka rasu sakamakon ɓarkewar cutar sanƙarau a ƙananan hukumomin Jega, Gwandu, Aliero, Bunza, da Birnin Kebbi da ke Jihar Kebbi.
Hukumar Lafiya ta Jihar ta tabbatar da ɓullar cutar bayan gwaje-gwajen da aka yi a Abuja.
Ƙungiyoyin ƙwadago sun buƙaci Tinubu ya mayar da Fubara kan kujerarsa Shugaban Dattawan Arewa ya ajiye sarautar Magajin Rafin ZazzauSakataren Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kebbi, Dokta Nuhu Koko, ya bayyana cewa a Gwandu ne aka fi samun waɗana suka rasu, inda mutum 25 suka rasu, sai Jega da ke 16, sannan Aliero ke da mutum 14 da suka mutu.
Yawancin waɗanda suka rasu sun ɗauka cewa zazzaɓin cizon sauro ne ke damunsu, wanda hakan ya sa ba su garzaya asibiti ba da wuri.
“Ba mu san cewa sanƙarau ce ba. Mutane suna kamuwa da zazzaɓi mai tsanani da ciwon kai, sannan suna mutuwa ba zato ba tsammani,” in ji wani mazaunin Jega, Jafaru Abubakar.
“Wasu na fama da ciwon wuya, wasu kuma suna yin amai sosai kafin su rasu.”
An danganta yaɗuwar cutar da rashin tsafta da cunkoso, musamman a makarantu.
An tabbatar da mutuwar ɗalibai biyar a Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Aliero.
Sai dai duk da haka ba a rufe makarantar ba, amma an mayar da asibitin Jami’ar cibiyar killace marasa lafiya.
Dokta Koko, ya yi gargaɗi kan shan magani ba tare da izinin likita ba, da jinkirta zuwa asibiti, inda ya ce hakan na ƙara yawan mace-mace.
“Yawancin waɗanda suka rasu sun zo asibiti a makare, bayan cutar ta haddasa matsaloli masu tsanani,” in ji shi.
Gwamnatin jihar ta fitar da Naira miliyan 30 don ɗaukar matakan gaggawa, ciki har da raba magunguna, allurar rigakafi, da wayar da kan jama’a.
An shawarci al’umma da su gaggauta zuwa asibiti idan suka ga alamun cutar, su guji shiga cunkoso, tare da kula da tsaftar jiki da muhalli domin daƙile yaɗuwar cutar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: gwamnati Mutuwa Rashin lafiya Sanƙarau
এছাড়াও পড়ুন:
Hizbullah Ta Kasar Lebanon Ta Godewa JMI Dangane Da Tallafawa Kungiyar Saboda Gwagwarmaya Da HKI
Babban sakataren kungiyar Hezbullah ta kasar Lebanon Sheikh Na’em Qasim ya godewa shugabancin JMI, wato Imam Sayyif Aliyul Khaminaei kan goyon bayan da yake bawa kungiyar babu kakkautawa don yakar makiyar kasar HKI.
Shugaban kungiyar ya bayyana haka ne a lokacinda yake hira da tashar talabijin ta Al-Mayadeen ta kasar Lebanon, a karon farko tun bayan shahadr shugaban kungiyar Sayyid Hassan Nasarallah a shekarar da ta gabata.
Babban malamin ya kara da cewa, taimakon da Imam Khaminae yayiwa kungiyar Hizbullah, ya kai matsayinda ba zamu tambaya, ko roka ba. Musamman bayan fara yaki a cikin watan Octoban shekara ta 2023, kuma ta bada wadannan taimakon ba tare da ta shiga yakin kai tsaye ba.
Sheikh Qasem ya bayyana cewa, bamu bukaci JMI ta shiga yakin ba, kuma bai kamata ta shiga yakin ba, saboda muma bama bukatar da shiga yakin.
Daga karshen shugaban kungiyar ya bayyana cewa zancen da aka cika duniya da shin a cewa kungiyar ta mika makamanta ga gwamnatin kasar. Saboda takurawar da manya-manyan kasashen duniya suke yi don shi ne bukatar HKI.
Don haka yamata su san cewa bamu da Kalmar mika kai a kamusimmu, ko nasara ko shahada babu wata na uku iji shi.
Kuma wannan halin da ake ciki, na keta hurimun yarjeniyar 1701 wanda HKI take yi ba zai dore har’abada ba.