Aminiya:
2025-05-01@00:46:39 GMT

Sanƙarau ta kashe mutum 55 saboda rashin tsafta a Kebbi

Published: 20th, March 2025 GMT

Aƙalla mutum 55 ne suka rasu sakamakon ɓarkewar cutar sanƙarau a ƙananan hukumomin Jega, Gwandu, Aliero, Bunza, da Birnin Kebbi da ke Jihar Kebbi.

Hukumar Lafiya ta Jihar ta tabbatar da ɓullar cutar bayan gwaje-gwajen da aka yi a Abuja.

Ƙungiyoyin ƙwadago sun buƙaci Tinubu ya mayar da Fubara kan kujerarsa Shugaban Dattawan Arewa ya ajiye sarautar Magajin Rafin Zazzau

Sakataren Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kebbi, Dokta Nuhu Koko, ya bayyana cewa a Gwandu ne aka fi samun waɗana suka rasu, inda mutum 25 suka rasu, sai Jega da ke 16, sannan Aliero ke da mutum 14 da suka mutu.

Yawancin waɗanda suka rasu sun ɗauka cewa zazzaɓin cizon sauro ne ke damunsu, wanda hakan ya sa ba su garzaya asibiti ba da wuri.

“Ba mu san cewa sanƙarau ce ba. Mutane suna kamuwa da zazzaɓi mai tsanani da ciwon kai, sannan suna mutuwa ba zato ba tsammani,” in ji wani mazaunin Jega, Jafaru Abubakar.

“Wasu na fama da ciwon wuya, wasu kuma suna yin amai sosai kafin su rasu.”

An danganta yaɗuwar cutar da rashin tsafta da cunkoso, musamman a makarantu.

An tabbatar da mutuwar ɗalibai biyar a Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Aliero.

Sai dai duk da haka ba a rufe makarantar ba, amma an mayar da asibitin Jami’ar cibiyar killace marasa lafiya.

Dokta Koko, ya yi gargaɗi kan shan magani ba tare da izinin likita ba, da jinkirta zuwa asibiti, inda ya ce hakan na ƙara yawan mace-mace.

“Yawancin waɗanda suka rasu sun zo asibiti a makare, bayan cutar ta haddasa matsaloli masu tsanani,” in ji shi.

Gwamnatin jihar ta fitar da Naira miliyan 30 don ɗaukar matakan gaggawa, ciki har da raba magunguna, allurar rigakafi, da wayar da kan jama’a.

An shawarci al’umma da su gaggauta zuwa asibiti idan suka ga alamun cutar, su guji shiga cunkoso, tare da kula da tsaftar jiki da muhalli domin daƙile yaɗuwar cutar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: gwamnati Mutuwa Rashin lafiya Sanƙarau

এছাড়াও পড়ুন:

Hajjin 2025: An Fara Yi Wa Maniyyata Allurar Rigakafi A Jigawa

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ƙaddamar da shirin rigakafin mahajjata na shekarar 2025 a yankin Hadejia da ke shiyyar arewa maso gabas ta jihar.

Shugaban hukumar, Alhaji Ahmed Umar Labbo, ne ya bayyana hakan ga manema labarai a Hadejia.

Alhaji Ahmed Umar Labbo ya jaddada kudirin hukumar na ba da fifiko ga lafiya da kuma tsaron mahajjatan jihar.

Ya ce, kare lafiyar mahajjatan jihar  nauyi ne da ya rataya a wuyan  hukumar.

“Shirin rigakafin da muka fara yana nuna shirinmu na tabbatar da nasarar aikin Hajjin shekarar 2025. Ina ƙarfafa mahajjata su ba da haɗin kai tare da bin ƙa’idojin lafiya yayin wannan tafiya mai albarka.”

“Ina kuma ƙarfafa ku da ku zama masu bin doka da haƙuri yayin aikin Hajji. Da fatan za ku halarci dukkan tarukan bita da kai da aka shirya, domin muhimmanci su Alhazai” In ji shi.

Labbo, wanda ya sa ido a kan shirin rigakafin tare da bai wa wani mahajjaci daga Hadejia allurar farko, ya bayyana cewa aikin rigakafin zai ci gaba har zuwa lokacin tafiyar su zuwa ƙasa mai tsarki.

Haka kuma, Shugaban cibiyar lafiya a matakin farko, Dr. Bala Ismaila, ya bayyana muhimmancin allurar rigakafin da ake bayarwa, wanda ya haɗa da rigakafin cutar sankarau, cutar shan inna, da kuma cutar zazzabin cizon sauro (yellow fever).

Ya kuma yi bayani kan yiwuwar fuskantar rashin lafiya bayan rigakafin, inda ya shawarci mahajjata da su nemi kulawar likita cikin gaggawa idan suka fuskanci hakan ko wata matsala da ta wuce kima.

Wakilinmu ya ruwaito cewa, ana gudanar da aikin rigakafin a dukkan kananan hukumomi 27 na jihar.

 

Usman Muhammad Zaria 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ISWAP ta ɗauki alhakin kashe mutum 26 a Borno
  • An kashe mafarauta 10 a Adamawa
  • Wani abin fashewa ya kashe mutum 26 a Borno
  • Za a rataye wani soja saboda laifin kashe budurwarsa
  • Shugaban Majalisar Ƙoli ta Shari’ar Musulunci a Najeriya ya rasu
  • Bom ɗin Boko Haram ya kashe mutane 26 a Borno
  • Jihar Kebbi Ta Kammala Shirye-shiryen Aikin Hajjin 2025
  • Hajjin 2025: An Fara Yi Wa Maniyyata Allurar Rigakafi A Jigawa
  • Jiragen Yakin Amurka Sun Kashe Mutane Da Dama A lardin Sa’ada Na Kasar Yemen
  • Dukan farar hula saboda sanya kayan sojoji kuskure ne — Janar Chibuisi