Aminiya:
2025-11-18@20:22:21 GMT

Sanƙarau ta kashe mutum 55 saboda rashin tsafta a Kebbi

Published: 20th, March 2025 GMT

Aƙalla mutum 55 ne suka rasu sakamakon ɓarkewar cutar sanƙarau a ƙananan hukumomin Jega, Gwandu, Aliero, Bunza, da Birnin Kebbi da ke Jihar Kebbi.

Hukumar Lafiya ta Jihar ta tabbatar da ɓullar cutar bayan gwaje-gwajen da aka yi a Abuja.

Ƙungiyoyin ƙwadago sun buƙaci Tinubu ya mayar da Fubara kan kujerarsa Shugaban Dattawan Arewa ya ajiye sarautar Magajin Rafin Zazzau

Sakataren Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kebbi, Dokta Nuhu Koko, ya bayyana cewa a Gwandu ne aka fi samun waɗana suka rasu, inda mutum 25 suka rasu, sai Jega da ke 16, sannan Aliero ke da mutum 14 da suka mutu.

Yawancin waɗanda suka rasu sun ɗauka cewa zazzaɓin cizon sauro ne ke damunsu, wanda hakan ya sa ba su garzaya asibiti ba da wuri.

“Ba mu san cewa sanƙarau ce ba. Mutane suna kamuwa da zazzaɓi mai tsanani da ciwon kai, sannan suna mutuwa ba zato ba tsammani,” in ji wani mazaunin Jega, Jafaru Abubakar.

“Wasu na fama da ciwon wuya, wasu kuma suna yin amai sosai kafin su rasu.”

An danganta yaɗuwar cutar da rashin tsafta da cunkoso, musamman a makarantu.

An tabbatar da mutuwar ɗalibai biyar a Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Aliero.

Sai dai duk da haka ba a rufe makarantar ba, amma an mayar da asibitin Jami’ar cibiyar killace marasa lafiya.

Dokta Koko, ya yi gargaɗi kan shan magani ba tare da izinin likita ba, da jinkirta zuwa asibiti, inda ya ce hakan na ƙara yawan mace-mace.

“Yawancin waɗanda suka rasu sun zo asibiti a makare, bayan cutar ta haddasa matsaloli masu tsanani,” in ji shi.

Gwamnatin jihar ta fitar da Naira miliyan 30 don ɗaukar matakan gaggawa, ciki har da raba magunguna, allurar rigakafi, da wayar da kan jama’a.

An shawarci al’umma da su gaggauta zuwa asibiti idan suka ga alamun cutar, su guji shiga cunkoso, tare da kula da tsaftar jiki da muhalli domin daƙile yaɗuwar cutar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: gwamnati Mutuwa Rashin lafiya Sanƙarau

এছাড়াও পড়ুন:

GGCSS Maga: Halin da iyaye ke ciki bayan sace ’ya’yansu

Iyayen ɗalibai ’yan mata 25 ’yan bindiga sace ɗakunan kwanansu a Jihar Kebbi sun bayyana irin tashin hankali da suka shiga bayan abin da ya faru.

“Ita kaɗai gare ni,” in ji Malam Muhammad Maga, mahaifin Nafisa, wadda ita kadai ya haifa, kuma take cikin ɗaliban da ’yan bindiga suka sace a makarantar.

Malam Muhammad wanda idanunsa ke cike da ƙwalla ya ce, “Roƙona Allah Ya sa a dawo min da ita lafiya, ita kaɗai gare ni. Ina roƙon Gwamna Idris ya taimaka a dawo mana da su.  Mun san ƙoƙarin da yake yi a fannin tsaro a tsawon shekara biyu da ya yi a kan mulki.”

Shi ma Malam Aliyu Yakubu, ɗaya daga cikin iyayen ɗaliban da aka sace, ya ce, “’Yata na cikin ɗaliban da aka sace daga ɗakin kwanansu a safiyar Litinin, gaskiya ni da sauran iyaye muna cikin tashin hankali.

Za mu ceto ’Yan Matan GGCSS Maga cikin ƙoshin lafiya — Gwamnan Kebbi Sace Ɗalibai: Gwamnatin Tinubu ba ta shirya kawo ƙarshen ta’addancin ’yan bindiga ba — Amnesty Mayaƙan ISWAP sun kashe kwamandan soji a Borno

“Babban abin da nake tsoro shi ne kada abin ya zama irin na Makarantar ’Yan Mata ta Gwamantin Tarayya ta Birnin Yauri, inda yaran da aka sace suka shafe sama da shekara biyu a hannun ’yan bindiga

Muna rokon Gwamnatin Jihar Kebbi da Gwamnatin Tarayya su yi duk mai yiwuwa su ceto mana ’ya’yan mu”

Aminiya ta ruwaito cewar da asubahin ranar Litinin ne ’yan bindiga suka yi ta harbe-harbe a iska sa’annan suka kutsa cikin Makarantar sakandaren ’Yan Matan Gwamnati ta Musamman (GGCSS) da ke garin Maga a Ƙaramar Hukumar Danko Wasagu a Jihar Kebbi, suka yi abin gaba da ɗalibai 25.

’Yan bindigar sun ci karensu babu babbaka, ba tare da wani ƙalubale ba, in banda Mataimakin Shugaban Makarantar, Malam Hassan Yakubu Makuku, wanda ya yi ƙoƙarin hana su tafiya da ɗaliban, amma suka harba shi har lahira, suka yi abin gaba da yaran.

Makarantar GGCSS Maga ta kasance a rufe na kimanin shekaru biyar saboda tsaron irin garin GGSS Birnin Tauri a zamanin gwamnatin da ta gabata ta Abubakar Atiku Bagusu, sai ’yan shekarun baya aka buɗe ta, inda aka girke jami’an tsaro.

Wani mahaifi da ’yarsa A’isha take cikin ɗaliban da aka sace, ya ce, wani mazaunin garin ne ya fara sanar da shi cewa A’isha tana cikin yaran da aka sace,  “Amma ban gaskata ba, sai da na zo makarantar na iske iyaye na ta koke-koke. Roƙona ga gwamnati shi ne ta taimaka ta ceto maka ’ya’yanmu.”

Kawai Altine, wanda shi ma ’yan bindiga sun sace ’yarsam ya ce, “Na miƙa komai ga Allah, kuma na yi imanin cewa Allah Zai dawo mana da ita nan ba da jimawa ba. Roƙona kawo shi ne gwamnati da jami’an tsaro kada su yi ƙasa a gwiwa, wajen bi sawu domin gano yaran namu.”

Wani shugaban al’umma a yankin, Malam Rabi’u Abubakar, ya ce harin ya girgiz al’ummar yankin, musamman iyayen ɗalibai.

Ya ce, “Muna da dalilin yin baƙin ciki, saboda sun tafi mana da ’ya’ya, kuma suka kashe mana Malam Yakubu Makuku, saboda ya nemi kada su ɗauki yaran. Haƙiƙa wannan babban rashi ne.”

Kakakin Gwamnan Jihar Kebbi, Abdullahi Idris Zuru, ya shaida wa Aminiya cewa an turo ƙarin jami’an tsaro daga Abuja zuwa jihar domin su taimaka a aikin da ake yi na nema da kuma ceto ɗaliban.

Tun da farko Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kebbi ta tabbatar da harin, tare da sanar da cewa tuni jami’an tsaro da mafarauta suka fara aikin ceto ɗaliban.

Aminiya ta ruwaito cewa Gwamna Jihar Kebbi, wanda labarin harin ya sa shi gaggawar yanke ziyarar aiki da ya kai Abuja, ya yi wata ganawa da iyayen ɗaliban, inda ya ba su tabbacin yin duk mai yiwuwa tare da jami’an tsaro domin kuɓutar da yaran.

Karo na biyu ke nan da ’yan bindiga suka kutsa cikin makarantar kwana ta ’yan a Jihar Kebbi suka yi garkuwa da gomman dalibai — na farko shi ne a Makarantar ’Yan Mata ta Gwamantin Tarayya da ke Birnin Yauri.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnan Taraba ya dakatar da ficewa daga PDP saboda sace ɗalibai a Kebbi
  • Dole ku ceto daliban da aka sace a Kebbi Shugaban Sojoji
  • GGCSS Maga: Halin da iyaye ke ciki bayan sace ’ya’yansu
  • Za mu ceto ’Yan Matan GGCSS Maga cikin ƙoshin lafiya — Gwamnan Kebbi
  • Mayaƙan ISWAP sun kashe kwamandan soji a Borno
  • Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi
  • Masu ibadar Umara 42 sun mutu a hatsarin mota a hanyar zuwa Makka
  • Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 3 sun sace 64 a Zamfara
  • Ɗan Najeriya ya kashe mahaifinsa, ya yanki ƙannensa da wuƙa a Amurka