Sanƙarau ta kashe mutum 55 saboda rashin tsafta a Kebbi
Published: 20th, March 2025 GMT
Aƙalla mutum 55 ne suka rasu sakamakon ɓarkewar cutar sanƙarau a ƙananan hukumomin Jega, Gwandu, Aliero, Bunza, da Birnin Kebbi da ke Jihar Kebbi.
Hukumar Lafiya ta Jihar ta tabbatar da ɓullar cutar bayan gwaje-gwajen da aka yi a Abuja.
Ƙungiyoyin ƙwadago sun buƙaci Tinubu ya mayar da Fubara kan kujerarsa Shugaban Dattawan Arewa ya ajiye sarautar Magajin Rafin ZazzauSakataren Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kebbi, Dokta Nuhu Koko, ya bayyana cewa a Gwandu ne aka fi samun waɗana suka rasu, inda mutum 25 suka rasu, sai Jega da ke 16, sannan Aliero ke da mutum 14 da suka mutu.
Yawancin waɗanda suka rasu sun ɗauka cewa zazzaɓin cizon sauro ne ke damunsu, wanda hakan ya sa ba su garzaya asibiti ba da wuri.
“Ba mu san cewa sanƙarau ce ba. Mutane suna kamuwa da zazzaɓi mai tsanani da ciwon kai, sannan suna mutuwa ba zato ba tsammani,” in ji wani mazaunin Jega, Jafaru Abubakar.
“Wasu na fama da ciwon wuya, wasu kuma suna yin amai sosai kafin su rasu.”
An danganta yaɗuwar cutar da rashin tsafta da cunkoso, musamman a makarantu.
An tabbatar da mutuwar ɗalibai biyar a Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Aliero.
Sai dai duk da haka ba a rufe makarantar ba, amma an mayar da asibitin Jami’ar cibiyar killace marasa lafiya.
Dokta Koko, ya yi gargaɗi kan shan magani ba tare da izinin likita ba, da jinkirta zuwa asibiti, inda ya ce hakan na ƙara yawan mace-mace.
“Yawancin waɗanda suka rasu sun zo asibiti a makare, bayan cutar ta haddasa matsaloli masu tsanani,” in ji shi.
Gwamnatin jihar ta fitar da Naira miliyan 30 don ɗaukar matakan gaggawa, ciki har da raba magunguna, allurar rigakafi, da wayar da kan jama’a.
An shawarci al’umma da su gaggauta zuwa asibiti idan suka ga alamun cutar, su guji shiga cunkoso, tare da kula da tsaftar jiki da muhalli domin daƙile yaɗuwar cutar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: gwamnati Mutuwa Rashin lafiya Sanƙarau
এছাড়াও পড়ুন:
Sudan: Makaman ‘Drones’ Sun Kashe Ma’aikatan MDD 6 A Kadugli Na Kurdufan Ta Kudu
Jami’an tsaro na MDD wadanda suke aiki a rundunar (UNISFA) guda 6 ne suka rasa rayukansu a jiya Asabar a wani harin da aka kaiwa sansaninsu a lardin Kurdufan da kudu a kasar Sudan.
Shafin yanar gizo na Labarai ‘Sudan Tribune’ ya nakalto gwamnatin kasar Sudan tana aza laifin kai hare-haren kan kungiyar RSF ta yan tawaye a yankin. Amma RSF ta musanta zargin.
Dakarun MDD ta (UNISFA) dai suna tabbatar da zaman lafiya a yankin Abiea da sudan da kuma sudan ta kudu suke takaddama a kansu ne tun shekara ta 2011. Kuma wannan shi ne hari na farko kai tsaye kan dakarun MDD a yankin tun lokacinda aka fara yakin basabsa a kasar ta Sudan fiye da shekaru 2 da suka gabata. Wato tun wata Afrilun shekara ta 2023.
Labarin ya kara da cewa makaman Drones, watojiragen yakin da ake sarrafasu daga nesa guda uku ne suka kai hare-hare kan sansanin sojojin na MDD inda suka kashe mutane 6 daga kasar Bangladesh suka kuma lalata wata tashar ajiyar makamashi.
Labarin ya kara da cewa mutane biyu daga cikin wadanda suka ji rauni suna cikin mummunan hali. Ya zuwa yanzu dai Majalisar bata zargi wani bangare da kai hare-haren ba. Mazauna garin Kadugli inda aka kai harin, sun bayyana cewa mayakan kungiyar SPLM-N karkashin Abdulaziz Al-Hilu sun yi barin wuta a kan garin a jiya Asabar. Bayan yiwa garin kawanyana na watanni.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Eritrea Ta Fice Daga Kungiyar Raya Kasahsen Gabacin Afrika (IGAD) December 14, 2025 َA Yau Ne Za’a Gudanar Da Taron Koli Na Kungiyar ECOWAS A Birnin Abuja December 14, 2025 Iran Ta karbi Bakunci Taron Kasashen Dake Makwabtaka Da Afghanistan Da Rasha December 14, 2025 Isra’ilaTa Kashe Wani Bafalasdine Matashi A Wani Hari Da Takai A Arewacin Kogin Jodan. December 14, 2025 Shuwagabannin Majalisar Kasar Iran Da Na Ethiopia Sun Gudanar Da Taron Manema Labarai December 14, 2025 Ghana Ta Kori Wasu Yahudawa Guda 3 Don Mayar Da Martani December 14, 2025 Araghchi ya bukaci Amurka ta girmama al’ummar Iran da gwamnatinta December 14, 2025 Dan bindiga ya kashe sojojin Amurka biyu da wani farar hula a Siriya December 14, 2025 Mutum biyu sun mutu a harbin bindiga a Jami’ar Brown ta Amurka December 14, 2025 Shugabannin kasashen (ECOWAS) na taro a Abuja December 14, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci