Aminiya:
2025-06-15@19:43:15 GMT

Abba ya rantsar da sabon Kwamishinan Gidaje na Kano

Published: 17th, March 2025 GMT

Gwamna Abba Kabir Yusuf a wannan Litinin ɗin ya rantsar da sabon Kwamishinan Ma’aikatar Tsarawa da Bunƙasa Gidaje ta Kano, Ibrahim Yakubu Adamu.

Wannan dai shi ne karo na huɗu cikin ƙasa da shekaru biyu ke nan da gwamnan yake faɗaɗa majalisar zartarwa jihar ta Kano.

Ana zargin wa da ƙani da yi wa almajiri yankan rago a Adamawa Majalisar Ribas ta soma shirye-shiryen tsige Gwamna Fubara

Aminiya ta ruwaito cewa gabanin wannan sabon naɗin, Ibrahim Yakubu Adamu shi ne Shugaban Hukumar Tsara Birane ta Kano KNUPDA.

Antoni Janar kuma Kwamishinan Shari’a na Kano, Haruna Isah Dederi ne ya jagoranci rantsar da sabon Kwamishinan da aka gudanar a fadar Gwamnatin Kano.

Da yake jawabi, Gwamnan ya yaba wa sabon kwamishinan wanda ya ba da shaida kan ƙwazo da kuma ƙwarewa haɗi da gudunmawar da ya bayar wajen ci gaban birnin na Dabo.

Gwamnan ya buga misali da yadda sabon kwamishinan ya jagoranci aikin tsarawa da kuma bunƙasa rukunin gidajen nan na Kwankwasiyya da Amana da Bandirawo waɗanda aka gina a tsakanin shekarar 2013 zuwa 2015 a zamanin gwamnatin Sanata Rabiu Musa Kwankwaso.

Sabon kwamshinan wanda ƙwararren mai zana gine-gine ne, Gwamnan ya hikaito yadda ya taka rawar gani wajen tsarawa da kuma aiwatar da wasu muhimman ayyukan gine-gine a lokacin da yake Kwamishinan Ayyuka da Gidaje a tsakanin shekarar 2011 zuwa 2015.

A wani labarin mai nasaba da wannan, Gwamnan ya umarci duk waɗanda suka mallaki gida a rukunin gidaje na Kwankwasiyya ko Amana ko Bandirawo da su tabbatar sun tare nan da watanni uku ko kuma su sanya ’yan haya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ibrahim Yakubu Adamu Kwamishinan Bunƙasa Gidaje da sabon Kwamishinan

এছাড়াও পড়ুন:

Na’im Kassim: Harin HKI Akan Iran Ba Abinda Zai Jawo Mata Sai Kaskanci

Babban sakataren kungiyar Hizbullah ta Lebanon Sheikh Na’im Kassim ya yi Allawadai da harin da HKI ta kai wa Iran, wanda ya bayyana shi da cewa; Yana da hatsarin gaske, kuma ‘yan sahayoniyar sun yi hakan ne bisa cikakken goyon bayan Amurka.

Sheikh Na’im Kassim ya kuma bayyana cewa; Harin na ‘yan sahayoniya ba shi da wani dalili da ya wuce a rufe bakin gaskiya wanda yake taimakawa al’ummar Falasdinu a Gaza da ake yi wa kisan kiyashi, haka nan kuma taimakawa da goyon bayan gwgawarmayar Lebanon da dukkanin wannan yankin.

Babban magatakardar kungiyar ta Hizbullah ya kuma kara da cewa; Wannan harin da wuce gona da irin za iyi tasiri mai girma a cikin wannan yankin, sannan ya kara da cewa: Wannan harin ba zai wuce ba tare da fuskantar martani daga jamhuriyar musulunci ta Iran.

Haka nan kuma Na’im Kassim ya kara da cewa; Isra’ilawa makiya tare da Amurka ba za su taba yin tasiri akan hanyar da Iran ta zabarwa kanta ba ta gwgawarmaya ko kuma rawar da take takawa a cikin wannan yankin.

Babban magatakardar kungiyar ta Hizbullah ya ce; Hizbullah da magoya bayanta, suna ci gaba da riko da tafarkin gwagwarmaya da kuma goyon bayan jamhuriyar musulunci ta Iran wajen kare hakkokinta.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Masu ƙwacen waya sun kashe ma’aikacin Jami’ar Northwest a Kano
  • Dakarun Kare Juyin Juya Halin Musulunci Na Iran Sun Bayyana Sabon Salon Mayar Da Martani Kan Isra’ila
  • Iran ta sake kai hare-haren martani kan Isra’ila
  • Miliyoyin Mutane Sun Gudanar  Da Bukukuwan “Idin Gadir” A Tehran Da Sauran Garuruwan Iran
  • Gwamnan Kaduna ya bai wa sabon Sarkin Moro’a sandar mulki
  • Mahara sun kashe mutum 26 a sabon hari a Binuwai
  • Na’im Kassim: Harin HKI Akan Iran Ba Abinda Zai Jawo Mata Sai Kaskanci
  • Ambaliya: Gwamnatin Kano ta fara tsaftace magudanan ruwa
  • Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6
  • Gwamnan Gombe Ya Yi Allah Wadai Da Kisan Da ‘Yan Daba Suka Yi Wa Amadi Kasiran