Gwamna Malam Umar Namadi ya kaddamar da rukuni na farko na jami’an tsaro karkashin shirin Safe Schools Initiative na Jihar Jigawa.

Taron, wanda kuma ya kasance  bikin kammala horo ga masu tsaron, an gudanar da shi ne a sansanin horas da matasa masu yi wa ƙasa hidima (NYSC) da ke Panisau, a Dutse.

Wannan shiri, wanda shi ne irin sa na farko a ƙasar, an kirkireshi ne domin kare makarantu, da asibitoci, da  kotuna, da wuraren samar da ruwa a fadin jihar, inda aka dauki ma’aikata 9,974 don aiwatar da wannan aiki.

Za a tura Jami’an tsaron ne karkashin kamfanonin tsaro masu zaman kansu guda uku da aka rarraba zuwa mazabun yan majalisun dattawa.

Kamfanonin tsaron sun hada da Kare-Kallo a Jigawa ta Tsakiya, sai  JIMAD a Jigawa ta Arewa maso Yamma, da Corporate Security a  Jigawa ta Arewa maso Gabas.

Wadanda aka dauka sun fito daga sassan jihar daban-daban na jihar, kuma sun hada da masu shaidar karatu ta digiri, da NCE, da difloma, kuma za su yi aiki ne a yankunansu.

Da yake jawabi a wajen taron, Gwamna Namadi ya jaddada kudirin gwamnatinsa na kare kayayyakin more rayuwa da tabbatar da dorewar su.

“Wannan shiri an kirkireshi ne domin kare jarin da aka zuba a wadannan gine-gine na jama’a. Mun sha ganin yadda barayi ke lalata wadannan gine-gine, suna satar tagogi, kujeru, da sauran kayayyaki masu muhimmanci. A matsayina na shugaba mai kishin al’umma, mun dauki matakan dakile wannan matsala,” in ji shi.

Gwamnan ya kuma jaddada cewa wannan shiri ba wai tsaro kadai yake bayarwa ba, har da samar da ayyukan yi.

“Baya ga kare kadarorin gwamnati, wannan shiri kuma wata dama ce ta samar da aikin yi ga matasa. Kowane daya daga cikin mutum 9,974 da aka dauka daga yankunansu zai tabbatar da tsaron gine-ginen da ke yankinsa.”

Ya bukaci al’ummar yankunan da su baiwa jami’an tsaron hadin kai, yana mai cewa:

“A hakika, yakamata al’ummomi su rika kula da tsaron wadannan gine-gine da kansu, amma wannan shiri yana samar da tsari mai kyau na tsaro da ya dogara da al’ummar da ke yankunan.”

 

Da yake yi wa sabbin jami’an tsaron jawabi, ya bukace su da su yi aiki da gaskiya da rikon amana, yana mai tabbatar da cewa gwamnati na da shirin inganta jin dadinsu.

“Kayan da kuke sawa alamar iko ne don kare al’umma, ba don tsoratar da su ba. Gwamnati ta ware sama da Naira biliyan 3.4 duk shekara domin aiwatar da wannan shiri, abin da ke nuna muhimmancinsa ga jihar.”

Ya bukaci kamfanonin tsaro da ke kula da jami’an da su kula da jin dadinsu, kuma ya roki shugabannin kananan hukumomi da su bada hadin kai don tabbatar da nasarar shirin.

“Muna da yarjejeniya kan albashi mai kyau da adalci ga jami’an tsaro. Muna bukatar a kula da su yadda ya kamata, a biya su akan lokaci, sannan a basu kulawa da horo da ya dace domin tabbatar da ingancin tsaro.”

Gwamna Namadi ya bayyana shirin a matsayin wani bangare na karfafa matasa.

 

Usman Muhammad Zaria 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jami an Tsaro Makarantu Jigawa jami an tsaro wannan shiri tabbatar da

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Ta’adda A Dajin Taraba

Kwamandan rundunar ta 6, Birgediya Janar Kingsley Chidiebere Uwa, ya yabawa sojojin bisa nuna kwarewa da juriya, inda ya bukace su da su ci gaba da sharar daji har sai an kakkaɓe duk wasu masu aikata laifuka gaba daya a jihar Taraba.

 

Ya bayyana ci gaba da jajircewar rundunar sojin Nijeriya wajen tabbatar da tsaro da tsaron duk ‘yan kasa masu bin doka da oda, yana mai ba da tabbacin cewa, sojojin za su ci gaba da hada kai da sauran hukumomin tsaro da al’ummomin yankin domin samun dawwamammen zaman lafiya a jihar.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai Yajin Aikin: Ɗalibai Sun Bai Wa ASUU Da Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwana 7 Su Warware Rikicinsu October 15, 2025 Manyan Labarai 2027: Babu Ɗan Siyasar Da Zai Iya Ƙalubalantar Tinubu — Fadar Shugaban Ƙasa October 15, 2025 Labarai Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba Barazana Ce Ga Tsaro A Yammacin Afirka – Tinubu October 15, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Akwai Bukatar Al’umma Ta San Aikin Da Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFUND) Ya Yi  – Masari
  • Majalisar Dokokin Jihar Kaduna Za Ta Kafa Dokar Wuraren Tsaro A Makarantu
  • Batun Yin Afuwa Ga ‘Yan Yankin Ogoni Huɗu
  • ’Yan bindiga sun kashe jami’an tsaro 8 a harin kwanton ɓauna a Zamfara
  • Gwamna Lawal Ya Yi Alhinin Kisan Jami’an Tsaro A Zamfara
  • ’Yan sanda sun kama gungun masu fashi a kan hanyar Katsina zuwa Kano
  • Baba-Ahmed Ya Zargi El-Rufai Da APC Kan Haifar Da Rashin Tsaro Don Neman Mulki
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Cire Darasin Lissafi Zai Taimakawa Dalibai Shiga Jami’a
  • Sojoji Sun Fatattaki ‘Yan Ta’adda A Dajin Taraba
  • Dakta Umar Kabir Yusuf-Bakatsinen da ya kirkiro manhajar Masjid Suite da ke sada zumuncin hada masallaci da masallata