Gwamna Namadi Ya Kaddamar Da Rukuni Na Farko Na Masu Tsaron Makarantu
Published: 13th, March 2025 GMT
Gwamna Malam Umar Namadi ya kaddamar da rukuni na farko na jami’an tsaro karkashin shirin Safe Schools Initiative na Jihar Jigawa.
Taron, wanda kuma ya kasance bikin kammala horo ga masu tsaron, an gudanar da shi ne a sansanin horas da matasa masu yi wa ƙasa hidima (NYSC) da ke Panisau, a Dutse.
Wannan shiri, wanda shi ne irin sa na farko a ƙasar, an kirkireshi ne domin kare makarantu, da asibitoci, da kotuna, da wuraren samar da ruwa a fadin jihar, inda aka dauki ma’aikata 9,974 don aiwatar da wannan aiki.
Za a tura Jami’an tsaron ne karkashin kamfanonin tsaro masu zaman kansu guda uku da aka rarraba zuwa mazabun yan majalisun dattawa.
Kamfanonin tsaron sun hada da Kare-Kallo a Jigawa ta Tsakiya, sai JIMAD a Jigawa ta Arewa maso Yamma, da Corporate Security a Jigawa ta Arewa maso Gabas.
Wadanda aka dauka sun fito daga sassan jihar daban-daban na jihar, kuma sun hada da masu shaidar karatu ta digiri, da NCE, da difloma, kuma za su yi aiki ne a yankunansu.
Da yake jawabi a wajen taron, Gwamna Namadi ya jaddada kudirin gwamnatinsa na kare kayayyakin more rayuwa da tabbatar da dorewar su.
“Wannan shiri an kirkireshi ne domin kare jarin da aka zuba a wadannan gine-gine na jama’a. Mun sha ganin yadda barayi ke lalata wadannan gine-gine, suna satar tagogi, kujeru, da sauran kayayyaki masu muhimmanci. A matsayina na shugaba mai kishin al’umma, mun dauki matakan dakile wannan matsala,” in ji shi.
Gwamnan ya kuma jaddada cewa wannan shiri ba wai tsaro kadai yake bayarwa ba, har da samar da ayyukan yi.
“Baya ga kare kadarorin gwamnati, wannan shiri kuma wata dama ce ta samar da aikin yi ga matasa. Kowane daya daga cikin mutum 9,974 da aka dauka daga yankunansu zai tabbatar da tsaron gine-ginen da ke yankinsa.”
Ya bukaci al’ummar yankunan da su baiwa jami’an tsaron hadin kai, yana mai cewa:
“A hakika, yakamata al’ummomi su rika kula da tsaron wadannan gine-gine da kansu, amma wannan shiri yana samar da tsari mai kyau na tsaro da ya dogara da al’ummar da ke yankunan.”
Da yake yi wa sabbin jami’an tsaron jawabi, ya bukace su da su yi aiki da gaskiya da rikon amana, yana mai tabbatar da cewa gwamnati na da shirin inganta jin dadinsu.
“Kayan da kuke sawa alamar iko ne don kare al’umma, ba don tsoratar da su ba. Gwamnati ta ware sama da Naira biliyan 3.4 duk shekara domin aiwatar da wannan shiri, abin da ke nuna muhimmancinsa ga jihar.”
Ya bukaci kamfanonin tsaro da ke kula da jami’an da su kula da jin dadinsu, kuma ya roki shugabannin kananan hukumomi da su bada hadin kai don tabbatar da nasarar shirin.
“Muna da yarjejeniya kan albashi mai kyau da adalci ga jami’an tsaro. Muna bukatar a kula da su yadda ya kamata, a biya su akan lokaci, sannan a basu kulawa da horo da ya dace domin tabbatar da ingancin tsaro.”
Gwamna Namadi ya bayyana shirin a matsayin wani bangare na karfafa matasa.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jami an Tsaro Makarantu Jigawa jami an tsaro wannan shiri tabbatar da
এছাড়াও পড়ুন:
Iran, ta yi wa Isra’ila ruwan makamai masu linzami
Iran ta kaddamar da wasu jerin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila a matsayin maida martani kan haren haren da Isra’ila ta kai wa kasar a cikin daren ranar Juma’a.
Bayanai sun ce hare-haren na Iran sun lalata gine-gine da dama da jikkata mutane yayin da wasu rahotannin ke cewa an samu hasarar rayuka na akalla mutum biyu.
A cewar rahotannin kafofin yada labaran Isra’ila daban-daban, makamai masu linzami na iran sun fada a yankunan Tel Aviv, Haifa, Beersheba da wasu wurare.
An bayar da rahoton barna mafi muni a birnin Tel Aviv, inda akalla makami mai linzami guda ya afkawa wani bene mai hawa 50, lamarin da ya janyo fashewar wani abu mai karfi wanda ya sa hayaki ya tashi a sararin samaniyar birnin.
A cewar darektan cibiyar nazarin dabarun da huldar kasa da kasa, Amir Al-Mousawi, daya daga cikin makami mai linzamin na Iran ya afkawa wata cibiyar binciken nukiliya da ke birnin Tel Aviv.
Wasu rahotanni sun ce an kuma yi nasarar kaiwa ma’aikatar harkokin sojan Isra’ila hari.
Gwamnatin kasar ta sanya takunkumi, inda ta umarci mazauna yankin da kada su buga hotuna ko bidiyo na wuraren da makami mai linzami na Iran ya kai hari, kamar yadda kafar yada labaran Isra’ila ta bayyana.
Birgediya Janar Ahmad Vahidi, da yake magana da gidan talabijin na iran, ya ce martanin na iran mai lakabin Operation True Promise III “zai ci gaba muddin akwai bukatar hakan,” yayin da ya sha alwashin daukar fansar jinin shahidai.
Tun da farko, Vahidi ya ce an kai hari a kalla wurare 150 a harin ramuwar gayya kan gwamnatin Isra’ila, ciki har da wasu sansanonin soji masu matukar muhimmanci.