Aikin Hako Man Fetur A Kasar Somaliya Ya Kusa Kammala
Published: 13th, March 2025 GMT
Ministan man fetur da ma’adanai na gwamnatin tarayyar kasar Somaliya Taha Shari Muhammad ya sanar da cewa, ya zuwa yanzu aikin da kamfanin kasar Turkiya yake yi na hako man fetur a kasar ya yi nisa, kuma da akwai yiyuwar nan da shekara ta 2026 kasar za ta fara fitar da man Fetur.
Taha Shari ya kuma kara da cewa; Ana gudanar da aikin hako man ne a yankunan “Marig” dake gundumar “Galgadun” da kuma yankin “Harar Tiri” dake gundumar Madga.
Ministan man fetur da kuma ma’adanan na kasar Somaliya ya ce; Idan an gama aiki a wadannan yankunan biyu, za’a nufi garin “ Hobiyo”, don ci gaba da hako wasu rijiyoyin man.
Bugu da kari ministan man fetur na kasar Somaliya ya ce;gwamanti ta na da kwararru wadanda suke yi nazari a kan harkar hakar danyen man fetur, wadanda zasu yi aiki a cikin wani yanayi da ake ciki. Wani kalubalen da minstan ya bijiro da shi, shi ne yadda jiragen kasashen waje suke shiga cikin iyakar ruwan kasar suna aikin neman danyen mai, ba tare da izinin gwamnati ba
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Somaliya
এছাড়াও পড়ুন:
Osimhen Ya Kammala Komawa Galatasaray
Tauraron dan wasan gaba na Super Eagles, Victor Osimhen, ya kammala komawarsa ƙungiyar Galatasaray ta ƙasar Turkiyya daga Napoli, a wata yarjejeniya ta dindindin da ta kai Yuro miliyan 75. Ƙungiyar Galatasaray ta sanar da kammala ɗaukar Osimhen a shafinta na yanar gizo a ranar Alhamis, inda ta bayyana cewa yarjejeniyar ta fara aiki daga nan take.
Ɗan wasan mai shekaru 26 ya rattaba hannu kan yarjejeniyar shekaru huɗu tare da zakarun na ƙasar Turkiyya, kuma za a biya shi Yuro miliyan 15 a kowace kakar wasa. Hakazalika, zai karɓi ƙarin Yuro miliyan 5 a matsayin hakkinsa na mallakar hoto, yayin da Napoli za ta sami kashi 10 cikin 100 na duk wani kudi da za a sayar da shi da shi nan gaba.
Napoli Ta Nada Antonio Conte A Matsayin Sabon Kocinta De Bruyne Ya Kammala Komawa Napoli Bayan Barin Man CityA cikin yarjejeniyar, an haramtawa Osimhen sake komawa wata ƙungiya daga Serie A ta Italiya na tsawon shekaru biyu masu zuwa. Yayin da yake jawabi bayan sanya hannu, Osimhen ya bayyana farin cikinsa da dawowa cikin ƙungiyar Galatasaray. “Ina godiya ga shugaban kulob ɗin da mataimakinsa bisa wannan dama. Ina alfahari da kasancewa a cikin wannan babban gida,” in ji shi.
Osimhen ya yi kyakkyawan aiki a kakar da ta gabata inda ya zura ƙwallaye 37 tare da taimakawa aka zura ƙwallo 8 a wasanni 41 da ya buga. Wannan sanarwar na zuwa ne daidai lokacin da ake ta rade-radin saɓani tsakaninsa da Napoli, wanda yanzu haka an rufe batun.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp