Iran Tace Wani Dan Sako Daga UAE Ne Zai Isar Da Sakon Trump Zuwa Tehran
Published: 12th, March 2025 GMT
Wani jami’an gwamnatin kasar UAE ne zai isar da sakon shugaban kasar Amurka Donal Trump zuwa Tehran.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Esma’il Baghani ya na fadar haka. Ya kuma kara da cewa a halin yanzu mai bawa shugaban kasa shawara na kasar UAE Anwar Gargash yana kan hanyarsa ta zuwa Tehran dauke da wasikar, don isar da ita ga jagoran juyin juya halin musulunci Imam Sayyid Aliyul Khaminaei.
Labarin ya kara da cewa Gargash zai hadu da ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi da farko bayan isarsa birnin Tehran.
Kafin haka dai Majid Takht-Ravanchi mataimakin ministan harkokin wajen kasar Iran kan al-amuran siyasa, wanda ya je kasar UEA don halattar taron kwamitin siyasa na kasashen biyu ya gana da Gargash inda suka tattauna batun wasikar.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Yadda Bunkasar Tattalin Arzikin Kasar Sin Ke Samar Da Karin Damammaki Ga Kasashe Masu Tasowa
Wani abun lura ma a nan shi ne yadda a matsayinta na kasa mai tasowa ta farko a tarihin duniya da ta cimma nasarar samun wadata cikin lumana, Sin ta samar da wata taswira mai inganci, wadda sauran kasashe masu tasowa za su iya bi domin raya kansu cikin lumana, kuma karkashin hakan ne take ta fitar da shawarwari na ingiza ci gaban duniya bi da bi, irinsu shawarar raya jagorancin duniya da kasar ta gabatar a baya bayan nan. Shawarar da masharhanta da yawa ke ganin na da ma’anar gaske, wajen ingiza adalci, da daidaito a tsarin cudanyar mabanbantan sassan duniya.
A gani na tun da har kasar Sin ta kai ga gina tsari mai gamsarwa na raya kai bisa salon musamman mafi dacewa da yanayinta, wanda kuma yake ta kara samun karbuwa tsakanin kasashen duniya, a halin yanzu, kasar na kan wani matsayi na rarraba kwarewarta tare da sauran abokan tafiya, musamman kasashe masu tasowa. Wanda hakan kyakkyawan misali ne da dukkanin wata kasa a duniyan nan za ta iya lura da shi, yayin da take kokarin bunkasa kanta gwargwadon yanayin da take ciki.
Tabbas, ci gaban kasar Sin mai ban mamaki ya nunawa duniya cewa, kowace kasa na iya samun ci gaba ba tare da murdiya, muzgunawa wasu sassa, ko nuna karfin iko na siyasa ko tattalin arziki ba, maimakon hakan kasar Sin ta nunawa duniya cewa abu ne mai yiwuwa, a samu ci gaba bisa hadin gwiwar cimma moriya tare, ta yadda za a gudu tare a kuma tsira tare.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA