Iran Tace Wani Dan Sako Daga UAE Ne Zai Isar Da Sakon Trump Zuwa Tehran
Published: 12th, March 2025 GMT
Wani jami’an gwamnatin kasar UAE ne zai isar da sakon shugaban kasar Amurka Donal Trump zuwa Tehran.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Esma’il Baghani ya na fadar haka. Ya kuma kara da cewa a halin yanzu mai bawa shugaban kasa shawara na kasar UAE Anwar Gargash yana kan hanyarsa ta zuwa Tehran dauke da wasikar, don isar da ita ga jagoran juyin juya halin musulunci Imam Sayyid Aliyul Khaminaei.
Labarin ya kara da cewa Gargash zai hadu da ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi da farko bayan isarsa birnin Tehran.
Kafin haka dai Majid Takht-Ravanchi mataimakin ministan harkokin wajen kasar Iran kan al-amuran siyasa, wanda ya je kasar UEA don halattar taron kwamitin siyasa na kasashen biyu ya gana da Gargash inda suka tattauna batun wasikar.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Kakakin majalisar dokokin Ribas da takwarorinsa 16 sun fice daga PDP zuwa APC
Kakakin Majalisar Dokokin jihar Ribas, Martin Amaewhule tare da mambobin majalisar su 15 sun sanar da sauya sheka daga jam’iyyar PDP zuwa APC.
Amaewhule ya bayyana shawarar ’yan majalisar ne a zaman majalisa na ranar Juma’a, inda ya ce akwai abin da ya kira “rarrabuwar kai a fili” a cikin PDP wanda ya sa suka yanke wannan shawara.
Muna tafe da karin bayanai…