Iran Tace Wani Dan Sako Daga UAE Ne Zai Isar Da Sakon Trump Zuwa Tehran
Published: 12th, March 2025 GMT
Wani jami’an gwamnatin kasar UAE ne zai isar da sakon shugaban kasar Amurka Donal Trump zuwa Tehran.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Esma’il Baghani ya na fadar haka. Ya kuma kara da cewa a halin yanzu mai bawa shugaban kasa shawara na kasar UAE Anwar Gargash yana kan hanyarsa ta zuwa Tehran dauke da wasikar, don isar da ita ga jagoran juyin juya halin musulunci Imam Sayyid Aliyul Khaminaei.
Labarin ya kara da cewa Gargash zai hadu da ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi da farko bayan isarsa birnin Tehran.
Kafin haka dai Majid Takht-Ravanchi mataimakin ministan harkokin wajen kasar Iran kan al-amuran siyasa, wanda ya je kasar UEA don halattar taron kwamitin siyasa na kasashen biyu ya gana da Gargash inda suka tattauna batun wasikar.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Bankin Duniya Ya Daga Hasashen Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na 2025 Da Maki Kaso 0.4
Bankin duniya ya fitar da sabon hasashensa kan tattalin arzikin Sin a bana a jiya Alhamis, inda ya daga na kasar Sin da maki kaso 0.4.
Bankin ya ce manufofin kudi masu inganci sun sun taimaka wa harkokin sayayya da na zuba jari. Haka kuma, bukatu daga kasashe masu tasowa sun ingiza fitar da kayayyaki daga kasar.
Daraktar sashen kula da harkokin Sin da Mongolia da Korea na bankin duniya, Mara Warwick, ta ce ci gaban kasar Sin a shekaru masu zuwa zai kara dogara kan sayayya a cikin gida. Kuma baya ga dabarun kashe kudi na gajeren lokaci, inganta gyare-gyaren tsarin kyautatawa al’umma da samar da kyakkyawan muhallin kasuwanci, ka iya taimakawa kara kwarin gwiwa da shimfida tubalin juriya da ci gaba mai dorewa. (FMM)
ADVERTISEMENT ShareTweetSendShare MASU ALAKA