Iran Ba Zata Karbi Umrni Daga Wani Kan Shrin Nukliyar Kasar Ba
Published: 12th, March 2025 GMT
Mohammad Reza Aref mataimakin shugaban kasa na farko a nan JMI ya bayyana cewa gwamnatin kasar Iran ba zata karbi umurni daga wata kasa dangane da shirin makamashin nukliya ta zaman lafiya na kasar ba.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Reza Aref yana fadar haka a jiya Talata, ya kuma kara da cewa, JMI ta na ci gaba da jajircewa da takunkuman tattalin arzikin da kasashen yamma suka dora mata, dangane da shirin kasar na amfani da fasahar Nukliya.
Sai dai har yanzun ba zata nemi shawara ko karbi umurni daga wata kasa a kan amfani da wannan fasaha mai dimbin amfani ba.
Mataimakin shugaban kasar ya ce, sinadarin Nukliya ya na da matukar amfani kuma mai yawa, bai kamata a haramtawa wasu kasashe amfani da shi ba.
Banda haka ya ce, fasahar nukliya ci gaba ne, idan an hada tsarin addinin musulunci da ke gudanar da kasar, ci gaba ne mai yawa. Yace kasar Iran tana da arziki mai yawa tare da wadannan abubuwa biyu.
Yace ammam wasu kasashe a duniya suna sun su takaita wannan fasahar garesu su kadai, don su rika bautar da mutane. Basa son ganin Iran ta kai ga wannan fasahar, don haka sun samar da ra’ayin kin iraniyawa a duniya.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Za A Yi Manyan Zabuka A Kasar Habasha A Watan Yuni Na 2026
Hukumar zaben kasar Habasha ta sanar da cewa za a yi manyan zabukan kasar a ranar 1 ga watan Yuni na 2026.
Shugabar hukumar zaben kasar ta Habasha Melatwork Hailu ta fada wa kafafen watsa labarun kasar cewa; Ana gudanar da ayyukan ne a yanzu domin tsara wuraren da za a yi zabukan da samar da rumfunan zabe a cikin rassan da za a kada kuri’a.”
Har ila yau shugabar hukumar zaben kasar ta Habasha ta ce, jam’iyyun siyasar kasar sun sami horon da ya dace domin bayyana da tallata manufofinsu ga jama’ar kasar.
Sai dai yin zabe a kasar ta Habasha yana fuskantar kalubale mai yawa. Kasar dai ba ta dade da fitowa daga yakin basasa ba wanda aka yi a tsakanin gwamnatin tarayya da yankin Tigray da aka yi a tsakanin 2020 zuwa 2022.
Rikicin ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 600,000, kuma wasu da adadinsu ya kai miliyan 1 su ka bar gidajensu.
Kuma har yanzu ana fama da tashe-tashen hankula a cikin yankunan Oromia da Amhara.
A jawabin da ya gabatar a ranar 28 ga watan Oktoba, Fira ministan kasar ta Habasha Abiy Ahmed ya ce; Gwamnatin kasar tana da karfin da za ta iya gudanar da zabukan.”
Haka nan kuma ya ce, zaben da za a yi zai zama shi ne mafi tsaruwa a tarihin kasar.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Turkiya A Shirye Take Ta Aike Da Sojoji Zuwa Yankin Gaza December 12, 2025 Kremlin: Putin Ya Bayyana Wa Shugaba Maduro Na Venezuela Goyon Bayansa December 12, 2025 Ben Gafir Ya Sha Alwashin Rushe Kabarin Sheikh Izzuddin Alkassam December 12, 2025 Maduro: Amurka Ta Bude Sabon Salon Fashi Akan Doron Ruwa December 12, 2025 Ayatollah Khamenei : Iran na samun ci gaba duk da kalubale da dama December 11, 2025 Kyaftin Traoré : Yau Burkina ta zama misali a duniya December 11, 2025 Iran da Kazakhstan Sun rattaba hannu kan yarjeniyoyi da dama December 11, 2025 Hamas : Isra’ila ta gaza cika alkawarin da ta dauka kan yarjejeniyar tsagaita wuta December 11, 2025 Kasashen ECOWAS sun rage kudin sufirin jiragan sama a tsakaninsu December 11, 2025 Dakarun IRGC 3 Sun Yi Shahada A wani Harin Ta’addanci A Kudancin Kasar Iran December 11, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci