HausaTv:
2025-03-28@09:59:27 GMT

Iran Ba Zata Karbi Umrni Daga Wani Kan Shrin Nukliyar Kasar Ba

Published: 12th, March 2025 GMT

Mohammad Reza Aref mataimakin shugaban kasa na farko a nan JMI ya bayyana cewa gwamnatin kasar Iran ba zata karbi umurni daga wata kasa dangane da shirin makamashin nukliya ta zaman lafiya na kasar ba.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Reza Aref yana fadar haka a jiya Talata, ya kuma kara da cewa, JMI ta na ci gaba da jajircewa da takunkuman tattalin arzikin da kasashen yamma suka dora mata, dangane da shirin kasar na amfani da fasahar Nukliya.

Sai dai har yanzun ba zata nemi shawara ko karbi umurni daga wata kasa a kan amfani da wannan fasaha mai dimbin amfani ba.

Mataimakin shugaban kasar ya ce, sinadarin Nukliya ya na da matukar amfani kuma mai yawa, bai kamata a haramtawa wasu kasashe amfani da shi ba.

Banda haka ya ce, fasahar nukliya ci gaba ne, idan an hada tsarin  addinin musulunci da ke gudanar da kasar, ci gaba ne mai yawa. Yace kasar Iran tana da arziki mai yawa tare da wadannan abubuwa biyu.

Yace ammam wasu kasashe a duniya suna sun su takaita wannan fasahar garesu su kadai, don su rika bautar da mutane. Basa son ganin Iran ta kai ga wannan fasahar, don haka sun samar da ra’ayin kin iraniyawa a duniya.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Yansanda A Kasar Turkiyya Suna Ci Gaba Da Fafatawa Da Yan Adawa A Birnin Istambul

Yansanda a kasar Turkiyya suna ci gaba da fafatawa day an adawa masu goyon bayan magajin garin birnin Istambul Ekram Imam oglu.

Tashar talabijin ta Al-mayadeen ta kasar Lebanon ta bayyana cewa magajin garin na birnin Istambul yana daga cikin fitattun masu adawa da gwamnatin Urdugan, sannan a halin yanzu jami’an sharia a kasar sun bada sanarwan cewa sun kammala bincike a kansa, kuma nan ba da dadewa ba zasu gurfanar da shi a gaban kotu don fuskantar shari’a.

A ranar laraban da ta gabat ce gwamnatin kasar Turkiya ta bada umurnin kama Ekram Imam oglu magajin garin birnin Istambul tare da zarginsa da cin hanci da rashawa da kuma ayyukan ta’addanci. Wanda ya musanta hakan a yanke.

Har’ila yau masu gabatar da shari’a a kasar sun bukaci a ci gaba da tsare magajin garin har zuwa lokacinda za’a fara shari’arsa a cikin yan kwanaki masu zuwa. Tun ranar laraban da ta gabace yan sanda a birnin istambul da kuma wasu birane a kasar suke fafatawa da dubban daruruwan magoya bayan Imam oglu wadanda suke bukatar a sake shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Ta Gudanar Da Faretin Jiragen Ruwa A Tekun Farisa Da Kuma Tekun Caspian Don Raya Ranar Kudud Ta Duniya
  • Sojojin Sudan Suna Ci Gaba Da Samun Nasara A Akan Dakarun Kai Daukin Gaggawa
  • Nijar : An nada Janar Tiani, a mukamin shugaban rikon kwarya
  • Gwamnatin Tarayya ta ayyana Litinin da Talata a matsayin hutun sallaGwamnati Ta Ayyana 31 Ga Maris Da 1 Ga Afrilu A Matsayin Ranakun Hutu Don Bukin Eid-el-Fitr Gwamnatin Tarayya ta ayyana Litinin, 31 ga Maris, da Talata, 1 ga Afrilu, a matsayin ranakun hu
  • Jagoran Juyin Musulunci Ya Amince Da Yin Afuwa Ga Wasu Fursunoni Masu Yawa
  • Hukumar IAEA ta yi ishara da yiwuwar sake komawa teburin tattaunawa tare da Iran
  • Sin Na Ci Gaba Da Kasancewa Cibiyar Rarraba Hajojin Da Masana’antu Ke Sarrafawa
  • Kasuwar Kayayyakin Masarufi Ta Sin Za Ta Ci Gaba Da Nuna Yanayin Bunkasa Bisa Daidaito A Bana
  • Yansanda A Kasar Turkiyya Suna Ci Gaba Da Fafatawa Da Yan Adawa A Birnin Istambul
  • Shugaban Majalisar Dokokin Kasar Lebanon Ya Ce Basa Da Wani Shiri Na Samar Da Haldar Jakadanci Da HKI