Iran Ba Zata Karbi Umrni Daga Wani Kan Shrin Nukliyar Kasar Ba
Published: 12th, March 2025 GMT
Mohammad Reza Aref mataimakin shugaban kasa na farko a nan JMI ya bayyana cewa gwamnatin kasar Iran ba zata karbi umurni daga wata kasa dangane da shirin makamashin nukliya ta zaman lafiya na kasar ba.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Reza Aref yana fadar haka a jiya Talata, ya kuma kara da cewa, JMI ta na ci gaba da jajircewa da takunkuman tattalin arzikin da kasashen yamma suka dora mata, dangane da shirin kasar na amfani da fasahar Nukliya.
Sai dai har yanzun ba zata nemi shawara ko karbi umurni daga wata kasa a kan amfani da wannan fasaha mai dimbin amfani ba.
Mataimakin shugaban kasar ya ce, sinadarin Nukliya ya na da matukar amfani kuma mai yawa, bai kamata a haramtawa wasu kasashe amfani da shi ba.
Banda haka ya ce, fasahar nukliya ci gaba ne, idan an hada tsarin addinin musulunci da ke gudanar da kasar, ci gaba ne mai yawa. Yace kasar Iran tana da arziki mai yawa tare da wadannan abubuwa biyu.
Yace ammam wasu kasashe a duniya suna sun su takaita wannan fasahar garesu su kadai, don su rika bautar da mutane. Basa son ganin Iran ta kai ga wannan fasahar, don haka sun samar da ra’ayin kin iraniyawa a duniya.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran: Kalaman Da Trump Yayi Na Rufe Sararin Samaniyar Kasar Venuzuwela Ya Sabama Doka.
Rahotanni sun bayyana cewa iran ta yi tir da sanarwar da shugaban Amurka ta fitar na rufe sararin samaniyar kasar venuzuwela kuma ta bayyana shi a matsayin keta dokokin kasa da kasa, da kuma dokokin kula da zirga –zirgar jiragen sama.
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar iran Isma’ila Baghae ne ya fitar da wannan sanarwa inda ya jaddada cewa abin da Washington ta kira a matsayin sanarwa wani bangare ne na adawa na dogon lokaci da kokarin karbe ikon kasar venuzuwela, kuma ya bayyana matakin a matsayin na son rai da ya sabama doka.
Wannan sanarwar ta trump ta ja hankali sosai a bangaren diplomasiya da kuma masana harkokin zirga zirgar jiragen sama, inda wasu kwararru ke ganin babu wata kasa da take da ikon rufe sararin samaniyar wata kasa bisa dokokin sufurin jiragen sama.
A baya bayan nan ne shugaban Amurka Donald Trump ya rubuta a shafinsa na sadarwa na truth social na yin barazana a hukumance cewa matuka jiragen sama da da sauran kamfanonin jiragen sama su dauka sararin samaniyar kasar venuzuwela an rufe shi baki daya.
Ana ta bangaren kasar venuzuwela ta yi watsi da wannan sanarwar tare da bayyana ta a matsayin siyasa kuma tana son mayar da kasar saniyar ware maimakon tabbatar da tsaro
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Shugaban Pakistan Yayi Kira Da A Gudanar Da Bincike Kan Laifukan Yaki Da HKI Ke Tafkawa November 30, 2025 MDD Ta Bukaci Isra’ila Da ta Kawo Karshen Mamayar Da Tayi wa Yankunan Falasdinawa November 30, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 163 November 29, 2025 Iran A Shirye Take Ta Maida Martani Mai Kan Kan Duk Wata Barazanar Tsaro November 29, 2025 Iran Ta Kakkabo Jiragen Yakin HKI Fiye Da 196 A Yakin Kwanaki 12 November 29, 2025 Trump Ya Bada Sanarwan Rufe Sararin Samaniyar Kasar Venezuela Gaba Daya November 29, 2025 Kamfanin Kera Jiragen Sama Na Airbus Ya Bukaci A Dawo Da Jiragen Sama Samfrin A320 Saboda Gyara November 29, 2025 An Kammala Gasar ‘Rayan’ Na AI Ta Kasa Da Kasa A Nan Tehran November 29, 2025 Iran da Kasashen Larabawa Sun Yi Allah wadai da kutsen sojojin Isra’ila a Kudancin Siriya November 29, 2025 MDD ta yi kira da a gudanar da cikakken bincike kan kisan gillar da aka yi wa Falasdinawa November 29, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci