Gwamnatin Bahrain Ta Kara Kaimi Wajen Kama Yan Adawa Daga Ciki Har Da Yara Kanana
Published: 12th, March 2025 GMT
Wata kungiyar kare hakkin bil’adama a kasar Bahrain ta bayyana cewa, gwamnatin kasar ta kara yawan kama mutane yan adawa daga ciki har da yara kanana saboda shiga cikin zanga-zanga, ko kuma bayyana ra’ayinsu na siyasa.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto kungiyar kare hakkin bil’adama ta ” The Americans for Democracy & Human Rights in Bahrain (ADHRB), ta kuma kara da cewa, bayan afwar da gwamnatin Bahrain ta yi wa yan adawar kasar kimani 1,584 a cikin watan Afrilun shekara ta 2024 da ya gabata, daga ciki har da yara 40, amma daga baya ta fara kama yan adawan tana tsaresu.
Shugaban kungiyar kare hakkin bil’adama ta ADHRB Hussain Abdullah yayi allawadai da kama yan adawa musamman yara kanana kimani 11 da mahukuntan kasar ta Bahrain suka tsare, ba tare da gabatar da su a gaban kotu ba. Har’ila yau tare da hana iyayensu ziyartarsu, ko kuma sanin inda suke.
Sannan akwai rahoton azabtar da wasu daga cikinsu, da hanasu abinci mai gina jiki da kuma rashin kula da lafiyarsu ko basu magani.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Harin Benuwe: ’Yan sanda sun tarwatsa masu zanga-zanga
An shiga zaman ɗari-ɗari a garin Makurdi na Jihar Benuwe, bayan ’yan sanda sun harba barkonon tsohuwa domin tarwatsa wasu masu zanga-zanga a shataletalen Wurukum.
Masu zanga-zangar sun fara taruwa da misalin ƙarfe 9:30 na safe domin nuna fushinsu kan kisan mutane sama da 100 a garin Yelewata da ke Ƙaramar Hukumar Guma, a ranar Asabar.
Takarar Tinubu: Rikici ya ɓarke a APC bayan Ganduje ya ƙi goyon bayan Shettima HOTUNA: Yadda aka yi sulhu da ƙasurgumin ɗan fashin daji Ado Aliero a KatsinaTun kafin fara zanga-zangar, jami’an tsaro daga hukumomi daban-daban sun mamaye manyan hanyoyi a birnin Makurdi.
Da safiyar ranar Lahadi da misalin ƙarfe 7 na safe jami’an tsaro, ciki har da motar yaƙi ta ‘yan sanda sun yi wa wajen tsinke.
An kuma hango sojoji a gadar kusa da wajen, yayin da jami’an NDLEA, NSCDC da sauran hukumomi suka kasance ɗauke da manyan makamai.
Rahotanni sun nuna cewa wannan matakin tsaro an ɗauke shi ne don hana zanga-zangar, amma da mutane suka fara taruwa, ‘yan sanda sun harba barkonon tsohuwa da misalin ƙarfe 11 na safe domin tarwatsa su.
Duk da haka, masu zanga-zangar ba su karaya ba, yayin da wani shahararren mai fafutuka a kafafen sada zumunta, VeryDarkMan, ya jagoranci zanga-zangar.
Kwamishinan ’Yan Sandan jihar, Ifeanyi Enemari, ya isa wajen zanga-zangar sannan ya roƙi matasan da ke zanga-zangar da su zauna lafiya.
Ya ce jami’an tsaro na bakin ƙoƙarinsu don kawo ƙarshen kashe-kashen da ke faruwa a jihar.
Ya bayyana cewa Sufeto Janar na ’Yan Sanda ya tura rundunoni na musamman zuwa jihar domin taimakawa wajen tsaro, kuma wasu daga cikinsu sun isa jihar, sauran kuma na hanya.
Kwamishinan ya ce gwamnati ta bai wa jami’an tsaro goyon baya sosai kuma an riga an kama wasu.