Wata kungiyar kare hakkin bil’adama a kasar Bahrain ta bayyana cewa, gwamnatin kasar ta kara yawan kama mutane yan adawa daga ciki har da yara kanana saboda shiga cikin zanga-zanga, ko kuma bayyana ra’ayinsu na siyasa.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto kungiyar kare hakkin bil’adama ta ” The Americans for Democracy & Human Rights in Bahrain (ADHRB), ta kuma kara da cewa, bayan afwar da gwamnatin Bahrain ta yi wa yan adawar kasar kimani 1,584 a cikin watan Afrilun shekara ta 2024 da ya gabata, daga ciki har da yara 40, amma daga baya ta fara kama yan adawan tana  tsaresu.

Suna kama dukan wanda ya nuna  kiyyarsa, ko ya bayyana ra’ayinsa na siyasa, ko kuma ya fito zanga-zanga a cikin kasar, daga ciki har da yara kanana. Musamman a tsakanin watannin Augusta zuwa watan Decemban shekara ta 2024.

Shugaban kungiyar kare hakkin bil’adama ta ADHRB Hussain Abdullah yayi allawadai da kama yan adawa musamman yara kanana kimani 11 da mahukuntan kasar ta Bahrain suka tsare, ba tare da gabatar da su a gaban kotu ba. Har’ila yau tare da hana iyayensu ziyartarsu, ko kuma sanin inda suke.

Sannan akwai rahoton azabtar da wasu daga cikinsu, da hanasu abinci mai gina jiki da kuma rashin kula da lafiyarsu ko basu magani.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Wargajewar HKI Ba Makawa Inji Wani Janar Daga Sojojin JMI

Daya daga cikin manya manyan sojojin kasar Iran ya bayyana cewa wargajewar HKI da kuma halakar Firai ministan kasar tabbas ne babu makawa. Ya kuma gargadi makiyan JMI kan cewa duk wani kuskuren da zasu tabka sai ya sanya dukkan sansanoninsu na soje a yankin cikinbabban barazana na lalatasu.

Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta nakalto , Major General Yahya Rahim Safavi yana fadar haka a taron addu’a da kuma girmma marigayi Manji Janar Muhammad Baqiri babban hafsan hafsoshin kasar wanda yayi shahada a ranar Jumma’a 13 ga watan Yunin da ya gabata.

Ya kuma kara da cewa babban shaitan da kuma karamin shaitan duk zasu halaka sun kasa kaiwa ga bukatunsu a yankin kwanaki 12 da suka dorawa JMI. Janar Safawi wanda kuma ya kasance daga cikin masu bawa jagoran juyin juya halin musulunci a nan Iran ya kara da cewa yakin da ya gabata  ya gaggauta halaka da kuma bacewar HKI daga yankin gaban ta tsakiya.

Ya ce, tsagaita wutan da aka amince, dan sararawa ce ga makiya JMI amma su tabbatar da cewa da yardar All…yaki mafi muni yana gabansu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Kasar Iran Ya Bayyana Irin Aniyar Da Gwamantinsa Ta Kudurta Wajen Kare Tsaron Kasa Da Al’ummarta
  • ’Yan sanda sun kama wani mutum da jabun kuɗi a Gombe
  • David Mark ya fice daga PDP, ya shiga haɗaka don ƙalubalantar Tinubu
  • Arsenal Ta Sayi Kepa Daga Chelsea
  • ’Yan sanda sun kama matashin da ya kashe mahaifiyarsa a Jigawa
  • Wargajewar HKI Ba Makawa Inji Wani Janar Daga Sojojin JMI
  • Togo: An Kashe Mutane 7 A Zanga-zangar Kin Jinin Gwamnati
  • Iran Ta Bawo Mayakan Huthi Fasahar Kera Makamai Masu Linzami Daga Cikin Ruwa
  • Cikar MDD Shekara 80: Nasarorinmu Sun Kara Mana Kaimi Da Kyakkyawar Makoma A Nan Gaba
  • Iran: An Kama Wani Dan Leken Asirin “Mosad” A Tehran A Jiya Lahadi