Wata kungiyar kare hakkin bil’adama a kasar Bahrain ta bayyana cewa, gwamnatin kasar ta kara yawan kama mutane yan adawa daga ciki har da yara kanana saboda shiga cikin zanga-zanga, ko kuma bayyana ra’ayinsu na siyasa.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto kungiyar kare hakkin bil’adama ta ” The Americans for Democracy & Human Rights in Bahrain (ADHRB), ta kuma kara da cewa, bayan afwar da gwamnatin Bahrain ta yi wa yan adawar kasar kimani 1,584 a cikin watan Afrilun shekara ta 2024 da ya gabata, daga ciki har da yara 40, amma daga baya ta fara kama yan adawan tana  tsaresu.

Suna kama dukan wanda ya nuna  kiyyarsa, ko ya bayyana ra’ayinsa na siyasa, ko kuma ya fito zanga-zanga a cikin kasar, daga ciki har da yara kanana. Musamman a tsakanin watannin Augusta zuwa watan Decemban shekara ta 2024.

Shugaban kungiyar kare hakkin bil’adama ta ADHRB Hussain Abdullah yayi allawadai da kama yan adawa musamman yara kanana kimani 11 da mahukuntan kasar ta Bahrain suka tsare, ba tare da gabatar da su a gaban kotu ba. Har’ila yau tare da hana iyayensu ziyartarsu, ko kuma sanin inda suke.

Sannan akwai rahoton azabtar da wasu daga cikinsu, da hanasu abinci mai gina jiki da kuma rashin kula da lafiyarsu ko basu magani.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Xi Jinping Ya Yi Kira Da a Kara Horar Da Kwararrun Masana A Fannin Aikin Gona

Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya amsa wasika daga daukacin malamai da daliban jami’ar nazarin aikin gona ta kasar Sin, inda ya taya dukkan malamai da dalibai da ma’aikatan jami’ar, da kuma wadanda suka kammala karatu a jami’ar murnar cika shekaru 120 da kafuwar jami’ar.

Xi ya yi fatan jami’ar za ta ci gaba da tafiyar da harkokinta yadda ya kamata, da kudurce aniyar inganta aikin gona don amfanin kasa, da kuma zurfafa yin gyare-gyare kan hanyoyin koyarwa da ilmantarwa, da kara kokarin bincike, da kirkire-kirkire a fannin aikin gona, da kuma amfani da sakamakon binciken yadda ya kamata, ta yadda za a kai ga horar da karin kwararrun masana a fannin aikin gona, don ba da sabuwar gudummawa ga karfafa karfin kasar Sin ta fannin aikin gona, da sa kaimi ga zamanantar da kasa bisa salon kasar Sin. (Amina Xu)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Shugabannin Kasashe Da Dama Sun Yaba Wa Sin Kan Gudummawar Da Ta Bayar A Fannin Tabbatar Da Daidaiton Jinsi October 16, 2025 Daga Birnin Sin Ɗaga Matsayin Dangantakar Zambia Da Sin Ya Haifar Da Manyan Nasarori October 16, 2025 Daga Birnin Sin Sashen Cinikayyar Kamfanonin Sarrafa Hajoji Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso 4.7 Bisa Dari Cikin Watanni Tara Na Farkon Shekarar Nan October 15, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NIEPA Ta Jinjinawa UNICEF Bisa Kare Hakkokin Yara Na Samun Ilimi A Najeriya
  • Hukumar Gidan Yarin Kano Ta Tabbatar Da Dauke Abduljabbar Zuwa Abuja
  • An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana
  • Gwamnan Gombe ya ƙaddamar da shirin tallafa wa karatun yara mata
  • Majalisar Dokokin Jihar Kaduna Za Ta Kafa Dokar Wuraren Tsaro A Makarantu
  • Gwamnatin Jigawa Ta Raba Tallafin Kayayyakin Sana’o’i A Karamar Hukumar Gagarawa
  • An kama ɓarayi da motocin da aka sace a Gombe
  • Xi Jinping Ya Yi Kira Da a Kara Horar Da Kwararrun Masana A Fannin Aikin Gona
  • Tarayyar Afirka AU, Ta Jingine Samuwar Madagaska Daga Cikin Kungiyar
  • DSS ta cafke tsoffin jami’anta 2 kan aikata zamba