Gwamnatin Bahrain Ta Kara Kaimi Wajen Kama Yan Adawa Daga Ciki Har Da Yara Kanana
Published: 12th, March 2025 GMT
Wata kungiyar kare hakkin bil’adama a kasar Bahrain ta bayyana cewa, gwamnatin kasar ta kara yawan kama mutane yan adawa daga ciki har da yara kanana saboda shiga cikin zanga-zanga, ko kuma bayyana ra’ayinsu na siyasa.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto kungiyar kare hakkin bil’adama ta ” The Americans for Democracy & Human Rights in Bahrain (ADHRB), ta kuma kara da cewa, bayan afwar da gwamnatin Bahrain ta yi wa yan adawar kasar kimani 1,584 a cikin watan Afrilun shekara ta 2024 da ya gabata, daga ciki har da yara 40, amma daga baya ta fara kama yan adawan tana tsaresu.
Shugaban kungiyar kare hakkin bil’adama ta ADHRB Hussain Abdullah yayi allawadai da kama yan adawa musamman yara kanana kimani 11 da mahukuntan kasar ta Bahrain suka tsare, ba tare da gabatar da su a gaban kotu ba. Har’ila yau tare da hana iyayensu ziyartarsu, ko kuma sanin inda suke.
Sannan akwai rahoton azabtar da wasu daga cikinsu, da hanasu abinci mai gina jiki da kuma rashin kula da lafiyarsu ko basu magani.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Muna buƙatar taimakon ƙasashen waje kan tsaro a Najeriya — Obasanjo
Tsohon Shugaban Ƙasa, Olusegun Obasanjo, ya ce Najeriya na buƙatar taimakon ƙasashen waje don dakatar da kashe-kashe da rashin tsaro, domin gwamnati ta gaza kare al’umma.
Ya bayyana haka ne a wani taro da ya gudana Jihar Filato, inda ya ce a ci gaba ya kawo fasahar da za a iya gano masu aikata laifi, amma ta gaza yin hakan.
Yadda aka horar da mata 100 sana’o’in dogaro da kai a Gombe Yadda ’yan mata ke kuɗancewa da kasuwancin fara a KanoObasanjo, ya yi gargaɗin cewa ana kashe ’yan Najeriya ba tare da la’akari da addini ko ƙabilanci ba, don haka gwamnati ta gaggauta ɗaukar mataki.
Ya ce idan gwamnati ta kasa kare jama’a, ’yan ƙasa na da damar neman taimakon ƙasashen duniya.
Ya soki masu kare kashe-kashen da ake yi, inda ya bayyana cewa rayuwar kowanne ɗan Najeriya na da muhimmanci.
Obasanjo, ya kuma tambayi dalilin da ya sa gwamnati ke tattaunawa ko biyan kuɗin ’yan bindiga kuɗin fansa, inda ya ce hakan na ƙara taɓarɓarewar lamarin.
Ya kira ’yan Najeriya da su haɗa kai domin tabbatar da zaman lafiya, tare da tabbatar da cewa kowa na rayuwa ba tare da fargaba ba.
Gwamnan Jihar Filato, Caleb Mutfwang, shi ma ya yi jawabi a wajen taron.
Ya ce al’ummar jihar dole su haɗa kai su daina abubuwan da za su raba su.
Mutfwang, ya buƙaci jama’a su yi aiki tare domin jihar ta ci gaba da kuma shawo kan matsalolin tsaro.