Gwamnatin Bahrain Ta Kara Kaimi Wajen Kama Yan Adawa Daga Ciki Har Da Yara Kanana
Published: 12th, March 2025 GMT
Wata kungiyar kare hakkin bil’adama a kasar Bahrain ta bayyana cewa, gwamnatin kasar ta kara yawan kama mutane yan adawa daga ciki har da yara kanana saboda shiga cikin zanga-zanga, ko kuma bayyana ra’ayinsu na siyasa.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto kungiyar kare hakkin bil’adama ta ” The Americans for Democracy & Human Rights in Bahrain (ADHRB), ta kuma kara da cewa, bayan afwar da gwamnatin Bahrain ta yi wa yan adawar kasar kimani 1,584 a cikin watan Afrilun shekara ta 2024 da ya gabata, daga ciki har da yara 40, amma daga baya ta fara kama yan adawan tana tsaresu.
Shugaban kungiyar kare hakkin bil’adama ta ADHRB Hussain Abdullah yayi allawadai da kama yan adawa musamman yara kanana kimani 11 da mahukuntan kasar ta Bahrain suka tsare, ba tare da gabatar da su a gaban kotu ba. Har’ila yau tare da hana iyayensu ziyartarsu, ko kuma sanin inda suke.
Sannan akwai rahoton azabtar da wasu daga cikinsu, da hanasu abinci mai gina jiki da kuma rashin kula da lafiyarsu ko basu magani.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Sin Ta Gudanar Da Taron Tunawa Da Kisan Kiyashin Nanjing
Cikin makwanni shida, dakarun na Japan sun hallaka Sinawa fararen hula, da sojoji da ba sa dauke da makamai kimanin 300,000, a wata ta’asa mafi muni da ta auku yayin yakin duniya na biyu.
Memban ofishin siyasa na kwamitin kolin JKS Shi Taifeng, ya halarci taron tare da gabatar da jawabi. Cikin jawabin na sa, ya yi kira ga daukacin Sinawa da su zage-damtse wajen ingiza farfado da kasa, da bayar da gagarumar gudummawa ga ayyukan wanzar da zaman lafiya da ci gaban bil’adama. (Mai fassara: Saminu Alhassan)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA