HausaTv:
2025-12-13@14:29:02 GMT

Kungiyar Tarayyar Turai ta yi barazanar sake kakaba wa Syria takunkumi

Published: 12th, March 2025 GMT

Jami’ar kula da manufofin ketare ta Tarayyar Turai, Kaya Kalas, ta tabbatar da cewa, EU za ta iya sake kakaba takunkumi kan kasar Syria, idan aka samu tabarbarewar lamurra, tana mai nuni da yadda ake cin zarafin fararen hula a gabar tekun Syria.

Kaya Kalas ta shaidawa kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya cewa, “Muna shirye-shiryen mayar da takunkumi kan Syria, idan muka ga tabarbarewar lamurra na ci gaba, inda ta jaddada cewa, dole ne mika mulki ya kasance cikin lumana da kuma hadin kai, kuma dole ne a kare fararen hula a kowane hali.

Ta bukaci dukkan masu ruwa da tsaki na waje da su mutunta hadin kan Syria, da kuma iko da iyakokinta.”

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Amurka ta kama jirgin ruwan dakon man Najeriya

Amurka ta kama wani katafaren jirgin ruwan dakon man Najeriya kan zargin safarar ɗanyen mai na sata.

Jami’an tsaron Amurka sun kama jirgin mai suna Super Tanker, mai lamba 9304667, ne, bayan sun gano cewa ya yi basaja, inda ya maƙala tutar wata kasa daban maimakon ta Najeriya yayin shigarsa ruwan Amurka.

Wannan ya haifar da shakku kan sahihancin jirgin da ma wadanda ke tafiyar da shi. Daga bisani kuma aka gano cewa ba ya cikin tsarin jiragen da ake tsammani a hukumance.

Hukumomin Amurka sun ƙaddamar da bincike kan jirgin, wanda ake hasashen zai bankaɗo badaƙalar safarar man sata da fataucin miyagun ƙwayoyi da ayyukan ’yan fashin teku da ke shafar ƙasashe da dama.

An shafe shekaru ana magana ba kan matsalar yawan satar ɗanyen mai ayankin Neja Delta mai arzikin mai ya zame wa al’umma tamkar tamkar masifa.

Bayanan kama jirgin

Jirgin mallakin wani babban ɗan kasuwa a Najeriya mai kamfanin Thomarose Global Ventures, yanzu haka yana tsare a hannun jami’an tsaron Amurka.

Bayanan farko sun nuna cewa an fara gudanar da bincike kan alakar jirgin da safarar muggan ƙwayoyi da kuma harkokin barayin kan teku, musamman a zirin Tekun Gunea da ke addabar kasashe da dama, ciki har da Najeriya, Kamaru, Sao Tome da Ghana.

Alƙaluman da aka fitar a watan Nuwamba, shekarar 2025, sun nuna cewa Najeriya ta yi asarar kimanin dala biliyan 300 sakamakon satar ɗanyen mai a ciki da wajen kasar.

Wannan satar mai ba wai kawai tana jawo asarar kudi ba, har ma tana barin baya da kurar gurbata muhalli, lamarin da ke ci gaba da kassara yankin mai arzikin mai na Niger Delta.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan(a) 170
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan(a) 169
  • Amurka Ta Sanya Sabbin Takunkumi A Bangaren Manfetur Na  Venuzuela
  • Amurka ta kama jirgin ruwan dakon man Najeriya
  • Birtaniya Ta yi  Barazanar Yanke Gudunmawar Da Take Bawa Kotun Duniya
  • Kungiyar NLC A Najeriya Ta Shirya Zanga-Zanga Kan Matsalar Rashin Tsaro A Fadin Kasa
  • Duniyarmu A Yau: Iran Da Amurka A Yakin Kwanaki 12 Wa Ya Sami Nasara
  • Dan sanda ya yi batan dabo a bakin aikinsa a Katsina
  • Taron Abuja kan Tattaunawakan Tattalin Arziki Kasa- “Akwai yiyuwar tattalin arzikin kasa zai murmure a shekarar 2026”
  • Ƴan Bindigar Daji: Jihohin Arewa 7 Sun Kaddamar Da Rundunar Fatattakar Su