HausaTv:
2025-11-25@15:09:43 GMT

Kungiyar Tarayyar Turai ta yi barazanar sake kakaba wa Syria takunkumi

Published: 12th, March 2025 GMT

Jami’ar kula da manufofin ketare ta Tarayyar Turai, Kaya Kalas, ta tabbatar da cewa, EU za ta iya sake kakaba takunkumi kan kasar Syria, idan aka samu tabarbarewar lamurra, tana mai nuni da yadda ake cin zarafin fararen hula a gabar tekun Syria.

Kaya Kalas ta shaidawa kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya cewa, “Muna shirye-shiryen mayar da takunkumi kan Syria, idan muka ga tabarbarewar lamurra na ci gaba, inda ta jaddada cewa, dole ne mika mulki ya kasance cikin lumana da kuma hadin kai, kuma dole ne a kare fararen hula a kowane hali.

Ta bukaci dukkan masu ruwa da tsaki na waje da su mutunta hadin kan Syria, da kuma iko da iyakokinta.”

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

An ceto mutum 38 da aka sace a cocin Kwara — Tinubu

Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana cewar an ceto dukkanin mutanen da mahara suka sace a wata coci a yankin Eruku na Jihar Kwara.

’Yan bindigar sun sace masu ibadar ne a ranar Talata, lokacin da suka kai hari cocin Christ Apostolic Church (CAC) da ke Oke Isegun a Eruku, wani gari da ke iyaka da Kogi a Karamar Hukumar Ekiti ta Jihar Kwara.

ISWAP ta sace ’yan mata 13 a Borno Barin jama’a su kare kansu ne ke rura rashin tsaro — Sojoji

A cikin wani sako da Tinubu ya wallafa a X a ranar Lahadi, ya ce yana bibiyar yanayin tsaro a fadin kasar nan, kuma zai tabbatar da cewa gwamnatinsa ta kare ’yan Najeriya.

An yada bidiyon yadda maharan suka shiga cocin suka yi awon gaba da masu ibada yayin da suke tsaka da addu’a.

Lokacin da maharan suka dinga harbe-harbe a ciki cocin, wani Fasto ya jagoranci jama’a inda suka nemi mafaka.

Ya kuma ce an ceto dalibai 51 da aka sace a Jihar Neja.

Tinubu ya kara da cewa: “’Yan uwana ’yan Najeriya, za ku iya tuna cewa na soke zuwa taron G20 da aka yi a Afirka ta Kudu domin na mayar da hankali kan sha’anin tsaro a gida.

“Ina yi wa jami’an tsaro godiya kan aiki tukuru da suka cikin kwanaki biyun da suka wuce, an ceto dukkanin masu ibada 38 da aka sace a Eruku, a Jihar Kwara.

“Ina kuma farin ciki cewa an gano dalibai 51 daga cikin wadanda aka sace a wata makaranta a Jihar Neja.

“Ina bibiyar sha’anin tsaro sosai kuma ina samun rahotanni kai-tsaye. Ba zan yi kasa a gwiwa ba. Kowane dan Najeriya yana da ’yancin samun tsaro, kuma a karkashin jagorancina, za mu kare wannan kasa da mutanen ciki.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Chelsea za ta kece raini da Barcelona a Gasar Zakarun Turai
  • Hamas Tayi Gargadi Game Da Rushewar Yarjejeniyar Bude Wuta Idan Israila Ta ci Gaba Da Kai Hare-Hare  
  • Sace ɗalibai: Idan Tinubu ba zai iya ba ya sauka kawai — PDP
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 162
  • Najeriya: Kungiyar Yan Ta’adda Ta ISWAP Ta Sace Yan Mata 13 A Jihar Borno
  • Iran ta sake tir da sabon kudurin da Hukumar (IAEA)
  • An ceto mutum 38 da aka sace a cocin Kwara — Tinubu
  • Antonio Guterres Ya Kira Yi Kungiyar G 20 Da Su Warware Matsalar Rashin Adalci A Harkokin Kasuwanci
  • An Fitar Da Kudurin Bayan Taron Kungiyar G20 Ba Tare Da Halartar Kasar Amurka Ba
  • An Gabatar Da Jawabin Bayan Taro Na Kungiyar G20 Duk Tare Da Kauracewar Amurka