HausaTv:
2025-12-01@10:08:39 GMT

Kungiyar Tarayyar Turai ta yi barazanar sake kakaba wa Syria takunkumi

Published: 12th, March 2025 GMT

Jami’ar kula da manufofin ketare ta Tarayyar Turai, Kaya Kalas, ta tabbatar da cewa, EU za ta iya sake kakaba takunkumi kan kasar Syria, idan aka samu tabarbarewar lamurra, tana mai nuni da yadda ake cin zarafin fararen hula a gabar tekun Syria.

Kaya Kalas ta shaidawa kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya cewa, “Muna shirye-shiryen mayar da takunkumi kan Syria, idan muka ga tabarbarewar lamurra na ci gaba, inda ta jaddada cewa, dole ne mika mulki ya kasance cikin lumana da kuma hadin kai, kuma dole ne a kare fararen hula a kowane hali.

Ta bukaci dukkan masu ruwa da tsaki na waje da su mutunta hadin kan Syria, da kuma iko da iyakokinta.”

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan bindiga sun sace amarya da ƙawenta 14 a Sakkwato

’Yan bindiga sun shiga garin Chaco da ke Ƙaramar Hukumar Wurno a Jihar Sakkwato, inda suka sace amarya da ƙawayenta guda 14.

Yayin da mutane ke tsaka shagalin bikin auren, sai ’yan bindigar suka afka musu tare da tarwatsa komai.

Mutum 6 sun jikkata a rikici manoma da makiyaya a Jigawa Sojoji sun ceto mutum 7 da ’yan bindiga suka sace a Kano

Sun shigo garin a ƙafa, inda suka wuce kai-tsaye zuwa gidansu amaryar ba tare da sun taɓa kowa ba.

Wani daga cikin iyayen ƙawayen amaryar ya shaida wa Aminiya cewa ba a tantance adadin waɗanda aka sace ba, amma wasu na cewa 15 ne, wasu kuma na cewa 13, amma amaryar da ’yarsa na cikin waɗanda aka sace.

Ya ce: “’Yata ’yar uwar amaryar ce. Ta zo ne kawai domin taya ’yar uwarta murnar bikinta a Chaco. Ban ɗauka za ta kwana a nan ba, ashe ƙaddara ke jiranta.”

A cewarsa, ’yan bindigar sun shiga garin ne da misalin ƙarfe 12 na daren ranar Asabar.

Sun shiga gidansu amaryar kai-tsaye inda suka yi awon gaba da ita da ƙawayenta.

Yayin da suke barin garin, matasa ’yan sa-kai sun yi ƙoƙarin dakatar da su, inda suka yi artabu, tare da yi wa ɗan ɗan sa-kai a hannu.

Ya ƙara da cewa har yanzu ’yan bindigar ba su tuntuɓi kowa ba domin neman kuɗin fansa.

Ranar Lahadi ita ce ranar da aka tsara domin ɗaura auren amaryar, sannan a kai ta gidan mijinta.

Lamarin tsaro a yankin gabashin Sakkwato na ƙara taɓarɓarewa.

Kakakin rundunar ’yan sandan Sakkwato, Ahmad Rufa’i, bai amsa kiran da aka masa ba, zuwa lokacin haɗa wannan rahoto.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Lebanon: Wasikar Kungiyar Hizbullah Ga Paparoma
  • ’Yan bindiga sun sace amarya da ƙawenta 14 a Sakkwato
  • An sake zabar Eto’o a matsayin Shugaban Hukumar kwallon kafa ta Kamaru  
  • Kuɗin Cizo ya tilasta rufe fitacciyar sinima a Faransa
  • Tinubu ya sake aike wa majalisa ƙarin sunayen jakadu 32
  • Iran A Shirye Take Ta Maida Martani Mai Kan Kan Duk Wata Barazanar Tsaro  
  • Gwamnatin Kano ta nemi a binciki Ganduje kan zargin kalaman ta da hankali
  • Kungiyar ‘Yan’uwa Musulmi Ta Soki Shirin Donald Trump Na Bayyanata A Matsayin Kungiyar ‘Yan Ta’adda
  • Kasashen Qatar Da Jordan Sun Yi Allawadai Da Harin “Isra’ila” A Kasar Syria
  • Ministocin Tarayyar Turai Sun yi Tir Da Karuwar Hare –Haren Da Yahudawa Ke Kai wa Falasdinawa