Kungiyar Tarayyar Turai ta yi barazanar sake kakaba wa Syria takunkumi
Published: 12th, March 2025 GMT
Jami’ar kula da manufofin ketare ta Tarayyar Turai, Kaya Kalas, ta tabbatar da cewa, EU za ta iya sake kakaba takunkumi kan kasar Syria, idan aka samu tabarbarewar lamurra, tana mai nuni da yadda ake cin zarafin fararen hula a gabar tekun Syria.
Kaya Kalas ta shaidawa kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya cewa, “Muna shirye-shiryen mayar da takunkumi kan Syria, idan muka ga tabarbarewar lamurra na ci gaba, inda ta jaddada cewa, dole ne mika mulki ya kasance cikin lumana da kuma hadin kai, kuma dole ne a kare fararen hula a kowane hali.
Ta bukaci dukkan masu ruwa da tsaki na waje da su mutunta hadin kan Syria, da kuma iko da iyakokinta.”
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Na gana da Tinubu kan Kanu ba batun sauya sheƙa ba — Gwamnan Abia
Gwamnan Jihar Abia, Alex Otti, ya bayyana cewa ziyarar da ya kai wa Shugaba Bola Tinubu, ba ta shafi batun sauya sheƙarsa zuwa jam’iyyar APC ba, sai dai a kan shugaban ’yan awaren ƙungiyar Biyafara, Nnamdi Kanu.
Mai bai wa gwamnan shawara kan harkokin yaɗa labarai, Ferdinand Ekeoma, ya fayyace cewa ziyarar ta biyo bayan iƙirarin tsohon Kwamishinan jihar Charles Ogbonnaya.
Mutum 6 sun rasu, 13 sun jikkata a hatsarin mota a Kogi ’Yan Najeriya suna da ƙwarin guiwa a kaina, ba zan ba su kunya ba — Ministan TsaroTsohon Kwamishinan, ya ce Gwamna Otti ya gana da Tinubu ne don tattaunawa shirin sauya sheƙarsa zuwa APC kafin zaɓen 2027.
“Gwamnan ya gana da Shugaban Ƙasa bayan ziyartar Kanu a gidan yarin Sakkwato a ranar Lahadi, 30 ga watan Nuwamba, 2025.
“Batun Kanu ne kaɗai aka tattauna, ba a kan harkokin siyasa ba,” in ji Ekeoma.
Ziyarar da Otti ya kai wa Kanu, na zuwa ne bayan da wata Kotun Tarayya a Abuja, ta yanke masa hukuncin ɗaurin rai da rai.
Ekeoma, ya bayyana cewa ganawar ta shafi batun yadda za a tattauna kan yiwuwar yi wa Kanu afuwa maimakon hukuncin ɗaurin rai da rai da kotu ta yi masa.