HausaTv:
2025-12-02@04:26:13 GMT

Kungiyar Tarayyar Turai ta yi barazanar sake kakaba wa Syria takunkumi

Published: 12th, March 2025 GMT

Jami’ar kula da manufofin ketare ta Tarayyar Turai, Kaya Kalas, ta tabbatar da cewa, EU za ta iya sake kakaba takunkumi kan kasar Syria, idan aka samu tabarbarewar lamurra, tana mai nuni da yadda ake cin zarafin fararen hula a gabar tekun Syria.

Kaya Kalas ta shaidawa kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya cewa, “Muna shirye-shiryen mayar da takunkumi kan Syria, idan muka ga tabarbarewar lamurra na ci gaba, inda ta jaddada cewa, dole ne mika mulki ya kasance cikin lumana da kuma hadin kai, kuma dole ne a kare fararen hula a kowane hali.

Ta bukaci dukkan masu ruwa da tsaki na waje da su mutunta hadin kan Syria, da kuma iko da iyakokinta.”

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Kuɗin Cizo ya tilasta rufe fitacciyar sinima a Faransa

Wata fitacciyar sinima a Faransa, Cinematheque Francaise, ta rufe ɗakunan kallonta na tsawon wata guda saboda yaɗuwar kuɗin cizo da aka gano a cikinta

Cibiyar wadda ke gabashin birnin Paris ta ce rufe sinimar zai ba ta damar tabbatar da cewa masu kallo sun samu “aminci da kwanciyar hankali” bayan ƙorafe-ƙorafen da aka yi na cewa ƙwarin suna cizon mutane a lokacin kallon fina-finai.

Tinubu ya sake aike wa majalisa ƙarin sunayen jakadu 32 Dalilin da na koma jam’iyyar ADC — Atiku

A farkon watan Nuwamba, wasu daga cikin masu kallo sun shaida wa kafafen yada labarai cewa ƙwarin sun cije su bayan wani taro da aka yi da shahararriyar ’yar fim ɗin Hollywood, Sigourney Weaver.

Wani daga cikinsu ya ce an ga kuɗin cizon yana yawo a kujeru da kuma jikin tufafi.

Cinematheque ta bayyana cewa za a cire dukkan kujerun ɗakunan kallo, a kuma bi su da busasshen tururi mai zafin digiri 180 a ma’unin selshiyus. Haka kuma kafet da sauran wurare za su sami irin wannan tsaftacewa.

Duk da rufewar ɗakunan kallo huɗu, sauran sassan ginin cibiyar za su ci gaba da aiki, ciki har da wani baje kolin da ake yi game da fitaccen ɗan wasan Amurka, Orson Welles.

A shekarar 2023, Faransa ta fuskanci yaɗuwar kuɗin cizo a manyan birane, musamman a gidajen sinima, asibitoci da motocin jama’a, lamarin da ya ta da hankalin jama’a kafin Gasar Olympics ta Paris 2024.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan 164
  • Tawagar ECOWAS Ta Bar Guinea – Bissau bayan da shugaban kasar yayi barazanar korarsu Da Karfi
  • Sarkin Musulmi ya buƙaci gwamnonin Arewa suke saurarar ƙorafin jama’a
  • Najeriya Ta Kara Ƙaimi Wajen Kawar da Cutar HIV Nan da 2030
  • ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Garin Eruka Na Jihar Kwara
  • Lebanon: Wasikar Kungiyar Hizbullah Ga Paparoma
  • An sake zabar Eto’o a matsayin Shugaban Hukumar kwallon kafa ta Kamaru  
  • Kuɗin Cizo ya tilasta rufe fitacciyar sinima a Faransa
  • Tinubu ya sake aike wa majalisa ƙarin sunayen jakadu 32
  • Iran A Shirye Take Ta Maida Martani Mai Kan Kan Duk Wata Barazanar Tsaro