HausaTv:
2025-07-12@07:33:56 GMT

Kungiyar Tarayyar Turai ta yi barazanar sake kakaba wa Syria takunkumi

Published: 12th, March 2025 GMT

Jami’ar kula da manufofin ketare ta Tarayyar Turai, Kaya Kalas, ta tabbatar da cewa, EU za ta iya sake kakaba takunkumi kan kasar Syria, idan aka samu tabarbarewar lamurra, tana mai nuni da yadda ake cin zarafin fararen hula a gabar tekun Syria.

Kaya Kalas ta shaidawa kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya cewa, “Muna shirye-shiryen mayar da takunkumi kan Syria, idan muka ga tabarbarewar lamurra na ci gaba, inda ta jaddada cewa, dole ne mika mulki ya kasance cikin lumana da kuma hadin kai, kuma dole ne a kare fararen hula a kowane hali.

Ta bukaci dukkan masu ruwa da tsaki na waje da su mutunta hadin kan Syria, da kuma iko da iyakokinta.”

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Ba lallai matatun man gwamnati su sake aiki ba har abada a Najeriya – Ɗangote

Shugaban rukunin kamfanonin Dangote, Alhaji Aliko Ɗangote, ya ce yana da shakku a kan ko matatun mai mallakin gwamnatin Najeriya za su ƙara aiki a nan gaba.

Najeriya dai na da matatun mai guda hudu mallakinta a biranen Fatakwal da Warri da Kaduna.

Amma attajirin ya ce matatun man waɗanda ke ƙarƙashin kulawar Kamfanin Mai na Najeriya (NNPCL), sun laƙume sama da Dalar Amurka biliyan 18 wajen gyaransu, amma har yanzu sun ƙi aiki.

Sojoji sun kashe ’yan fashin daji masu yawan gaske a Zamfara Muna so a kafa doka ta bincikar yadda ’yan Nijeriya ke tara dukiya — EFCC

Ɗangote ya bayyana hakan ne ranar Alhamis lokacin da ya karɓi baƙuncin mambobin shugabannin kamfanoni wadanda ke Karatu a Lagos Business School, a rangadinsu a matatar Dangote da ke Legas.

‎Ya ce matatar man shi mai ƙarfin tace ganga 650,000 a kullum yanzu kusan kaso 50 na aikinta a kan tace man fetur ne, yana mai cewa hatta matatun man gwamnati kaso 22 na karfinsu suke sakawa a harkar tace man fetur ɗin.

A cewar attajirin na Afirka, “Mun taɓa sayen matatun man Najeriya daga hannun tsohon Shugaban Kasa Olusegun Obasanjo a watan Janairun 2007.

“Amma lokacin da marigayi Shugaban Kasa Umaru Yar’aduwa ya zo, tsofaffin manajojin matatun sai suka ce masa an sayar da matatun a ƙasa da ainihin ƙimar su a kasuwa, Obasanjo ya ba mu kamar kyauta ne kawai lokacin da zai tafi. Dole sai da muka mayar da su saboda an samu canjin gwamnati.

‎“A lokacin, manajojin matatun sun shaida wa Yar’aduwa cewa matsayin za su tashi, kawai ƙanin kyauta Obasanjo ya ba mu lokacin da zai tafi.

“Yanzu haka maganar da ake yi, an kashe sama da Dala biliyan 18 wajen gyaran su, amma har yanzu ba sa aiki. Kuma ba na tunani, ina da kokwanto a kan yiwuwar sake aikinsu a nan gaba,” in ji shi.

‎Dnagote ya kwatanta ƙoƙarin da ake yi na gyara matatun da na mutumin da ke kokarin zamanantar da motar da ya saya sama da shekaru 40 da suka wuce ne, alhalin zamani ya riga ya wuce wajen.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ba lallai matatun man gwamnati su sake aiki ba har abada a Najeriya – Ɗangote
  • Bafarawa Ya Kaddamar Da Kungiyar Hada Kan Arewa Da Samar Da Zaman lafiya A Kaduna 
  • Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ya Yi Allah  Wadai Da Kakaba Takunkumi Kan Jami’ar Majalisar Dinkin Duniya
  • Shugaban Kasar Iran Yace Huldar kasar Iran Da IAEA Zai Ci Gaba Ne Idan Ta Daina Fuska Biyu
  • Majalisar Limaman Turai Ta Nesanta Kanta Daga Wadanda Su Ka Ziyarci HKI
  • Somaliya: Kungiyar Al-Shabab Ta Kai Wa Barikin Soja Hari A Birnin Magadishu
  • Trump Ya Kakabawa Wata Jami’in MDD Takunkumi Bayan Ta Fallasa Laifukan HKI Da Hannun Amurka A Ciki
  • 2027: Idan ADC na son lashe zaɓe dole ta bai wa ɗan Arewa takara — Okonkwo
  • Kazem Sajjadpour Ya ce: Iraniyawa Suna Daukan Tarayyar Turai Ma Goyon Bayan Harin Zaluncin Isra’ila Kansu
  • Kwanan nan gwamnati za ta sake kara kudin lantarki a Najeriya – Minista