HausaTv:
2025-03-15@23:10:27 GMT

Ukraine ta amince da yarjejeniyar tsagaita wuta ta kwanaki 30

Published: 12th, March 2025 GMT

Kasar Ukraine ta bayyana aniyarta ta amincewa da shawarar da Amurka ta gabatar, game da dakatar da bude wuta nan take tsakaninta da Rasha har tsawon kwanaki 30, biyowa bayan fara tattaunawa da tawagar Amurka a birnin Jeddah na kasar Saudiyya.

Wata sanarwar hadin gwiwa tsakanin wakilan Ukraine da na Amurka da aka fitar a jiya Talata ce ta tabbatar da hakan, bayan sassan biyu sun shafe sa’o’i suna tattaunawa.

Sanarwar ta ce akwai yiwuwar tsawaita yarjejeniyar, kuma Amurka za ta tuntubi Rasha kasancewar amincewarta zai tabbatar da cimma nasarar matakin.

Baya ga hakan, Amurka ta amince da dage matakin dakatar da musayar bayanan sirri, kuma za ta ci gaba da baiwa Ukraine tallafin tsaro, yayin da kuma sassan biyu suka tattauna kan muhimmancin aiwatar da matakan samar da tallafin jin kai, musamman a wa’adin tsagaita bude wutar.

Har ila yau, masu shiga tsakanin sun amince da samar da tawagogin da za su fara tattaunawa, da nufin cimma nasarar wanzar da zaman lafiya mai dorewa.

 A daya hannun kuma, Amurka ta jaddada aniyarta ta hawa teburin shawara da Rasha, yayin da Ukraine ta jaddada muhimmancin shigar sauran abokan hulda na Turai cikin tsarin na cimma daidaito.

Bugu da kari, jagororin Ukraine da na Amurka, sun amince da gaggauta kaiwa karshen cikakkiyar yarjejeniyar bunkasa cin gajiya daga muhimman ma’adanan Ukraine, ta yadda za a kai ga fadada tattalin arzikin kasar. 

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Dokokin Jihar Kano Ta Amince Da Nada Kwamishina

Majalisar dokokin jihar Kano ta wanke Arc. Ibrahim Yakubu Adamu a matsayin kwamishina kuma mamba a majalisar zartarwa ta jiha.

 

 

A yayin aikin tantance kwamishinonin, ya jaddada mahimmancin kiyaye babban tsarin ga birane da yankunan karkara.

 

Ya kuma yi alkawarin bayar da gudunmowarsa wajen sauke nauyin da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya dora masa.

 

Adamu wanda a baya ya taba rike mukamin Manajan Darakta na Hukumar Kula da Tsare-Tsare Birane ta Jihar Kano (KNUPDA), ya bayyana jin dadinsa ga majalisar a yayin zaman majalisar.

 

Shugaban majalisar Jibril Ismail Falgore ya bukaci Adamu da ya kara samun nasarori a KNUPDA tare da yi masa fatan Alheri a sabon mukaminsa.

 

Nadin Adamu ya yi daidai da ikon da tsarin mulki na Gwamna Yusuf ya ba shi na nada ‘yan majalisar zartarwa ta jiha.

 

KHADIJAH ALIYU

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Araghchi : Iran a shirye take ta shiga tattaunawa da Turawa bisa mutunta juna
  •  Rasamani: Asarar Yakin HKI Ta Kai Dalar Amurka Biliyan 14
  • Dangote Da NNPCL Sun Koma Teburin Tattaunawa Kan Cinikin Danyen Mai A Kan Naira
  • HKI Tana Cigaba Da Keta Tsagaita Wutar Yaki A Lebanon
  • Araqchi: Iran ta karbi Wasikar Trump kuma tana yin nazari a kanta
  • Shugaba Vladimr Putin Na Kasar Rasha Ya Amince Da Tsagaita Wuta A Yakin Ukraine
  • Ukraine Ta Amince Da Tsagaita Wuta Na Wata Guda Da Rasha
  • Majalisar Dokokin Jihar Kano Ta Amince Da Nada Kwamishina
  • Jagora : kiran Trump, na tattaunawa Da Iran yaudarar duniya ne
  • Rasha  na goyon bayan sake farfado da yarjejeniyar nukiliyar Iran