Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [3]
Published: 11th, March 2025 GMT
Wannan magana ta al-imam Ibnu Juzai tana bayani ne kan abubuwa huɗu da ke hana mutum bin Allah da kuma yadda za a magance kowanne daga cikinsu. Ga ƙarin haske akan haka:
1. Shaiɗan: Shaiɗan shi ne abokin gaban mutum na ƙoli tun daga haihuwarsa har mutuwarsa. A matsayinsa na maƙiyi, burinsa shi ne ya ɓatar da mutum daga bin Allah.
Maganin Shaiɗan: Babban maganin Shaiɗan shi ne neman tsari da kariya a kansa a wurin Allah, da sɓa masa, Wato mutum ya yi ƙoƙarin yin akasin abin da Shaiɗan ke umarta. Idan Shaiɗan yana kiran mutum zuwa ga zunubi, ya yi ƙoƙarin kaucewa.
2. Son Zuciya: Zuciyar mutum tana da buƙatu da sha’awa, kuma tana iya karkatar da shi daga tafarkin gaskiya. Idan mutum bai kula ba, zuciyarsa za ta janyo masa son abin da bai dace ba, ko kuma nuna ƙyama ga abin da Allah ya shar’anta wanda hakan zai kai mutum da barin Allah da addinsa. Don haka; dole ne mutum ya kula da gyaran zuciyarsa.
Maganin Son Zuciya: Maganin son zuciya shi ne mutum ya fi ƙarfin ta, Wato mutum ya tilasta wa zuciyarsa bin gaskiya, ko da kuwa tana son akasin haka. Tanƙwara ta ta bi gaskiya, yana nufin horar da zuciya kan gaskiya da bin umurnin Allah. Hakan na faruwa ne ta hanyar tilasta wa kai yin biyayya, ta hanyar salla da azumi, da ambaton Allah, da kasancewa cikin kyawawan ayyuka tare da addu’a Allah Ya tsarkake ta.
3. Duniya: Duniya tana da ruɗi da ƙawanyar ƙyaleƙyale, tana janyo hankalin mutum zuwa ga jin daɗi kamar samun dukiya, ko matsayi, da sauran abubuwan da ke iya karkatar da shi daga bin Allah. Allah ya bayyana cewa duniya ruɗi a wurare daban-daban a cikin Alƙur’ani, hakanan Hadisai masu yawa sun yi bayani a kan ruɗin da duniya take yi wa mutane.
Maganin Duniya: Guje wa ƙyaleƙyalenta da ruɗinta, Wato mutum ya fahimci cewa duniya ba ta da daraja idan aka kwatanta da lahira, kuma bai kamata ya jefa kansa cikin ruɗinta ba, domin ba ta da tabbas. Mutum ya kasance mai tsoron Allah da ƙoƙarin bin dokokinsa a kowane hali.
4. Halittu (Mutane): Mutane na iya zama sanadin da zai hana mutum bin Allah, musamman idan yana koyi da su a kan abin da ba daidai ba. Akwai waɗanda za su janyo mutum cikin halayen banza ko su hana shi aikata alheri, ta yadda hakan zai lalata masa zuciya, domin zama da maɗaukin kanwa yana kawo farin kai.
Maganin Mutane: Karkata ga Allah Shi kaɗai, wato mutum ya yi ƙoƙarin maida hankalinsa ga Allah kaɗai, ba wai ya dogara da mutane ko kuma ya dinga yin abubuwa don faranta musu ba. Hakanan mutum ya nilisanci biyayya ga mutane idan a cikin abin da yake ɓata; Idan mutane suna jagorantar mutum zuwa ga ɓarna, ya kamata ya guje musu.
Zaɓar abokai nagari yana taimaka wa mutum wajen zama nagari. Ya zaɓi waɗanda za su taimaka masa wajen bin Allah, ba waɗanda za su janye shi zuwa ga halaka ba.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Abu Razina Nuhu Ubale Paki
এছাড়াও পড়ুন:
Bidiyon tsiraici: Babiana ta sake jawo ce-ce-ku-ce
A ƙarshen makon da ya gabata ne fitacciyar ’yar TikTok wacce aka fi sani da Babiana ta fitar da wani sabon bidiyo tana rusa ihu tana kira ga Shugaba Bola Tinubu da wasu mawaƙan kudancin Najeriya da su shiga tsakaninta da ’yan Arewa a kan abin da tace suna yi mata na cin zarafi tun bayan bayyanar bidiyo tsiraicinta a shekarar 2024.
Babiana ta yi bidiyon ne cikin harshen Ingilishi inda ta ce ba a yi mata adalci a Arewa kuma ana barazana da rayuwarta.
Sojan Isra’ila ya kashe kansa saboda firgicin yaƙin Gaza Wata bas mai daukar fasinja 56 ta yi hatsari a JosTa bayyana cewa tsawon shekara ɗaya ta yi tana raɓe-raɓe saboda ba ta son maganganun da mutane ke mata tun bayan bayyanar bidiyon tsiraicin nata a soshiyal midiya.
“Ina cikin halin ƙunci da damuwa, ’yan Kudu ku taimaka min Musulman Arewa na son ganin bayana” a cewar Babiana cikin harshen Ingilishi.
Yar TikTok ɗin ta ƙara bayyana cewa tun bayan ɓullar bidiyon tsiraicin nata ta shiga cikin damuwa inda kusan kullum cikin kuka take kwana, kuma har yanzu ’yan Arewa suna mata barazana da bidiyon.
Sabon bidiyo nata ya tayar ƙura, inda wasu ke ganin kalaman nata ba su kamata ba, kuma babu adalci a ciki, kuma ba ta ɗauko hanyar shawo kan matsalar ba.
Nasiru Salisu Zango, sharhi ya yi akan lamarin inda ya ce “ko da yake a cikin bidiyon Babiana ta yi maganganu na ɗora alhaki kan al’ummar Arewa Musulmai wanda hakan rashin adalci ne, amma fa duk da haka akwai buƙatar jan hankalin masu yaɗa bidiyon kan suji tsoron Allah.”
Ya ƙara da cewa “ya kamata a tausaya mata tun kafin ta faɗa wani yanayin na daban, mun sani tana da ’ya’ya da ’yan uwa da wannan yaɗa bidiyon zai iya rikita wa rayuwa.”
Shi kuwa Bilyaminu Ayuba, cewa ya yi ai dama alhaki kuikuyo ne kuma Babiana ba ta ɗauko hanyar da ya kamata ba wajen gyaran wannan matsalar duk da ya bayyana cewa abin da ake matan bai dace ba.
“ A ganina Babiana ba ta ɗauko hanyar gyara matsalar ba saboda shi mutumci madara ne, idan ya zube shi ke nan kuma har yanzu tana son shisshigi da aibanta mutane shi ya sa kullum za a dinga sukar ta da wannan bidiyon nata na marke.
“Idan har tana son zaman lafiya a rayuwarta, to dole ta daina jifa da shisshigi wa mutane, wannan shi ne. Allah Ya sa mu dace.”
Jamilu Sani a nasa ɓangaren cewa ya yi “a cikin lamarinki akwai wa’azi. A baya kece mai yaɗa bidiyon waɗansu idan sun yi irin wannan abin da kika kira kuskure, yau sai Allah Ya kama ki domin ki ji yadda kika jiyar da ’yan uwanki mata marasa tarbiyya da tunanin gobe.”
Ya ƙara da yin kira ga sauran mutane cewa Babiana da ire-irensu marasa “hangen nesa, sun yi aiki marar kyau a ɓoye. Sun yi wa kansu bidiyo, idan suka tuba , tuba na gaske, sai Allah Ya yafe musu.”
Hafsat Muhammed cewa ta yi, “Ita har ta manta duk abubuwan da ta yi wa mutane, kuma har yau ba ta nemi yafiyarsu ba har tana ma kanta kirari da ‘Queen of Update.’”
Abdulwahab Sa’id Ahmad a shafinsa na Facebook wallafawa ya yi cewa: “Wanda yake da cutar Depression ba shi yake ganewa ba sai dai a gane masa.
“Mahaukaci bai san yana hauka ba sai dai a ba shi labari bayan ya warke
“Ki bar nunawa cewa Musulmi sun yi watsi da ke da ’yan Arewa, ke ce ki ka zaɓi ki zauna a yadda ki ke.”