Tawagar Majalisar Dinkin Duniya na rangadi a wuraren da aka aikata kisan kiyashi a Syria
Published: 10th, March 2025 GMT
Rahotanni daga kasar Syria na cewa wata tawagar Majalisar Dinkin Duniya ta shiga birnin Jableh da ke yankin Latakia na kasar Siriya a karon farko a daren jiya Lahadi, kamar yadda wata majiya ta kasar ta shaida wa Al Mayadeen.
Tawagar ta Majalisar Dinkin Duniya sun zagaya a unguwannin Jableh, inda suka duba shaguna da gidajen jama’a da aka wawushe da kuma wadanda aka kona.
Wannan dai na zuwa ne bayan wani tashin hankali da ya barke a yammacin kasar ta Syria, inda aka ga wasu dauke da makamai masu alaka da ma’aikatar tsaron sabuwar gwamnatin kasar ta Syria da kuma dakarun tsaron cikin gida a cikin faifan bidiyo suna aikata munanan laifukan yaki da suka hada da kisan fararen hula da rana tsaka.
Tun bayan da gamayyar kungiyoyi masu dauke da makamai karkashin inuwar kungiyar Tahrir Sham mai alaka da kungiyar alkaida suka hambarar da gwamnatin Bashar Assad, suka fara aiwatar da kisa a bainar jama’a a kan tsiraru, bisa zargin cewa suna dad a alaka da gwamnatin Assad, amma lamarin ya kara tsanata a cikin ‘yan kwanakin nan.
Sakamakon tashin hankalin, an kashe ‘yan kasar Syria sama da 1,018, wadanda akasarinsu fararen hula ne, da suka hada da mata da kananan yara, a cewar wani rahoto da kungiyar kare hakkin bil’adama ta Syrian Observatory for Human Rights (SOHR) ta fitar, amma wasu bayanai daga bakunan mazauna yankunan da abin ya faru na nuni da cewa adadin ya zarta haka.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Gombe ta bai wa alƙalai da Khadi-Khadi kyautar sabbin motoci 16
Gwamnatin Jihar Gombe ta raba sabbin motoci ƙirar SUV guda 16 ga Alƙalai na Babbar Kotu da Khadi-Khadi na Kotun Shari’a domin taimaka musu wajen gudanar da aikinsu yadda ya kamata a fadin jihar.
Motocin sun haɗa da motoci biyu ƙirar Toyota SUV samfurin 2025 da aka bai wa babban alƙal8 da Grand Khadi.
Na kusa komawa APC – Gwamnan Taraba Tsohon Minista Kabiru Turaki ya zama sabon shugaban PDP na ƙasaMotocin guda 14 ƙirar GAC SUV samfurin 2025 da aka raba wa sauran alƙalai da khadi-khadi.
Da yake miƙa motocin, Mataimakin Gwamna Mannasah Daniel Jatau, ya ce gwamnatin Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya na ƙoƙari wajen samar da kayan aiki na zamani domin inganta ayyukan gwamnati, musamman a ɓangaren shari’a.
Ya ce gwamnati na magance matsalolin da ta gada, ciki har da biyan fansho da biyan albashi a kan lokaci.
Ya kuma yi kira ga waɗanda aka bai wa motocin da su yi amfani da su wajen gudanar da ayyukansu.
A nasa jawabin, Kwamishinan Kuɗi, Muhammad Gambo Magaji, ya bayyana cewa an kashe sama da Naira biliyan biyu wajen sayen motocin.
Ya ce tsawon sama da shekaru 10 ɓangaren shari’a bai samu sabbin motocin aiki ba.
Kwamishinan Shari’a, Barista Zubair Muhammad Umar, ya ce rabon motocin wani ɓangare ne na cika alƙawarin gwamnati na inganta ɓangaren shari’a.
Ya tunatar da cewa aikin gina sabon ginin Babbar Kotu na kimanin Naira biliyan 16 na ci gaba da gudana.
A jawabinsa na godiya, Babban Magatakardar Babbar Kotu, Barista Bello Shariff, ya yaba wa gwamnatin jihar bisa goyon bayan da ta ke bai wa bangaren shari’a.
Ya bayyana cewa za su yi amfani da motocin ta hanya mai kyau domin inganta ayyukansu.