Rahotanni daga kasar Syria na cewa wata tawagar Majalisar Dinkin Duniya ta shiga birnin Jableh da ke yankin Latakia na kasar Siriya a karon farko a daren jiya Lahadi, kamar yadda wata majiya ta kasar ta shaida wa Al Mayadeen.

Tawagar ta Majalisar Dinkin Duniya sun  zagaya a unguwannin Jableh, inda suka duba shaguna da gidajen jama’a da aka wawushe da kuma wadanda aka kona.

Wannan dai na zuwa ne bayan wani tashin hankali da ya barke a yammacin kasar ta Syria, inda aka ga wasu dauke da makamai masu alaka da ma’aikatar tsaron sabuwar gwamnatin kasar ta Syria da kuma dakarun tsaron cikin gida a cikin faifan bidiyo suna aikata munanan laifukan yaki da suka hada da kisan  fararen hula da rana tsaka.

Tun bayan da gamayyar kungiyoyi masu dauke da makamai karkashin inuwar kungiyar Tahrir Sham mai alaka da kungiyar alkaida suka hambarar da gwamnatin Bashar Assad, suka fara aiwatar da kisa a bainar jama’a a kan tsiraru, bisa zargin cewa suna dad a alaka da gwamnatin Assad, amma lamarin ya kara tsanata a cikin ‘yan kwanakin nan.

Sakamakon tashin hankalin, an kashe ‘yan kasar Syria sama da 1,018, wadanda akasarinsu fararen hula ne, da suka hada da mata da kananan yara, a cewar wani rahoto da kungiyar kare hakkin bil’adama ta Syrian Observatory for Human Rights (SOHR) ta fitar, amma wasu bayanai daga bakunan mazauna yankunan da abin ya faru na nuni da cewa adadin ya zarta haka.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Radda Ya Sanya Hannu Kan Kasafin 2026 Ya Zama Doka

Daga Isma’il Adamu 

Gwamna Dikko Radda na Jihar Katsina ya sanya hannu kan kudirin kasafin kudin jihar na 2026 na Naira Biliyan 897, makonni uku bayan gabatar da shi a gaban majalisar dokokin jihar.

Yayin rattaba hannu a Fadar Gwamnati da ke Katsina, a gaban ‘yan majalisar dokokin jihar, gwamnan ya jinjinawa majalisar bisa gaggawar amincewa da kasafin, tare da tabbatar da cewa za a aiwatar da shi yadda ya dace.

Ya bayyana cewa kashi 82 cikin ɗari na kasafin an ware shi ne ga manyon ayyuka(capital expenditure), yayin da kashi 18 cikin ɗari aka ware ga ayyukan yau da kullum(recurrent expenditure), rabo wanda ya ce ya fi abin da doka ta baya ta tanada, wadda ke bukatar kada kudaden gudanarwa su haura kashi 30 cikin ɗari.

Gwamna Radda, wanda ya bayyana kasafin a matsayin “kasafin jama’a,” ya ce an tsara shi ne daga shawarwarin da aka tattara a tarukan jin ra’ayin jama’a da aka gudanar a fadin kananan hukumomi 34 na jihar.

Yayin da yake jinjinawa ‘yan majalisar dokokin jihar bisa kyakkyawar alakar aiki da suke da ita da bangaren zartarwa, gwamnan ya bukaci kwamitocin majalisar su gudanar da aikinsu na sa ido don tabbatar da cewa an aiwatar da kasafin yadda ya kamata.

Tun da farko, yayin mika kudirin kasafin domin rattaba hannu, Shugaban Majalisar Dokokin Jihar, Alhaji Nasir Yahaya, ya ce ‘yan majalisar sun duba tare da amince da kasafin cikin makonni uku, lamarin da ya sanya Katsina ta zama jihar farko da ta samu dokar kasafin kudin shekara ta 2026.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sarakuna sun goyi bayan Gwamnatin Gombe kan yaƙi da cin zarafin mata
  • Portugal ta lashe Kofin Duniya na ’yan ƙasa da shekaru 17 a karon farko
  • Gwamnatin Kano ta nemi a binciki Ganduje kan zargin kalaman ta da hankali
  • Kasashen Qatar Da Jordan Sun Yi Allawadai Da Harin “Isra’ila” A Kasar Syria
  • Isra’ila Na Barazanar Sake Shiga Wani Sabon Yaki Da Kasar Lebanon
  • An Zabi JMI A Cikin Majalisar Zartarwan Ta Hukumar Yaki Da Makaman Guba Ta Duniya CWC
  • Gwamna Radda Ya Sanya Hannu Kan Kasafin 2026 Ya Zama Doka
  • Tinubu ya aike wa Majalisar Dattawa sunayen jakadu
  • Reuters: Kungiyar Likitoci Ba Da Iyaka Ba Ta Fice Daga Asibitin Darfur Bayan Bude Wa Ma’aikatanta Wuta
  • Kotu ta yanke wa mutum 5 hukuncin rataya a Oyo saboda aikata kisan kai