Rahotanni daga kasar Syria na cewa wata tawagar Majalisar Dinkin Duniya ta shiga birnin Jableh da ke yankin Latakia na kasar Siriya a karon farko a daren jiya Lahadi, kamar yadda wata majiya ta kasar ta shaida wa Al Mayadeen.

Tawagar ta Majalisar Dinkin Duniya sun  zagaya a unguwannin Jableh, inda suka duba shaguna da gidajen jama’a da aka wawushe da kuma wadanda aka kona.

Wannan dai na zuwa ne bayan wani tashin hankali da ya barke a yammacin kasar ta Syria, inda aka ga wasu dauke da makamai masu alaka da ma’aikatar tsaron sabuwar gwamnatin kasar ta Syria da kuma dakarun tsaron cikin gida a cikin faifan bidiyo suna aikata munanan laifukan yaki da suka hada da kisan  fararen hula da rana tsaka.

Tun bayan da gamayyar kungiyoyi masu dauke da makamai karkashin inuwar kungiyar Tahrir Sham mai alaka da kungiyar alkaida suka hambarar da gwamnatin Bashar Assad, suka fara aiwatar da kisa a bainar jama’a a kan tsiraru, bisa zargin cewa suna dad a alaka da gwamnatin Assad, amma lamarin ya kara tsanata a cikin ‘yan kwanakin nan.

Sakamakon tashin hankalin, an kashe ‘yan kasar Syria sama da 1,018, wadanda akasarinsu fararen hula ne, da suka hada da mata da kananan yara, a cewar wani rahoto da kungiyar kare hakkin bil’adama ta Syrian Observatory for Human Rights (SOHR) ta fitar, amma wasu bayanai daga bakunan mazauna yankunan da abin ya faru na nuni da cewa adadin ya zarta haka.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Mu’ammalar Al’adu Muhimmin Karfi Ne Na Ciyar Da Bunkasar Wayewar Kan Bil’adama Da Wanzar Da Zaman Lafiyar Duniya

Albarkacin taron ministocin kasa da kasa na tattauna mu’ammalar wayewar kai ta duniya, CGTN ta hada hannu da jami’ar Renmin ta kasar Sin, domin jin ra’ayin al’ummun kasashe 41 da yawansu ya kai dubu 12.

Masu bayyana ra’ayoyin na ganin cewa, mu’ammala, da cudanyar al’adu, da wayewar kai muhimmin karfi ne na ciyar da bunkasar wayewar kan daukacin bil’adama da zaman lafiyar duniya gaba, don haka ne ma darajanta al’adu da magabata suke dora muhimmanci a kanmu, da kirkire-kirkire, na da babbar ma’ana ga zamanantar da al’ummun bil’adama, wanda hakan ya sa shawarar bunkasa al’adun duniya da Xi Jinping ya gabatar, ta samu karbuwa tsakanin sassan kasashe daban-daban, yayin da suke kokarin tinkarar kalubaloli a duniya.

Yayin da aka tabo batun fahimtar alamun al’adun Sinawa, kashi 60.6% daga cikin mutanen da aka jin ra’ayinsu, na mai da batun kirkire-kirkire a gaban komai. A ganinsu kirkire-kirkire a bangaren kimiya na jawo hankulansu matuka. Kazalika, kaso 77.2% daga cikinsu sun fi mayar da matukar hankali kan kimiyar Sin, da yadda ake amfani da ita, fiye da mayar da hankula kan zamantakewar Sinawa, da al’adun gargajiya, da al’adu na zamani na kasar Sin. Dadin dadawa, kaso 81.6% daga cikinsu na ganin cewa, tasirin al’adun Sin sun rika karuwa a duniya, kuma fiye da kashi 80% na matasan da aka ji ra’ayinsu ’yan kasa da shekaru 44, su ma sun amince da wannan ra’ayi. Kana kashi 70.6% na ganin cewa, wayewar kan Sinawa, ta bullo da wata sabuwar hanyar daidaita harkokin duniya. (Amina Xu)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran:  Goyon Bayan Shugaban Gwamnatin Jamus Ga ‘Yan Sahayoniya, Yin Tarayya Ne A Fada Da Iran
  • “Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai
  • Bafarawa Ya Kaddamar Da Kungiyar Hada Kan Arewa Da Samar Da Zaman lafiya A Kaduna 
  • Kamfanonin Jiragen Ruwa Sun Yanke Hulda Da Isra’ila Saboda Matsalar Hare-Haren Kasar Yemen
  • Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ya Yi Allah  Wadai Da Kakaba Takunkumi Kan Jami’ar Majalisar Dinkin Duniya
  • Mu’ammalar Al’adu Muhimmin Karfi Ne Na Ciyar Da Bunkasar Wayewar Kan Bil’adama Da Wanzar Da Zaman Lafiyar Duniya
  •  HKI Tana Cigaba Da Yi Wa Mutanen Gaza Kisan Kiyashi
  • Majalisar Limaman Turai Ta Nesanta Kanta Daga Wadanda Su Ka Ziyarci HKI
  • Somaliya: Kungiyar Al-Shabab Ta Kai Wa Barikin Soja Hari A Birnin Magadishu
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutum 22 Kan Zargin Kisan ‘Yan Ɗaurin Aure A Filato