Aminiya:
2025-06-15@19:22:20 GMT

’Yan bindiga sun yi garkuwa da matashi a Kano

Published: 10th, March 2025 GMT

’Yan bindiga sun yi garkuwa da wani matashi mai shekaru 20, Muhammed Bello a ƙauyen Zakirai da ke Ƙaramar Hukumar Gabasawa ta Jihar Kano.

Aminiya ta ruwaito cewa lamarin ya faru ne yayin da ’yan bindigar suka kai hari a gidan wani mai suna Alhaji Yusha’u Ma’aruf, wanda yake da wani asibiti mai zaman kansa a ƙauyen na Zakirai.

Mun bai wa Akpabio sa’o’i 48 ya dawo da Sanata Natasha — SERAP Ramadan: Abubuwa goma ga ma’aurata

Kazalika, wani ɗan gidan mai suna Abubakar Yusha’u mai shekaru 23 ya samu rauni yayin da ’yan bindigar suka guntule masa yatsa ɗaya a hannunsa na hagu.

Wata majiya ta shaida wa Aminiya cewa lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 2:15 na dare, inda maharan su uku riƙe da bindigogi da adduna suka rufar wa gidan Alhaji Yusha’u.

Kazalika, maharan sun arce da wayoyin hannu da kuɗaɗe da ba a kai ga tantance ko nawa ba ne.

Kakakin rundunar ’yan sandan Kano, Abdullahi Haruna Kiyawa ya tabbatar da faruwar lamarin da bincike ya soma gudana a kansa.

SP Kiyawa ya ce tuni ’yan sanda suka fara farautar ɓata-garin domin ceto matashin da aka yi garkuwa da shi.

Aminiya ta ruwaito cewa, a bayan nan ne ’yan sanda suka kama wasu mutum huɗu da ake zargin ’yan bindiga ne, sannan ta ƙwace makamai da alburusai da kuɗi kimanin naira 1,028,800 a unguwar Hotoro da ke Jihar Kanon.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Jihar Kano mahara

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda mota ta kashe mutum 8 ’yan gida daya bayan dawowa daga yawon Sallah a Kaduna

Wani mummunan hatsarin mota a hanyar Kaduna zuwa Zariya ya yi sanadin mutuwar mutum takwas ’yan gida daya, yayin da wasu mutum biyu ke can kwance a asibiti rai a hannun Allah.

Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne wajen misalin karfe 6:00 na yammacin ranar Litinin a garin Barakallahu da ke kan hanyar Kaduna zuwa Zariya, ana tsaka da bukukuwan Babbar Sallah.

A cewar rahotannin, lamarin ya faru ne lokacin da wata mota da ke tsala gudu ta kwace sannan ta danne mutanen da ke tsaye a gefen hanya bayan dawowarsu daga yawon sallah.

Sojoji sun kashe kasurguman ’yan bindiga 3 a Zamfara Mutum ɗaya ya tsira da ransa cikin 242 a hatsarin jirgin India

A cewar mahaifin mamatan, Malam Jamilu Usman Maiyadi, wata mota kirar GLK Marsandi mai ruwan toka ce ta take iyalan nasa, kuma wani yaro ne yake tuka ta.

Sai da a cewarsa, yaron wanda suka yi ittifakin dan gidan wani fitaccen dan siyasa ne a yankin, ya cika wandonsa da iska bayan faruwar lamarin.

Ya ce, “Mun rasa iyalai takwas ’yan gida daya a rana daya. Daga ciki akwai matata Khadija Umar da ’ya’yana su biyu sai kuma kanne da yayyen matar tawa da kuma wata gwaggonsu, duk sun mutu.

“A jimlance, mutum takwas kenan motar ta take; takwas sun mutu nan take, biyu kuma har yanzu suna asibiti,” in ji shi.

Malam Jamilu ya ce iyalan nasa na tsaye ne a bakin hanya suna jiran su sami motar da za ta kai su gida lokacin da motar ta kwace daga kan titi ta afka musu.

Ya kuma ce, “Tabbas motar na gudun wuce sa’a lokacin faruwar lamarin saboda kafar matata ta yi karayar da ba za a iya gyarawa ba, sannan sai jami’an hukumar kiyaye hadura ne ma daga baya suka gano wasu sassan jikin dana Sadiq,” Malam Jamilu ya fada fuskarsa cike da alhini.

‘Har da mai cikin wata takwas da za ta haifi tagwaye a cikin wadanda suka mutu’

Daga cikin wadanda suka rasu har da Zainab Muhammad wacce ke dauke da juna-biyun wata takwas da za ta haifi tagwaye.

Mijin marigayiyar, Sulaiman Abdulkadir Mai Shinkafa, wanda malamin addini ne a Hayin Rigasa, ya bayyana lamarin a cikin alhini.

Ya ce, “Ta kusa haihuwa. Mun riga mun sayi duk kayan jarirai muna shirye-shiryen haihuwar. Har mun ma sanya wa jariran sunan Hassan da Hussaini. Sannan akwai danmu mai shekara shida mai suna Khalid da aka kashe.

“An take matar tawa, sannan dana sai da muka kankaro namansa da katako kafin a yi musu jana’iza. Abu ne da babu wanda zai yi fatan ya gani a rayuwarsa.”

‘Ko uffan iyalan yaron da ya take mu ba su ce mana ba’

Kamar sauran masu alhinin, Malam Sulaiman ya nuna takaici kan yadda ya ce iyalan yaron da gwamnati sun yi watsi da su ko uffan ba su ce musu ba.

“Babu wani daga cikin iyalan yaron, wanda dan wani fitaccen dan siyasa ne a yankin da ya tuka motar, ko kuma daga gwamnatin jihar Kaduna da ya zo ya yi mana ta’aziyya.

“Ko uffan ba su ce mana ba. hatta mahaifin direban motar bai zo ba, sai ka ce yaruwar iyalan namu ba ta da wani amfani,” in ji shi.

Hukumar Kiyaye Hadura ta Kasa (FRSC) ta tabbatar da faruwar lamarin inda ta alakanta shi da gudun wuce sa’a da kuma kwacewar mota a kan hanyar da ba a jima da dauke ruwan sama ba.

Kwamandan shiyya na hukumar a Kaduna, Tijjani Iliyasu ne ya tabbatar da hakan.

Sai dai ya ce sun mika lamarin zuwa hannun ’yan sanda domin fadada bincike a kai.

Kazalika, duk kokarin wakilinmu na jin ta bakin rundunar ’yan sandan Kaduna da gwamnatin jihar sun ci tura saboda sun ki cewa komai a kai.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Masu ƙwacen waya sun kashe ma’aikacin Jami’ar Northwest a Kano
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 100 a Benuwe
  • Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025
  • An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasu
  • Ambaliya: Gwamnatin Kano ta fara tsaftace magudanan ruwa
  • Ƴansanda Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 2, Sun Ceto Mutane 11 A Delta Da Katsina
  • Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6
  • Hajjin 2025: Yadda Alhazan Nijeriya 7 Suka Rasa Rayukansu A Saudi Arabiya
  • Yadda mota ta kashe mutum 8 ’yan gida daya bayan dawowa daga yawon Sallah a Kaduna
  • Sojoji sun kashe kasurguman ’yan bindiga 3 a Zamfara