An yi cikakken zama na uku na taron shekara shekara na majalisar bada shawarwari kan harkokin siyasar kasar Sin da safiyar yau Lahadi a babban dakin taron al’umma dake birnin Beijing, inda zaunannen memban ofishin siyasa na kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar, wanda kuma shi ne shugaban majalisar bada shawarwari kan harkokin siyasar kasar Sin, Wang Huning ya halarci taron, kana, membobin majalisar guda 14 ne suka gabatar da jawabai.

A jawabinta, mambar majalisar Ge Huijun ta ce, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da wani muhimmin jawabi a wajen babban taron murnar cika shekaru 75 da kafa majalisar bada shawarwari kan harkokin siyasar kasar, jawabin da ya kafa alkabila da samar da babban tushe ga ci gaban harkokin majalisar. Ta ce ya dace membobin majalisar su kara gogewa wajen sauke nauyin aiki, da kara kwarewa a fannonin da suka shafi bada jagoranci ta fuskar siyasa, da bada shawarwari game da ayyukan zamanantar da kasa, da kara tuntuba gami da hidimtawa jama’a, tare kuma da kokarin raya kasa da farfado da al’ummomin kasar. (Murtala Zhang)

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Mutum 3 sun mutum yayin haƙar rijiya a Kano

Wasu mutane uku sun rasu yayin da suke tsaka da aikin yasar rijiya a garin Badume da ke Ƙaramar Hukumar Bichi a Jihar Kano. 

A yayin da suke aikin haƙar rijiya, ɗaya daga cikinsu ya shiga domin yasowa biyu kuma na janyo ƙasar da aka haƙo.

Ana cikin haka igiyar ta tsinke, inda nan take ƙasa ta koma kan dattijon mai shekara 65 da ke haƙar rijiyar.

Hakan ya sa ɗansa mai shekara 20 shiga rijiyar domin fito da shi amma abu ya tura.

A nan ne na ukunsu mai 60 Yakubu Abdullahi shi ma ya shiga domin ceto su, amma duka dai abu ya gagara.

A ƙarshe jami’an Hukumar Kashe Gobara sun yi nasarar ceto su ukun a sume, amma daga baya likita ya tabbatar da rasuwarsu bayan kai su asibiti kamar yadda mai magana da yawun rundunar ya bayyana.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Ta Zama Zakaran  Duniya A Wasan “Taekwondo” Na Masu Shekaru Kasa Da 21
  • Ma’aikatar Ayyuka da Sufuri ta Jigawa Ta Bada Kiyasin Kasafin Kudi na Sama da Naira Biliyan 161
  • Mutum 3 sun mutum yayin haƙar rijiya a Kano
  • Shugaban Majalisar Dattawan Akpabio ya Nemi Sanata Natasha ta Biya Shi Diyyar Biliyan 200
  • Fyaɗe ga ’yar shekara 12 ya ja wa matashi ɗaurin rai-da-rai a Yobe
  • Jigajigan Majalisar Ribas 17 Sun Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC
  • Cikakken jadawalin rukunin Gasar Kofin Duniya ta 2026
  • Ina nan a PDP duk da sauya sheƙar ’yan majalisar Ribas — Wike
  • Kakakin majalisar dokokin Ribas da takwarorinsa 16 sun fice daga PDP zuwa APC
  • Iran Ta Mayar Da Martani Kan Sanarwar Bayan Taron  Majalisar Kasashen Yankin Tekun Fasha