An yi cikakken zama na uku na taron shekara shekara na majalisar bada shawarwari kan harkokin siyasar kasar Sin da safiyar yau Lahadi a babban dakin taron al’umma dake birnin Beijing, inda zaunannen memban ofishin siyasa na kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar, wanda kuma shi ne shugaban majalisar bada shawarwari kan harkokin siyasar kasar Sin, Wang Huning ya halarci taron, kana, membobin majalisar guda 14 ne suka gabatar da jawabai.

A jawabinta, mambar majalisar Ge Huijun ta ce, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da wani muhimmin jawabi a wajen babban taron murnar cika shekaru 75 da kafa majalisar bada shawarwari kan harkokin siyasar kasar, jawabin da ya kafa alkabila da samar da babban tushe ga ci gaban harkokin majalisar. Ta ce ya dace membobin majalisar su kara gogewa wajen sauke nauyin aiki, da kara kwarewa a fannonin da suka shafi bada jagoranci ta fuskar siyasa, da bada shawarwari game da ayyukan zamanantar da kasa, da kara tuntuba gami da hidimtawa jama’a, tare kuma da kokarin raya kasa da farfado da al’ummomin kasar. (Murtala Zhang)

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Abba Kabir Zai Gabatar Da Kudirin Kafin 2026 Ga Majalisar Kano Ranar Laraba

Daga Khadijah Aliyu 

Majalisar Dokokin Jihar Kano ta karɓi wasiƙa daga Gwamna Abba Kabir Yusuf kan gabatar da kasafin kuɗi na shekarar 2026 wanda ya kai Naira tiriliyan 1, irinsa na farko a tarihin jihar.

Za a gabatar da kudurin ne a ranar Laraba, 19 ga watan Nuwamban 2025.

Wasiƙar, wadda Kakakin Majalisar, Alhaji Jibril Isma’il Falgore, ya karanta a zaman majalisar, ta bayyana cewa gabatar da kasafin ya yi daidai da sashe na 121 na Kundin Tsarin Mulkin Tarayyar Najeriya na 1999, wanda aka yi wa gyara.

Gwamna Yusuf ya bayyana cewa yawan kasafin da ya karu sosai na nuna ƙudurin gwamnatinsa na ƙarfafa manyan ayyukan gine-gine, shirye-shiryen sabunta birane, da haɓaka ci gaban zamantakewa da tattalin arziki a fadin jihar Kano.

Shugaban Majalisar ya ce Gwamna Yusuf ya yi bayanin cewa kasafin na 2026 zai mayar da hankali ne kan raya gidaje, aikin gona, ilimi, kiwon lafiya, da tallafawa ƙanana da matsakaitan sana’o’i, domin farfaɗo da tattalin arziƙi da samar da hanyoyin dogaro da kai ga al’ummar Kano.

Da zarar an gabatar da kudirin, za a miƙa kasafin kuɗin zuwa Majalisar Dokokin Jihar Kano domin nazari da amincewa. Idan aka amince da shi, zai kasance kasafin kuɗi na farko mai irin wannan girma da jiha daga Arewa ta gabatar.

Gwamna Yusuf ya sake tabbatar da aniyarsa ta gaskiya, bin ƙa’ida wajen kashe kuɗi, da tabbatar da cewa kowane bangare ya samu tallafi isasshen da zai ba shi damar samar da ingantattun ayyuka ga jama’ar Kano.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An  Cimma Yarjejeniya A Karshen Taron Kare Muhalli Na Duniya A Kasar Brazil
  • Antonio Guterres Ya Kira Yi Kungiyar G 20 Da Su Warware Matsalar Rashin Adalci A Harkokin Kasuwanci
  • An Fitar Da Kudurin Bayan Taron Kungiyar G20 Ba Tare Da Halartar Kasar Amurka Ba
  • An Gabatar Da Jawabin Bayan Taro Na Kungiyar G20 Duk Tare Da Kauracewar Amurka
  • Majalisar Dattawa A Najeriya Ta Bukaci shugaba Tinubu Ya Dauki Sojoji 100,000
  •  Afirka Ta Kudu: Rashin Halartar Amurka Taron G-20 Ba Zai Yi Wani Tasiri Ba
  • Yan Majalisar Dokokin Amurka Sun Sami Rarrabuwar Kai Dangane Da ‘Keshe Kiristoci A Najeriya’
  • Zaman Majalisar Amurka Kan Zargin Kisan Kiristoci A Najeriya
  • Gwamna Abba Kabir Zai Gabatar Da Kudirin Kafin 2026 Ga Majalisar Kano Ranar Laraba
  • China ta ce Ya Kamata A Aiwatar Da Sakamakon Taron Kolin Tianjin Don Inganta Kungiyar SCO