An yi cikakken zama na uku na taron shekara shekara na majalisar bada shawarwari kan harkokin siyasar kasar Sin da safiyar yau Lahadi a babban dakin taron al’umma dake birnin Beijing, inda zaunannen memban ofishin siyasa na kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar, wanda kuma shi ne shugaban majalisar bada shawarwari kan harkokin siyasar kasar Sin, Wang Huning ya halarci taron, kana, membobin majalisar guda 14 ne suka gabatar da jawabai.

A jawabinta, mambar majalisar Ge Huijun ta ce, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da wani muhimmin jawabi a wajen babban taron murnar cika shekaru 75 da kafa majalisar bada shawarwari kan harkokin siyasar kasar, jawabin da ya kafa alkabila da samar da babban tushe ga ci gaban harkokin majalisar. Ta ce ya dace membobin majalisar su kara gogewa wajen sauke nauyin aiki, da kara kwarewa a fannonin da suka shafi bada jagoranci ta fuskar siyasa, da bada shawarwari game da ayyukan zamanantar da kasa, da kara tuntuba gami da hidimtawa jama’a, tare kuma da kokarin raya kasa da farfado da al’ummomin kasar. (Murtala Zhang)

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Mako mai Majalisa za ta kada ƙuri’a kan ƙudurin ƙirƙirar sabbin jihohi

Majalisar Wakilai za ta ƙada kuri’a a ranakun 10 da 11 ga watan Disamba kan muhimman kudurorin gyaran kundin tsarin mulkin 1999, ciki har da kirkirar sabbin jihohi da kafa ’yan sandan jihohi.

Mataimakin Kakakin Majalisar, Benjamin Okezie Kalu, ya sanar da jadawalin a zaman majalisar, inda ya ce tattaunawa kan kudirin sauya kundin tsarin mulki za ta gudana yau da gobe kafin kada kuri’ar mako mai zuwa.

An aiwatar da sauye-sauye a wasu muhimman kwamitocin Majalisar Dattawa Tinubu ya naɗa Janar Christopher Musa sabon Ministan Tsaron Nijeriya

Kalu, wanda shi ne shugaban kwamitin majalisar kan nazarin kundin tsarin mulki, ya bukaci ’yan majalisa su halarci zaman.

Ya shaida wa majalisar kwanan nan cewa kwamitin ya kammala aikin da ake bukata a wannan mataki, kuma yana shirin gabatar da takardun da aka daidaita don a yi la’akari da su.

A farko dai an gabatar da jimillar kudirori 87 da ke neman sauya sassa daban-daban na kundin tsarin mulki.

Kudirorin sun shafi gyaran harkokin zabe da shari’a, ’yan sandan jihohi da batutuwan kudi.

Sai dai bayan jin ra’ayin jama’a a matakin jihohi, taron jin ra’ayin jama’a na kasa a Abuja, tattaunawa da masu ruwa da tsaki da kuma daidaitawa da kwamitin majalisar dattawa kan kundin tsarin mulki, adadin kudirin da za a kada kuri’a ya ragu zuwa kusan 45.

A ranar Litinin, 24 ga watan Nuwamba, kwamitocin majalisar wakilai da na majalisar dattawa kan gyaran kundin sun gudanar da taron hadin gwiwa da kakakin majalisun jihohi a Abuja yayin da tsarin sauya kundin ya shiga matakin karshe.

Kalu da Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Barau Jibrin, sun shaida wa kakakin majalisun jihohi cewa makomar kudirin sauye-sauyen yanzu ta dogara ne da majalisun jihohi bayan majalisar tarayya ta kammala aikinta. Kalu ya ce taron ya nuna matakin karshe kafin fara kada kuri’a.

Muhimman kudirorin da ake son gyarawa

Daga cikin muhimman sauye-sauyen da aka gabatar kirƙirar ’yan sandan jihohi, ware kujeru na musamman ga mata a majalisa, ’yancin tsayawa takara ba tare da jam’iyya ba, karin ayyuka ga sarakunan gargajiya, karfafa ikon majalisar tarayya da ta jihohi wajen kira shugaban ƙasa da gwamnonin jihohi kan harkokin tsaro da sauransu.

Kazalika, wani kudiri na neman sauya kundin domin mayar da gudanar da zaben kananan hukumomi daga hukumar zabe ta jihohi zuwa INEC.

Haka kuma, wani kudiri na neman tabbatar da cewa a kammala dukkan shari’un zabe kafin rantsar da zababbun jami’ai.

Babban kudiri kuma shi ne na neman kafa ’yan sandan jihohi ta hanyar sauya kundin tsarin mulki domin cire su daga jerin dokokin tarayya zuwa jerin dokokin hadin gwiwa.

Masu goyon baya sun ce wannan mataki zai taimaka wajen magance matsalolin tsaro da suka yi yawa kuma suke neman fin ƙarfin ’yan sandan tarayya.

Kallo zai koma majalisun jihohi

Bayan an kammala kada kuri’a, za a tura kudirin da aka amince da su zuwa majalisun jihohi 36 don samun amincewa.

Aƙalla majalisun jihohi 24 (wato kashi biyu bisa uku) dole ne su amince da shi kafin a tura su ga shugaban ƙasa don ya sanya hannu.

Duk kudirin da bai samu amincewar jihohi ba zai mutu nan take.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Taron IMO : Tehran Ta Yi Watsi Da Zarge-zargen Isra’ila Marasa Tushe
  • Amurka ta soke bada mafaka ga ‘yan kasashen Afirka 10
  • Majalisar Dokokin Akwa Ibom ta yi fatali da ƙudurin neman hana cin naman kare
  • Yau Majalisar Dattawa za ta tantance sabon Ministan Tsaro
  • Mako mai Majalisa za ta kada ƙuri’a kan ƙudurin ƙirƙirar sabbin jihohi
  • Nigeria Ta Bai Wa Dan Takarar Shugabancin Kasar Guine Bissau Mafakar Siyasa
  • An Bude Taron Bikin Cika Shakaru 41 Da Kafa Kungiyar Tattalin Arziki Ta ECO A nan Tehran
  • Aljeriya: Taron Kasashen Afirka Kan Amincewa Da Mulkin Mallaka A Matsayin Laifi
  • Lebanon: An Gudanar Da Taron Musulunci da Kiristanci a Beirut tare da halartar Paparoma
  • Yawan Yahudawan Da Suke Ficewa Daga HKI Sun Nininka Har Sau 100%