An Yi Cikakken Zama Na Uku Na Taron Shekara-Shekara Na Majalisar Bada Shawarwari Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin
Published: 10th, March 2025 GMT
An yi cikakken zama na uku na taron shekara shekara na majalisar bada shawarwari kan harkokin siyasar kasar Sin da safiyar yau Lahadi a babban dakin taron al’umma dake birnin Beijing, inda zaunannen memban ofishin siyasa na kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar, wanda kuma shi ne shugaban majalisar bada shawarwari kan harkokin siyasar kasar Sin, Wang Huning ya halarci taron, kana, membobin majalisar guda 14 ne suka gabatar da jawabai.
A jawabinta, mambar majalisar Ge Huijun ta ce, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da wani muhimmin jawabi a wajen babban taron murnar cika shekaru 75 da kafa majalisar bada shawarwari kan harkokin siyasar kasar, jawabin da ya kafa alkabila da samar da babban tushe ga ci gaban harkokin majalisar. Ta ce ya dace membobin majalisar su kara gogewa wajen sauke nauyin aiki, da kara kwarewa a fannonin da suka shafi bada jagoranci ta fuskar siyasa, da bada shawarwari game da ayyukan zamanantar da kasa, da kara tuntuba gami da hidimtawa jama’a, tare kuma da kokarin raya kasa da farfado da al’ummomin kasar. (Murtala Zhang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
AU da MDD, sun karfafa dabarun tabbatar da zaman lafiya da tsaro
Kungiyar tarayyar Afrika da Majalisar Dinkin Duniya sun karfafa kawancensu kan dabarun tabbatar da zaman lafiya, tsaro da kuma ci gaba don magance kalubalen duniya da na yanki yanki.
“Hadin gwiwa tsakanin kungiyoyinmu bai taba kasancewa mafi karfi da muhimmanci fiye da yadda yake a yau ba,” in ji Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya António Guterres.
Wannan sanarwar ta zo ne a karshen taron hadin gwiwa na shekara-shekara na 9 na Tarayyar Afirka da Majalisar Dinkin Duniya, wanda aka gudanar a hedkwatar Majalisar Dinkin Duniya da ke New York a ranar Alhamis, wanda Shugaban Hukumar Tarayyar Afirka, Mahamoud Ali Youssouf, da Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya António Guterres suka jagoranta.
Guterres ya jaddada cewa duniya a halin yanzu tana fuskantar “rikici, tashin hankali, karuwar rashin daidaito, wadannan tasirinsu ake ganinshu sosai a nahiyar Afirka.”
Jami’an biyu sun jaddada cewa hadin gwiwa tsakanin AU da Majalisar Dinkin Duniya muhimmin ginshiki ne na kokarin kasa da kasa na inganta zaman lafiya da kare hakkin dan adam.
Sun nuna damuwa game da yaduwar rikice-rikicen jin kai da ke shafar yankuna da dama.
Babban Sakataren ya bayyana “damuwarsa mai zurfi” game da rahotannin baya-bayan nan na “kisan kiyashi da keta hakkokin dan adam” a Al-Fashir da kuma karuwar tashin hankali a yankin Kordofan na Sudan, tare da gargadi game da karuwar rashin tsaro a yankin Sahel ciki har da Mali, Sudan ta Kudu, Somaliya, Libya, da Jamhuriyar Demokraɗiyyar Kongo.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran ta bukaci duniya ta gaggauta daukar mataki a Sudan November 15, 2025 EU ta bukaci Isra’ila ta dauki mataki don kawo karshen tashin hankali a Yammacin Kogin Jordan November 15, 2025 Amurka Ta Sanar Da Fara Kai Farmakin Soja Mai Sunan ” Mashin Kudu” Akan Yankin Latin November 14, 2025 Ana Samun Kwararar ‘Yan Hijira Daga Mali Zuwa Kasar Cote De Voire November 14, 2025 Unrwa: Fiye Da Gidaje 282,000 “Isra’ila” Ta Rusa A Gaza November 14, 2025 Limamin Juma’a Ya Bukaci Ganin An Kai Karar Donald Trump A Kotunan Duniya November 14, 2025 Iran ce ta farko wajen fitar da dabino a duniya November 14, 2025 Wasu kasashen duniya sun nuna damuwa game da tsarin mulkin bayan yakin Gaza November 14, 2025 Kwamitin Tsaro ya tsawaita wa’adin aikin tawagar MDD a Afrika ta Tsakiya November 14, 2025 Tehran da Ankara sun jaddada muhimmancin zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin November 14, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci