An Yi Cikakken Zama Na Uku Na Taron Shekara-Shekara Na Majalisar Bada Shawarwari Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin
Published: 10th, March 2025 GMT
An yi cikakken zama na uku na taron shekara shekara na majalisar bada shawarwari kan harkokin siyasar kasar Sin da safiyar yau Lahadi a babban dakin taron al’umma dake birnin Beijing, inda zaunannen memban ofishin siyasa na kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar, wanda kuma shi ne shugaban majalisar bada shawarwari kan harkokin siyasar kasar Sin, Wang Huning ya halarci taron, kana, membobin majalisar guda 14 ne suka gabatar da jawabai.
A jawabinta, mambar majalisar Ge Huijun ta ce, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da wani muhimmin jawabi a wajen babban taron murnar cika shekaru 75 da kafa majalisar bada shawarwari kan harkokin siyasar kasar, jawabin da ya kafa alkabila da samar da babban tushe ga ci gaban harkokin majalisar. Ta ce ya dace membobin majalisar su kara gogewa wajen sauke nauyin aiki, da kara kwarewa a fannonin da suka shafi bada jagoranci ta fuskar siyasa, da bada shawarwari game da ayyukan zamanantar da kasa, da kara tuntuba gami da hidimtawa jama’a, tare kuma da kokarin raya kasa da farfado da al’ummomin kasar. (Murtala Zhang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Bankin Ajiya na Jihar Jigawa Ya Karamar Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu
Daga Usman Muhammad Zaria
Majalisar Karamar Hukumar Birnin Kudu ta bada tabbacin hada hannu da bankin ajiya na Savings and Loan na Jihar Jigawa domin habaka tattalin arziki.
Shugaban Karamar hukumar, Dr. Builder Muhammad Uba ya bada wannan tabbaci a lokacin da Manajan bankin, Babandi Isah Gumel ya kai masa ziyara.
Builder Muhammad Uba ya ce karamar hukumar za ta ci gaba da mu’amulla da bankin wajen ganin ma’aikatan wucin gadi na bude asusun ajiya a bankin.
Ya kuma bayyana farin cikinsa kan wannan ziyara da kuma karrama shi da aka yi.
A jawabinsa, Manajan bankin Savings and Loan na Jihar Jigawa, Babandi Isa Gumel, ya ce sun karrama shugaban Karamar hukumar ne bisa daukar ma’aikatan wucin gadi a karamar hukumar ta birnin kudu.
Yace Dr Muhammad Uba ya dauki ma’aikatan da dama a fannin kiwon lafiya da ilimi wato B-health da B-teach da kuma amincewa da yin mu’amulla da bankin.