Kasar Sin Za Ta Kara Albarkatu Da Kudade Domin Tallafawa Samar Da Ayyukan Yi
Published: 9th, March 2025 GMT
Ministar kula da ma’aikata da al’umma ta kasar Sin Wang Xiaoping, ta ce kasar za ta kara albarkatu da kudi domin tallafawa samar da ayyukan yi a bana, a wani yunkuri na gina wani tsarin raya kasa mai samar da ayyukan yi.
Wang Xiaoping ta bayyana haka ne a yau Lahadi, yayin wani taron manema labarai kan yanayin rayuwar jama’a da taro na 3 na Majalisar wakilan jama’ar kasar Sin karo na 14, ya gudanar.
A cewarta, rahoton aikin gwamnati na bana ya tsara tare da kara shirya aiwatar da manufofin raya tattalin arziki da kara zuba kudi wajen bunkasa harkokin da suka shafi jama’a, wanda zai samar da goyon baya mai karfi ga raya tattalin arziki da samar da aikin yi. Ta kara da cewa, bangaren samar da aikin yi na kasar ya fara da kafar dama a bana, kamar yadda alkaluma daga watanni biyun farkon bana suka bayyana.
Har ila yau yayin taron, Lei Haichao, shugaban hukumar kula da lafiya ta kasar Sin ya ce matsakaicin tsawon rayuwa a kasar ya kai shekaru 79 a shekarar 2024, karuwar kaso 0.4 idan aka kwatanta da 2023. Ya ce wannan nasara ta zarce abun da aka yi tsammanin samu a cikin rahoton raya kasa karo na 14 tsakanin 2021-2025, kuma an cimma nasarar kafin lokacin da aka tsara. Haka kuma ya nuna cewa kyakkyawar al’adar gargajiya ta kasar Sin da yanayin rayuwa mai aminci da aiwatar da jerin dabaru kamar na shawarar inganta kiwon lafiya a kasar Sin da bada fifiko ga raya bangaren kiwon lafiya, sun yi tasiri kai tsaye kan ingantuwar lafiyar al’umma. (Fa’iza Mustapha)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Hajjin 2025: Jihohi 11 sun kashe N6.2bn wajen tallafa wa Alhazai
Aƙalla jihohi 11 na Najeriya sun kashe sama da Naira biliyan 6.2 wajen tallafa wa Alhazansu domin sauƙaƙa musu wajen zama a ƙasar Saudiyya yayin gudanar da aikin Hajjin 2025.
Wannan tallafi ya haɗa da kuɗi, jakunkunan tafiya, da kuma sayen raguna na hadaya domin sallar Layya.
Tattalin arzikin Nijeriya zai haɓaka cikin shekaru uku masu zuwa — Bankin Duniya Dalilin da babu abin da gwamnatin NNPP ta taɓuka a Kano — APCGwamnatin Jihar Sakkwato ce ta fi kowa bayar da tallafi mafi yawa, inda Gwamna Ahmed Aliyu, ya bai wa kowane daga cikin alhazai 3,200 na jihar Riyal 1,000 (kimanin Naira 450,000).
A Kano kuwa, kowane alhaji daga cikin alhazai 3,345 sun samu kyautar Riyal 50.
Gwamnatin Jihar Legas ta bai wa kowane daga cikin alhazai 1,315 Riyal 180 (kimanin N74,870), yayin da Jihohin Jigawa da Kebbi suka bayar da mafi ƙarancin adadi.
Wani jami’in Gwamna Sanwo-Olu ya bayyana cewa: “Kowane Alhaji ya samu Riyal 180 a matsayin kyauta don sauƙaƙa rayuwarsu a lokacin aikin hajji.”
Jihar Borno ba ta bayar da kuɗi ba, amma ta biya kuɗin ragunan layya (hadaya) na Alhazan jihar guda 2,174.
Haka kuma, hukumomin Kano sun sanar da cewa kowane Alhaji zai samu babbar jakar tafiya domin dawowarsa gida cikin sauƙi.
Sai dai masana da malamai sun soki irin wannan kashe-kashen kuɗi da gwamnati ke yi, inda suka bayyana hakan a matsayin almubazzaranci da rashin fifita abin da ya fi muhimmanci.
Farfesa Yahaya Tanko, masani a harkokin siyasa, ya ce: “Wannan ba fifiko ba ne. Ya kamata gwamnoni su mayar da hankali kan matsalolin tsaro da talauci, ba tare da kashe kuɗi kan aikin hajji ba.”
Ya ƙara da cewa: “Al’umma na fama da sace-sace, manoma ba sa iya zuwa gonakinsu, amma gwamnoni na kashe miliyoyi kan aikin Hajji. Wannan ba daidai ba ne.”
Hakazalika, babban malamin addini, Sheikh Fuad Adeyemi, ya ce: “Kuɗaɗen da aka kashe a kan Hajji za a iya amfani da su wajen taimaka wa ‘ya’yan Alhazai su yi karatu. Wannan zai amfanar da iyalai da kuma al’umma gaba ɗaya.”
Mutane da dama a kafafen sada zumunta sun bayyana irin wannan kashe kuɗi a matsayin rashin adalci ga talakawa.
Wasu sun ce aikin Hajji ibada ce da ya kamata mutum ko al’umma su ɗauki nauyinta da kansu, ba gwamnati ba.
Yanzu haka ana ta kira ga gwamnoni da su dawo da hankali kan tsaro, kiwon lafiya, da ilimi domin hakan ne zai amfani mafi yawan jama’a, ba wasu ƙalilan da suka samu damar zuwa aikin Hajji kawai ba.