Mun kama ’yan bindiga da suka yi kutse a Kano — ’Yan sanda
Published: 8th, March 2025 GMT
Rundunar ’yan sandan Kano ta kama wasu mutum huɗu da take zargi ’yan bindiga ne da tarin makamai da kuɗaɗe a hannunsu.
Da yake yi wa manema labarai jawabi, mai magana da yawun rundunar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya ce an cafke ababen zargin ne a ranar 6 ga wannan wata na Maris.
NMDPRA ta ba da lasisin gina sabbin matatun mai 3 a Nijeriya Dalilin da muka dakatar da Sanata Natasha — Majalisar DattawaSP Kiyawa ya ce an kama ababen zargin ne da kimanin naira 1,028,800 a gidan mai na Chula da ke unguwar Hotoro suna ƙoƙarin sayen bindigar AK-47.
Sanarwar ta ce an samu mutanen huɗu waɗanda dukkansu matasa ne da wasu ƙananan bindigogi ƙirar gida, da wuƙaƙe da adduna da wayoyin hannu da wasu layu.
Ya bayar da sunayen matasan da ke hannu da suka haɗa da — Shukurana Salihu mai shekaru 25 da Rabi’u Dahiru mai shekaru 35 da Ya’u Idris mai shekaru 30 duk daga Jihar Katsina sai kuma Muktar Sani mai shekaru 30 daga yankin ’Yandodo na unguwar Hotoro da ke Kano.
SP Kiyawa ya ce a halin yanzu ana ci gaba da gudanar da bincike kan ababen zargin da ke tsare a sashen binciken miyagun laifuka na hedikwatarsu da ke Bompoi.
Rundunar ’yan sandan wadda ta ce za a gurfanar da ababen zargin a gaban kuliya da zarar an kammala bincike, ta kuma jaddada ƙudirinta na kawo ƙarshen duk wasu miyagu a faɗin jihar.
Ta kuma miƙa godiya ga al’umma dangane da goyon baya da haɗin kan da take samu a ƙoƙarinta na yaƙi da masu tayar da zaune tsaye.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Jihar Kano Jihar Katsina ababen zargin mai shekaru
এছাড়াও পড়ুন:
Cin hanci da rashawa sun yi ƙatutu a Najeriya — ICPC
Hukumar ICPC ta ce da ana aiwatar da dokokin yaƙi da cin hanci da rashawa yadda ya kamata, da kusan kashi 80 na ’yan Najeriya na ɗaure a gidan yari.
Kwamishinan ICPC na Jihar Kaduna, Sakaba Ishaku ne, ya bayyana haka a wani taron horaswa kan yadda ake kula da amana a ƙananan hukumomi.
Kisan Zariya: Na bar Buhari da Allah — Sheikh El-Zakzaky Najeriya za ta buga wasan sada zumunta da Masar kafin fara gasar AFCON ta 2025Ya ce cin hanci ya yi tasiri sosai a rayuwar ’yan Najeriya, kuma yana haifar da talauci, rikice-rikice, da jinkirta ci gaban ƙasa.
Ya ƙara da cewa yawancin dukiyar da wasu ke taƙama da ita a Najeriya ma da alaƙa da aikata rashin gaskiya, kuma mutane da yawa ba sa son jin batun yaƙi da cin hanci saboda suna jin daɗin aikata shi.
Ishaku, ya soki shugabannin ƙananan hukumomi da ke barin kujerarsu ba tare da sun aiwatar da wani gagarumin aiki ba.
Ya kuma nemi a tsaurara hukunci ga masu satar dukiyar gwamnati, inda ya ce duk wanda ya saci dukiyar jama’a bai kamata a masa hukunci mai sauƙi ba.
Kwamishinan Harkokin Ƙananan Hukumomi na Kaduna, Sadiq Mamman Legas, ya goyi bayan bayanan ICPC.
Ya ce gwamnati ta gyara na’urorin wutar lantarki a wasu yankuna, amma mazauna wajen suka lalata, tare da suka sace wasu.
Ya ce ba za a samu ci gaba ba idan mutane suna lalata dukiyar gwamnati.
Dukkanin jami’an sun yi kira da a ƙara ƙarfafa doka, a kula da ayyukan gwamnati sosai, kuma a wayar da kan jama’a domin rage cin hanci da kare kayayyakin gwamnati.