Mun kama ’yan bindiga da suka yi kutse a Kano — ’Yan sanda
Published: 8th, March 2025 GMT
Rundunar ’yan sandan Kano ta kama wasu mutum huɗu da take zargi ’yan bindiga ne da tarin makamai da kuɗaɗe a hannunsu.
Da yake yi wa manema labarai jawabi, mai magana da yawun rundunar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya ce an cafke ababen zargin ne a ranar 6 ga wannan wata na Maris.
NMDPRA ta ba da lasisin gina sabbin matatun mai 3 a Nijeriya Dalilin da muka dakatar da Sanata Natasha — Majalisar DattawaSP Kiyawa ya ce an kama ababen zargin ne da kimanin naira 1,028,800 a gidan mai na Chula da ke unguwar Hotoro suna ƙoƙarin sayen bindigar AK-47.
Sanarwar ta ce an samu mutanen huɗu waɗanda dukkansu matasa ne da wasu ƙananan bindigogi ƙirar gida, da wuƙaƙe da adduna da wayoyin hannu da wasu layu.
Ya bayar da sunayen matasan da ke hannu da suka haɗa da — Shukurana Salihu mai shekaru 25 da Rabi’u Dahiru mai shekaru 35 da Ya’u Idris mai shekaru 30 duk daga Jihar Katsina sai kuma Muktar Sani mai shekaru 30 daga yankin ’Yandodo na unguwar Hotoro da ke Kano.
SP Kiyawa ya ce a halin yanzu ana ci gaba da gudanar da bincike kan ababen zargin da ke tsare a sashen binciken miyagun laifuka na hedikwatarsu da ke Bompoi.
Rundunar ’yan sandan wadda ta ce za a gurfanar da ababen zargin a gaban kuliya da zarar an kammala bincike, ta kuma jaddada ƙudirinta na kawo ƙarshen duk wasu miyagu a faɗin jihar.
Ta kuma miƙa godiya ga al’umma dangane da goyon baya da haɗin kan da take samu a ƙoƙarinta na yaƙi da masu tayar da zaune tsaye.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Jihar Kano Jihar Katsina ababen zargin mai shekaru
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan bindiga sun sace amarya da ƙawenta 14 a Sakkwato
’Yan bindiga sun shiga garin Chaco da ke Ƙaramar Hukumar Wurno a Jihar Sakkwato, inda suka sace amarya da ƙawayenta guda 14.
Yayin da mutane ke tsaka shagalin bikin auren, sai ’yan bindigar suka afka musu tare da tarwatsa komai.
Mutum 6 sun jikkata a rikici manoma da makiyaya a Jigawa Sojoji sun ceto mutum 7 da ’yan bindiga suka sace a KanoSun shigo garin a ƙafa, inda suka wuce kai-tsaye zuwa gidansu amaryar ba tare da sun taɓa kowa ba.
Wani daga cikin iyayen ƙawayen amaryar ya shaida wa Aminiya cewa ba a tantance adadin waɗanda aka sace ba, amma wasu na cewa 15 ne, wasu kuma na cewa 13, amma amaryar da ’yarsa na cikin waɗanda aka sace.
Ya ce: “’Yata ’yar uwar amaryar ce. Ta zo ne kawai domin taya ’yar uwarta murnar bikinta a Chaco. Ban ɗauka za ta kwana a nan ba, ashe ƙaddara ke jiranta.”
A cewarsa, ’yan bindigar sun shiga garin ne da misalin ƙarfe 12 na daren ranar Asabar.
Sun shiga gidansu amaryar kai-tsaye inda suka yi awon gaba da ita da ƙawayenta.
Yayin da suke barin garin, matasa ’yan sa-kai sun yi ƙoƙarin dakatar da su, inda suka yi artabu, tare da yi wa ɗan ɗan sa-kai a hannu.
Ya ƙara da cewa har yanzu ’yan bindigar ba su tuntuɓi kowa ba domin neman kuɗin fansa.
Ranar Lahadi ita ce ranar da aka tsara domin ɗaura auren amaryar, sannan a kai ta gidan mijinta.
Lamarin tsaro a yankin gabashin Sakkwato na ƙara taɓarɓarewa.
Kakakin rundunar ’yan sandan Sakkwato, Ahmad Rufa’i, bai amsa kiran da aka masa ba, zuwa lokacin haɗa wannan rahoto.