Ramadan: Hisbah ta rufe shagon caca a Kano
Published: 8th, March 2025 GMT
Hukumar Hisbah ta Jihar Kano, ta rufe wani shagon da ake yin caca na zamani, wanda aka fi sani da “betting.
Mataimakin kwamandan hukumar a Kano, Sheikh Mujahideen Aminudeen, ne ya bayyana hakan yayin wani taron manema labarai da ya gudanar a Kano.
Kotu ta yanke wa dillalan ƙwayoyi hukuncin ɗaurin shekaru 95 Kisan malami: Shugabannin Kiristocin Kudancin Kaduna sun yi Allah-wadaiYa ce sun ɗauki wannan mataki ne bisa dokokin Jihar Kano, kuma hukumar ta kai samame wajen kafin ta rufe shagon gaba ɗaya.
Aminudeen ya nuna damuwa kan yadda wasu Musulmai ke shiga harkar caca, musamman a lokacin azumin watan Ramadan.
A watannin baya hukumar ta haramta yin cacar “betting” lamarin da ya sanya ta fara farautar wuraren da ake yin cacar domin rufe su.
An fara aiki da dokokin shari’ar Musulunci a Kano tun shekarar 2000, kamar yadda ake yi a wasu jihohi 11 na Arewacin Najeriya.
Waɗannan dokoki sun haramta caca, karuwanci da shan giya a jihar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ramadan Shari ar Musulunci
এছাড়াও পড়ুন:
Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi
Sun jaddada cewa dole ne manyan kafafen sada zumunta su kare ‘yancin yin magana.
Sun kuma yi kira ga ‘yan Nijeriya, ‘yan jarida, da masu fafutukar kare haƙƙin bil’adama su tashi tsaye don hana abin da suka kira yunƙurin mayar da Nijeriya “mulkin kama-karya a intanet.”
Lamarin ya biyo bayan wa’adin sati guda da DSS ta bai wa Sowore da ya goge wasu wasu rubuce-rubuce game da Shugaba Bola Tinubu, wanda ya ƙi amincewa.
Hakan ya sa hukumar ta shigar da shi ƙara a kotu.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp