Al-Houthi: Mun Baiwa Isra’ila Wa’adin Kwanaki 4 Da Ta Kawo Karshen Killace Gaza
Published: 8th, March 2025 GMT
Jagoran kungiyar Ansar Allah ta kasar Yemen, Sayyed Abdul-Malik al-Houthi, ya baiwa masu shiga tsakani wa’adin kwanaki hudu na tabbatar da shigar da kayayyakin jin kai a Gaza, yana mai gargadin cewa idan har Isra’ila ta ci gaba da toshe hanyoyin kai kayan agaji a Gaza, to dakarun Yemen za su ci gaba da kai hare-hare kan jiragen ruwa masu alaka da Isra’ila.
A cikin wani jawabi da ya yi wanda aka watsa a gidajen talabijin na ciki da wajen kasar Yemen, Al-Houthi ya soki ta’annutin da Isra’ila ke ci gaba da yi wa Falasdinu, yana mai jaddada cewa, rashin aiwatar da yarjejeniyar dakatar da bude wuta da kuma hana shigar da kayan agaji a Gaza da kuma ci gaba da killace yankin da Haramtacciyar Kasar Isra’ila ke yi, lamari ne mai matukar hadari.
Al-Houthi ya zargi Isra’ila da kin yin aiki da alkawuran da ta dauka a karkashin yarjejeniyar tsagaita wutar da aka cimma a kan Gaza, musamman dangane da ayyukan jin kai, yana mai cewa Hamas ta cika dukkanin alkawullanta da kuma sauke nauyin da ya rataya a wuyanta, ta hanyar kiyaye wannan yarjejeniyar.
Har ila yau Al-Houthi ya yi Allah wadai da zafafa hare-haren da Isra’ila ke kai wa a yankunan yammacin gabar kogin Jordan da kuma al-Quds, yana mai bayyana irin rawar da Isra’ila ke takawa wajen kara kai hare-hare kan Falasdinawa a matsayin laifin yaki.
Baya ga haka kuma, Ya soki yadda Amurka ke goyon bayan mamayar Isra’ila ido rufe a karkashin Shugaba Donald Trump, yana mai cewa goyon bayan Washington ya karfafa gwiwar Isra’ila wajen ci gaba da muzgunawa Falasdinawa.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Isra ila ke
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu bai shirya gudanar da sahihin zaɓe ba a 2027 – Buba Galadima
Jigo a jam’iyyar NNPP, Buba Galadima, ya yi zargin cewa gwamnatin Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ba ta da niyyar gudanar da sahihi kuma ingantaccen zaɓe a 2027.
Galadima ya bayyana hakan ne ranar Talata a wata hira da aka yi da shi a shirin Prime Time na gidan talabijin na Arise TV, inda ya ce gwamnatin da jam’iyyar APC ke jagoranta ta kankane cibiyoyin gwamnati don amfaninta.
Gwamnati ta fara duba yara marasa galihu kyauta a asibitin Aminu Kano Tun Tinubu yana Gwamna ba abin da ya fi shahara da shi kamar tara haraji – Adebayo“Wannan gwamnati ba ta shirya gudanar da zaɓen adalci ba. Daga yadda suke tafiyar da al’amura, za ka gane yadda suke tarwatsa jam’iyyun siyasa. Wannan yana nuna cewa ba sa son a samu hamayya a lokacin zaɓe,” in ji shi.
Galadima ya kuma yi gargadi kan shirin nada wani da ya kira mai lam’a a matsayin sabon shugaban Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), yana mai cewa hakan na iya jefa ƙasar cikin rudani.
“Ina fatan ba gaskiya ba ne, domin idan wannan mutumin ya zama shugaban INEC, ka tabbata cewa wannan gwamnati na neman tayar da yaƙin basasa,” in ji shi.
Sai dai bai ambaci sunan mutumin ba.
Dangane da batun fara yaƙin neman zaɓe da wuri da wasu jam’iyyu ke yi, Buba Galadima ya zargi INEC da gazawa wajen aiwatar da tanade-tanaden dokokin zaɓe.
“Wannan batun fara yaƙin neman zaɓe kafin INEC ta ba da izini, gwamnatin da ke kan mulki ce ta fara shi. Wannan yana nuna cewa INEC ba za ta iya zama mai adalci a irin wannan yanayin siyasa da muke ciki ba,” in ji shi.