Jagoran kungiyar Ansar Allah ta kasar Yemen, Sayyed Abdul-Malik al-Houthi, ya baiwa masu shiga tsakani wa’adin kwanaki hudu na tabbatar da shigar da kayayyakin jin kai a Gaza, yana mai gargadin cewa idan har Isra’ila ta ci gaba da toshe hanyoyin kai kayan agaji a Gaza, to dakarun Yemen za su ci gaba da kai hare-hare kan jiragen ruwa masu alaka da Isra’ila.

A cikin wani jawabi da ya yi wanda aka watsa a gidajen talabijin na ciki da wajen kasar Yemen, Al-Houthi ya soki ta’annutin da  Isra’ila ke ci gaba da yi wa Falasdinu, yana mai jaddada cewa, rashin aiwatar da yarjejeniyar dakatar da bude wuta da kuma hana shigar da kayan agaji a Gaza da kuma ci gaba da killace yankin da Haramtacciyar Kasar Isra’ila ke yi, lamari ne mai matukar hadari.

Al-Houthi ya zargi Isra’ila da kin yin aiki da alkawuran da ta dauka a karkashin yarjejeniyar tsagaita wutar da aka cimma a kan Gaza, musamman dangane da ayyukan jin kai, yana mai cewa Hamas ta cika dukkanin alkawullanta da kuma sauke nauyin da ya rataya a wuyanta, ta hanyar kiyaye wannan  yarjejeniyar.

Har ila yau Al-Houthi ya yi Allah wadai da zafafa hare-haren da Isra’ila ke kai wa a yankunan yammacin gabar kogin Jordan da kuma al-Quds, yana mai bayyana irin rawar da Isra’ila ke takawa wajen kara kai hare-hare kan Falasdinawa a matsayin laifin yaki.

Baya ga haka kuma, Ya soki yadda Amurka ke goyon bayan mamayar Isra’ila ido rufe a karkashin Shugaba Donald Trump, yana mai cewa goyon bayan Washington ya karfafa gwiwar Isra’ila wajen ci gaba da muzgunawa Falasdinawa.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Isra ila ke

এছাড়াও পড়ুন:

Ko Mene Ne Dalilin Da Ya Sa Trump Ya Gujewa Yaki Da Yemen Har Ya Kai Ga Fusata Kawayen Amurka

Gujewar da Trump ta yi daga yakin Yemen ya harzuka mahukuntan gwamnatin Isra’ila da kasashen Larabawa da suka dogara da shi

Shafin Jaridar Hill ta Amurka ta buga wani sabon labarin da ke bayyana irin kayen da Amurka ta sha a Yemen da kuma irin dimbin hasarar da Amurkan ta yi domin kare yahudawan sahayoniyya kafin ficewa daga kangin matakin martanin kasar Yemen.

Labarin da Imran Khaled ya rubuta mai taken “(Al’ummar Yemen) sun yi tsayin daka da kuma ja da baya da Trump ya yi… Shin Amurka za ta fice daga Yemen?”, yarjejeniyar “dakatar da kai hare-haren wuce gona da irin Amurka kan Yemen” ta bayyana yadda Amurka ta yin watsi da kawayenta cikin sauki, wanda ke nufin gwamnatin ‘yan sahayoniya.

Ya yi nuni da cewa: Barin harin wuce gona da iri kadai a gaban ci gaba da ayyukan Yemen, yana kara karfafa labarin kasar Yemen da suke gabatar da tallafi da taimako a kodayaushe ga gwamnatocin Larabawa da na Musulunci, da hakan ke fayyace cewa Amurka ba abar dogaro ba ce, kuma cikin sauri ta yi watsi da “kawayenta” wanda hakan ya faru a zahiri bayan ficewar Amurka daga “yakin kare yahudawan sahayoniyya”.

Ya bayyana cewa: Mai laifi Trump ya kwatanta mutanen Yemen a matsayin jarumai da masu juriya, bayan da a baya ya yi barazanar “murkushe su baki daya” ya nuna cewa shugaban na Amurka ya mika wuya tare da ayyana shan kaye, amma yana shelanta cewa ya yi nasara, yana mai jaddada cewa sakamakon yakin ya tabbatar da rashin nasara ga Amurka.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gaza : EU ba ta gamsu da sabon tsarin raba agaji na Amurka da Isra’ila ba  
  •  Falasdinawa Da Dama Sun Yi Shahada A Zirin Gaza
  • Ko Mene Ne Dalilin Da Ya Sa Trump Ya Gujewa Yaki Da Yemen Har Ya Kai Ga Fusata Kawayen Amurka
  • Hukumar Kare Hakkin Bil’adam Ta MDD Ta Bukaci A Kawo Karshen Kissan Kiyashi A Gaza
  •  Fizishkiyan: Wajibi Ne A Kawo Karshen Ta’addanci A Kan Iyakokin Iran Da Pakistan
  • Sojojin HKI Suna Ci Gaba Da Kai Wa Yankunan Gaza Hare-hare
  • Gaza : Spain ta bukaci kasashen duniya su kakabawa Isra’ila takunkumi
  • Falasdinawa 30 sun yi shahada a Wani harin Isra’ila kan wata makaranta
  • Hare-Haren HKI Kan Wata Makaranta A Gaza Ya Kashe Mutane 46 Daga Ciki Harda Yara Kanana
  • Shugaban Shirin  HKI Da Amurkan  Na Raba Kayan Agaji A Gaza Ya Yi Murabus