Aminiya:
2025-06-18@23:33:51 GMT

HOTUNA: Tinubu ya karɓi baƙuncin Shugaban Saliyo a Abuja

Published: 3rd, March 2025 GMT

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya gana da takwaransa na Saliyo Julius Maada Bio a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja.

Ganawar tsakanin shugabannin ƙasashen Afirka biyu ta gudana ne a bayan labule, inda jami’an gwamnati kalilan ne suka halarta.

NLC ta yi fatali da yunƙurin ƙara kuɗin lantarki Hakar ma’adanai: ILO ta horas da masu ruwa da tsaki kan illar bautar da yara

Shugaba Bio ya isa fadar shugaban ƙasa da misalin ƙarfe 12:30 na rana, kuma ya samu tarba daga Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Kasa, Femi Gbajabiamila.

Haka kuma, shugaban na Saliyo ya samu tarba ta ban girma, inda rundunar sojojin shugaban ƙasa suka yi masa fareti tare da kade-kaden gargajiya.

Duk da cewa ba a san ajandar wannan ganawa ba, sai dai Aminiya ta samu cewa ba zai rasa nasaba yunƙurin inganta alaƙar da ke tsakanin ƙasashen biyu ba.

Nijeriya da Saliyo mambobi ne na ƙungiyar raya tattalin arzikin ƙasashen yammacin Afirka da kuma ƙungiyar tarayyar Afrika, kuma sun haɗa kai kan tsare-tsaren da suka shafi samar da zaman lafiya, kwanciyar hankali da ci gaba a yankin.

Nijeriya ta taka rawar gani wajen ayyukan wanzar da zaman lafiya a ƙasashen Afirka da dama musamman Saliyo.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Tarayya Za Ta Kwaso ‘Yan Nijeriya Da Suka Maƙale A Isra’ila Da Iran

Sanarwar ta ƙara da cewa ana aiki tare da hukumomin cikin gida da na ƙasa da ƙasa domin ganin an gudanar da aikin kwasar cikin tsaro.

Sanarwar ta ce: “Ma’aikatar Harkokin Waje na sanar da jama’a cewa, sakamakon rikicin da ke ƙara ƙamari tsakanin Isra’ila da Iran, Gwamnatin Tarayya tana shirin ƙarshe na kwaso ‘yan Nijeriya da suka maƙale a waɗannan ƙasashe.

“Saboda haka, ana shawartar dukkanin ‘yan Nijeriya da abin ya shafa da su kiyaye matakan tsaro da kuma tuntuɓar ofishin jakadanci mafi kusa domin yin rijista da samun ƙarin umarni.”

Baya ga haka, Gwamnatin Tarayya ta sake kira da a dakatar da faɗa tsakanin Isra’ila da Iran, tare da buƙatar ɓangarorin su rungumi tattaunawa, su mutunta dokokin kare haƙƙin ɗan Adam na duniya, kuma su bai wa rayuwar fararen hula muhimmanci.

Ma’aikatar ta jaddada cewa Nijeriya na goyon bayan hanyoyin warware rikici ta hanyar lumana da kuma tallafa wa zaman lafiya a yankuna da duniya baki ɗaya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Najeriya Ya Kaddamar Da Aikin Samar Da Ruwa Da Kamfanin Sin Ya Gudanar A Birnin Abuja
  • HOTUNA: Yadda Tinubu ya ziyarci waɗanda suka jikkata a harin Benuwe
  • Tinubu Ya Kai Ziyara Benuwe Sakamakon Kisan Kiyashi Da Aka Yi Wa Jama’a
  • Sojoji sun raunata shugaban ISWAP na Najeriya, Albarnawi
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Kwaso ‘Yan Nijeriya Da Suka Maƙale A Isra’ila Da Iran
  • Majalisa ta aike wa Tinubu kudurorin dokar haraji domin ya rattaba musu hannu
  • Dalilin Mara Wa Tinubu Baya Ba Tare da Ambaton Shettima Ba – Shugaban APC Na Arewa Maso Gabas
  • Shugaba Xi Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan Kassym-Jomart Tokayev
  • Tinubu zai je jaje bayan kisan fiye da mutum 100 a Benuwe
  • Rundunar Sojin Ruwa Ta Nijeriya Ta Lalata Haramtattun Matatun Mai 5 A Ribas