HOTUNA: Tinubu ya karɓi baƙuncin Shugaban Saliyo a Abuja
Published: 3rd, March 2025 GMT
Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya gana da takwaransa na Saliyo Julius Maada Bio a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja.
Ganawar tsakanin shugabannin ƙasashen Afirka biyu ta gudana ne a bayan labule, inda jami’an gwamnati kalilan ne suka halarta.
NLC ta yi fatali da yunƙurin ƙara kuɗin lantarki Hakar ma’adanai: ILO ta horas da masu ruwa da tsaki kan illar bautar da yaraShugaba Bio ya isa fadar shugaban ƙasa da misalin ƙarfe 12:30 na rana, kuma ya samu tarba daga Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Kasa, Femi Gbajabiamila.
Haka kuma, shugaban na Saliyo ya samu tarba ta ban girma, inda rundunar sojojin shugaban ƙasa suka yi masa fareti tare da kade-kaden gargajiya.
Duk da cewa ba a san ajandar wannan ganawa ba, sai dai Aminiya ta samu cewa ba zai rasa nasaba yunƙurin inganta alaƙar da ke tsakanin ƙasashen biyu ba.
Nijeriya da Saliyo mambobi ne na ƙungiyar raya tattalin arzikin ƙasashen yammacin Afirka da kuma ƙungiyar tarayyar Afrika, kuma sun haɗa kai kan tsare-tsaren da suka shafi samar da zaman lafiya, kwanciyar hankali da ci gaba a yankin.
Nijeriya ta taka rawar gani wajen ayyukan wanzar da zaman lafiya a ƙasashen Afirka da dama musamman Saliyo.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Tinubu Ya Jinjinawa NAFDAC Bisa Matsayin Da Ta Taka A Hukumar Lafiya Ta Duniya
Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya taya Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC) murna bisa ci gaba da riƙe matsayin Maturity Level 3 (ML3) na Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) wajen kula da magunguna da rigakafi.
Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara na Musamman kan Harkokin Bayani da Tsare-tsare, Bayo Onanuga, a cikin wata sanarwa, ya bayyana cewa, an gudanar da binciken sake tantance matsayin WHO daga 28 zuwa 30 ga Mayu, 2025, inda aka kimanta NAFDAC bisa ka’idojin ƙasa da ƙasa.
Hukumar ta fara samun wannan matsayi na ML3 ne a 2022, inda ta zama hukumar farko a Afrika mai kula da ƙasashen da ba sa samar da magunguna da ta cimma wannan nasara.
Wannan sabon tantancewa ya biyo bayan wani binciken ne a watan Nuwamban 2024, tare da gudanar da tarukan duba Shirin Cigaban Cibiyoyi(IDP) guda biyar tsakanin Fabrairu zuwa Afriln 2025 domin tantance matakan gyara. WHO ta yaba wa NAFDAC kan ci gaba da samun tsari mai ƙarfi, da ke aiki yadda ya kamata, tare da yaba wa goyon bayan gwamnati wajen ƙarfafa hukumar.
Shugaba Tinubu ya jinjina wa shugabanni da ma’aikatan NAFDAC bisa ƙwarewa da sadaukarwa, yana mai cewa wannan nasara ta ƙara ɗaukaka matsayin Najeriya a fannin kula da lafiya da shirin kare cututtuka.
Ya ce wannan nasara na daidai da kudirin gwamnatinsa na Renewed Hope Agenda domin sauya tsarin kula da lafiya.
Shugaban ya yi nuni da ci gaba da ake samu, ciki har da inganta cibiyoyin kiwon lafiya na matakin farko 17,000, kyautata kulawa da mata masu juna biyu da na’urorin gano cututtuka a yankunan da ba su da iisassun kayayyakin kula da lafiya, horar da ma’aikatan lafiya 120,000, da kuma ninka yawan masu amfani da shirin inshorar lafiya na ƙasa cikin shekaru uku.
Ya kuma tabbatar da aniyarsa ta ƙarfafa samar da kayayyakin kiwon lafiya a cikin gida da jawo ra’ayin masu zuba jari a fannin lafiya.
Tinubu ya yi alkawarin ci gaba da tallafa wa NAFDAC a yunkurinta na cimma matsayin WHO Maturity Level 4, mafi girma a duniya kan ingancin sarin kula da magunguna.
Daga Bello Wakili