An Yi Jana’izar Shugaban Kasar Namibia Da Ya Samo Mata ‘Yanci
Published: 3rd, March 2025 GMT
A ranar Asabar din da ta gabata ne dai aka yi jana’izar Sam Nujoma wanda shi ne ya samo wa kasar ‘yanci bayan tsawon shekaru na gwgawarmaya.
Mahalarta jana’izar ta Nujoma sun kunshi iyalansa, mata,’ya’yan da jikokin, sai shugabannin kasashen Afirka na da, da masu ci.
A yayin jana’izar an bayyana Nujoma a matsayin wani gwarzo na fada da mulkin mallaka da tsarin wariya da ya kare nahiyar ta Afirka.
Shugaban kasar Namibia mai ci a yanzu ya bayyana Nujoma da cewa; Gwarzo ne da za a rufe shi a cikin makabartar da gwarazan kasar suke kwance. Kuma shi na musamman ne daga cikin ‘ya’yan wannan kasa, sannan kuma dan juyin juya hali.
Mahalarta jana’izar dai sun fito ne daga kowace kusurwa ta kasar Namibia,inda su ka taru a makabartar da ake rufe gwarazan kasar a birnin Waindhoek, domin yin jinjina da ban girma na krshe ga tsohon shugaban kasar wanda ya rasu yana dan shekaru 95.
Nujoma ya yi shugabancin kasar a zango uku daga 1990 zuwa 2005, tare da shimfida zaman lafiya da tsaro a cikin kasar.
An dauki kwanaki 21 ana juyayin rasuwarsa a gwamnatance, tare da yin kasa-kasa da tutar kasar.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025
A cewarsa, ɗalibai 1,367,210 ne suka yi rajistar jarrabawar; maza 685,514 da mata 681,696.
Daga cikinsu, ɗalibai 1,358,339 ne suka rubuta jarrabawar, waɗanda suka haɗa da maza 680,292 da mata 678,047.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp