An Yi Jana’izar Shugaban Kasar Namibia Da Ya Samo Mata ‘Yanci
Published: 3rd, March 2025 GMT
A ranar Asabar din da ta gabata ne dai aka yi jana’izar Sam Nujoma wanda shi ne ya samo wa kasar ‘yanci bayan tsawon shekaru na gwgawarmaya.
Mahalarta jana’izar ta Nujoma sun kunshi iyalansa, mata,’ya’yan da jikokin, sai shugabannin kasashen Afirka na da, da masu ci.
A yayin jana’izar an bayyana Nujoma a matsayin wani gwarzo na fada da mulkin mallaka da tsarin wariya da ya kare nahiyar ta Afirka.
Shugaban kasar Namibia mai ci a yanzu ya bayyana Nujoma da cewa; Gwarzo ne da za a rufe shi a cikin makabartar da gwarazan kasar suke kwance. Kuma shi na musamman ne daga cikin ‘ya’yan wannan kasa, sannan kuma dan juyin juya hali.
Mahalarta jana’izar dai sun fito ne daga kowace kusurwa ta kasar Namibia,inda su ka taru a makabartar da ake rufe gwarazan kasar a birnin Waindhoek, domin yin jinjina da ban girma na krshe ga tsohon shugaban kasar wanda ya rasu yana dan shekaru 95.
Nujoma ya yi shugabancin kasar a zango uku daga 1990 zuwa 2005, tare da shimfida zaman lafiya da tsaro a cikin kasar.
An dauki kwanaki 21 ana juyayin rasuwarsa a gwamnatance, tare da yin kasa-kasa da tutar kasar.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
NAJERIYA A YAU: Tinubu ya yi wa Arewa adalci a ayyuka da mukamai — Bayo Onanuga
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
Kungiyar Tuntuba ta Arewa (ACF) ta zargi Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu da kin yin adalci wurin ayyuka da raba mukamai tsakanin Arewa da Kudancin Kasar nan.
Wadannan zarge-zarge suka sa fadar Shugaban Kasa ta hannun mai taimaka masa na musamman kan kafofin yada labarai Bayo Onanuga mayar da martani ga kungiyar ta ACF.
Ko wadanne irin martani fadar shugaban kasar ta mayar ga kungiyar?
NAJERIYA A YAU: Yadda Za A Dama Da Matan Arewa A Fannin Kimiyya DAGA LARABA: Dalilan al’ummomi na rungumar gwaji kafin aureWannan shi ne batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba a kai.
Domin sauke shirin, latsa nan