MDD ta taya Musulmi murnar zuwan watan Ramadan
Published: 3rd, March 2025 GMT
Sakatare-Janar na Majalisar Dinkin Duniya (MDD), Antonio Guterres, ya taya al’ummar Musulmi murnar zagayowar watan Ramadan, yana mai bayyana wannan lokaci a matsayin mai cike da falala, tausayi, da zaman lafiya.
A sakon da MDD ta fitar ta hannunsa, Guterres ya ce, “Ramadan lokaci ne da ke karantar da kyawawan ɗabi’u na tausayawa, taimakekeniya, karamci, da mutunta juna.
Ya kuma jaddada muhimmancin tunawa da waɗanda suke cikin hali na ƙunci, musamman ’yan gudun hijira da waɗanda ke fama da rikice-rikice a wurare kamar Gaza, Sudan, da yankunan Sahel.
Guterres ya bayyana damuwarsa kan halin da suke ciki, yana mai cewa, “Ina tare da ku a wannan lokaci mai albarka, kuma ina roƙon samun zaman lafiya da kwanciyar hankali a gare ku.”
Ya yi kira ga al’umma da su yi amfani da wannan wata mai alfarma wajen haɗa kai da tabbatar da zaman lafiya.
“Zaman lafiya shi ne ginshiƙin rayuwa, kuma ya kamata mu yi aiki tare don gina duniya mai cike da adalci da mutunta juna,” in ji shi.
Sakatare Janar ɗin ya kuma bayyana cewa a kowanne Ramadan, yana yin azumi tare da al’ummar Musulmi a faɗin duniya, abin da ke ƙara masa fahimtar kyawawan dabi’u na Musulunci da kuma ƙwarin gwiwa.
A karshe, Guterres ya yi fatan Allah Ya karɓi ibadar al’ummar Musulmi yayin da suke azumtar wannan wata mai albarka, yana mai cewa, “Ina taya ku murnar wannan lokaci mai cike da albarka da tausayi.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Guterres Ramadan zaman lafiya
এছাড়াও পড়ুন:
An Kaddamar da Makon MNCH na 2025, Ya Rarraba Fakitin Bayarwa 6,000, Kayan C/S 500
Gwamnatin jihar Kano ta kaddamar da zagayen farko na makon lafiyar mata da jarirai da jarirai (MNCHW) na shekarar 2025 tare da raba fakiti 6,000 na kayan haihuwa da na’urar (C/S) 500 ga cibiyoyin lafiya a fadin jihar.
Gwamna Abba Kabir Yusuf wanda mataimakinsa, Kwamared Aminu Abdussalam Gwarzo ya wakilta shi ne ya jagoranci bikin kaddamar da shirin a hukumance da aka gudanar a cibiyar lafiya matakin farko na Birji da ke karamar hukumar Madobi.
Ya yi nuni da cewa, wannan aikin ya hada da na rigakafi na yau da kullun ga yara, karin sinadarin Vitamin A, Rarraba gidajen sauro masu maganin kwari ga mata masu juna biyu.
Gwamna Yusuf ya jaddada kudirin gwamnatin sa na karfafa wa shirin rabon gidajen sauro ta hanyar ware naira miliyan 140 domin adana gidajen sauro da aka raba.
Gwamnan ya bukaci mata da masu kulawa da su yi amfani da damar da za a yi na tsawon mako guda don samun muhimman ayyukan kiwon lafiya da ake bayarwa kyauta.
A cikin sakon sa na fatan alheri, shugabar ofishin UNICEF a Kano, Mista Rahama Rihood Mohammed Farah, ta yi kira ga gwamnatin jihar da ta kara yawan kwanakin hutun haihuwa da ake biyarwa domin kare lafiyar mata da jarirai da kuma inganta shayar da jarirai nonon uwa zalla.
Taron ya samu halartar kwamishinan lafiya, shugaban karamar hukumar Madobi, Hakimin Shanono, abokan cigaba, masu rike da mukaman siyasa da duk masu ruwa da tsaki.
COV/Khadija Aliyu