Gwamnatin Tarayya Ta ƙaryata Zargin Tigran Gambaryan Kan Jami’an Gwamnatin Nijeriya
Published: 15th, February 2025 GMT
Sai dai ya ce, dole ne a fayyace gaskiya don hana wannan yaudarar samun gindin zama.
Ya ce: “Karo na farko da Mista Gambaryan da tawagar sa suka zo Nijeriya, sun zo ne karan kansu ba tare da wata gayyata daga gwamnati ba. Sai dai da aka sanar da gwamnati wani batu na neman cin hanci a lokacin, sai aka buɗe bincike nan take, ko da yake babu wanda ya shigar da ƙorafi kai-tsaye.
Ya bayyana cewa, ziyarar Gambaryan ta biyu ta kasance wani ɓangare na bincike kan yadda ake amfani da kamfanin hada-hadar kuɗi na Binance don sarrafa darajar naira.
Ya ce, amma binciken ya gamu da cikas sakamakon dabarun da Gambaryan da tawagar sa suka yi amfani da su.
Ministan ya ƙara da cewa, Gambaryan ya samu ‘yanci a watan Oktoba na 2024 bisa dalilai na jinƙai, bayan cimma matsaya tsakanin Nijeriya da Amurka da ta kawo fa’ida ga Nijeriya.
Ya kuma ce gwamnati ta yi watsi da tayin da Binance ya yi na biyan dala miliyan 5 domin a saki Gambaryan, inda ta amince da wata yarjejeniya mai amfani da gwamnatin Amurka.
“Muna ƙaryata duk wata magana da Mista Gambaryan ke yi kan jami’an gwamnati da ke da hannu a shari’ar sa, kuma muna kira ga jama’a da su yi watsi da waɗannan ƙarairayi baki ɗaya,” inji Idris.
Ministan ya bayyana cewa zargin da Gambaryan ke yi babu hujja, kuma bai da inganci duba da cewa yana ƙoƙarin ɓata suna da razana waɗanda suka tabbatar an gurfanar da shi a gaban shari’a ne.
Ministan ya ce yana da yaƙinin cewa, tsarin shari’a na Nijeriya da na Amurka za su ba Gambaryan damar gabatar da hujjoji kan zarge-zargen da yake yi.
A halin yanzu, ya buƙaci ‘yan ƙasa da su yi hankali kada su faɗa tarkon waɗannan ƙarairayi da ƙazafi da wannan Ba’amurken yake yaɗawa.
এছাড়াও পড়ুন:
An kama mutumin da ake zargi da kashe jami’in sibil difens a Jigawa
Hukumar tsaro ta sibil difens (NSCDC) ta sanar da cafke wani mutum, Salisu Muhammad, mai shekaru 45, bisa zargin kashe jami’inta, Bashir Adamu Jibrin, a kasuwar Shuwarin da ke Karamar Hukumar Kiyawa a Jihar Jigawa.
A cewar wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na hukumar, Muhammed Badarudeen ya fitar a Dutse, babban birnin jihar, lamarin ya faru ne a ranar kasuwa lokacin da marigayin yake gudanar da aikinsa.
Ya ba wa alaramma kyautar motarsa saboda daɗin karatun Alkur’ani Tankokin mai sun yi bindiga a ZariyaRahotanni sun nuna cewa, ana zargin Salisu ya buga wa jami’in dutse a kai, lamarin da ya yi sanadin mutuwarsa.
Hukumar ta ce ta kama wanda ake zargin ne a gidansa da ke Shuwarin a ranar 7 ga watan Agusta, 2025.
Sai dai bayanai sun ce Salisu wanda bai cimma nasara ba yayi ƙoƙarin tserewa a yayin da ake jigilar sa zuwa hedikwatar NSCDC da ke Dutse a cikin motar jami’an tsaron.
Sanarwar ta ƙara da cewa, Salisu ya samu raunuka ne yayin da yake ƙoƙarin tserewa, kuma daga bisani aka kai shi babban asibitin Dutse, inda aka tabbatar da rasuwarsa sakamakon raunikan da ya samu.
Sai dai ’yan uwansa sun buƙaci cikakken bayani dangane da raunikan da ya samu har da dalilin rasuwarsa a asibitin Sambo Limited wanda aka garzaya da shi bayan ya yi yunƙrin tserewa daga mota da ke tafe.