Aminiya:
2025-05-01@04:06:26 GMT

Gurgu mai mata huɗu da bai yarda da yin bara ba

Published: 15th, February 2025 GMT

Duk da kasancewar Malam Murtala Abubakar nakasasshe mara kafafu, amma bai lamunci yin bara ba. Hasali ma, ya rabu da matarsa ta fari saboda dabi’arta ta yin bara.

Shekaru 50 da suka wuce Malam Muratala ya rasa kafafunsa, tun yana dan shekara bakwai a duniya. A haka ya ci gaba da rayuwarsa, inda a halin yanzu yake kula da iyalansa, mata hudu wadanda dukansu nakasassu ne da ’ya’yansu 15.

A haka yake fadi-tashin daukar dawainiyarsu, domin tsare mutuncinsa, saboda ya yi imanin cewa,  “Bara tana rage daraja da kimar mutum.” Wannan ne ma ya sa ya rabu da matarsa ta farko saboda dabi’ar bara.

Rayuwar Malam Murtala, wanda a lokacin da yake dan shekara bakwai yake takawa da kafafunsa zuwa ko’ina, ta juya ne bayan da ya kamu da wata cuta mai wuyar ganowa. Amma tsawon shekarun da ya yi da wannan lalura, yanzu ya zama babban abin misali da ke tabbatar da cewa nakasa ba kasawa ba ce.

A Najeriya, kasar da nakasassu da dama ke dogaro da bara don, Malam Murtala ya zama gagara-badau.

Madigancin, mazaunin unguwar Rikkos ne da ke Karamar Hukumar Jos ta Arewa a Jihar Filato, inda yake da dan shagon kayan masarufi da ya kafa tun shekaru kusan 25 da suka gabata. Da dan abin da yake samu daga shagon nasa da ke a tashar mota ta ‘Plateau Riders’ a birnin Jos yake kula da iyalinsa.

Auren mai nakasa shi ne zaman lafiya

Ya bayyana cewa daga bayan manyan ’ya’yansu sun shawo kansa, kuma yanzu ya dawo da babbar matarsa, a kan tsatsauran sharadin cewa ba za ta sake komawa bara ba, shi kuma zai samar mata da dan jarin fara sana’a a gida.

Ya bayyana rayuwarsa tare da su a matsayin “zabi cikin nutsuwa,” yana mai cewa ya auri nakasassu ne domin samun “salama da hutu a gida.

“Auren mace mai lafiya na iya jawo mini matsala,” ya yi dariya, ya kara da cewa, “Idan mazan da ke da nakasa za su rika auren mata masu lafiya, wa zai auri matan da ke da nakasa? Wannan na nufin za a bar mata da dama masu nakasa babu aure ba, kuma hakan zai tilasta wa yawancinsu ci gaba da bara.”

Ya tallafa wa matansa su yi sana’a

Shi da matan nasa hudu babu wanda ke motsa kafafunsu sakamakon yanayi daban-daban na rashin lafiya, amma duk da haka ba sa yin bara. A maimakon haka, kowacce ta sami karamin sana’ar da ta dogara da shi.

“Na karfafa musu gwiwa su gudanar da kananan sana’o’i a cikin gida domin mu taimaka wa juna wajen ciyar da iyali,” in ji shi, inda ya bayyana cewa yana son kowacce daga cikin matansa ta samu ’yancin samun kudi, musamman saboda ba ya samun isasshen kudi don biya wa dukkansu bukatunsu.

Ya samu goyon bayan matansa

Kaltume, matarsa ta biyu, tana goyon bayan matsayinsa a kan bara. Ta ce duk da yanayin kafafunta, ba ta taba jin sha’awar yin bara ba, tun kafin ya aure ta.

Ita ma ta yi imani da cewa “bara tana zubar da darajar mutum,” tana mai cewa duk yanayinsu su biyar, amma suna jin dadin rayuwarsu kuma suna da yakinin cewa Allah Zai tausaya musu matukar suna kokarin neman halak.

A lokacin da wakilinmu ya ziyarci gidansu da ke gefen unguwar Rikkos, ya ga yadda gidan da aka gina da laka ya cika da harkokin daban-daban da kuma kasuwanci. Matan Murtala uku da ke gida suna aiki cikin kuzari tare da jajircewa don samun abin rayuwa.

Wakilinmu ya lura da yadda matan suke kai-komo a cikin gida cikin kwarewa duk da yanayin jikinsu. Matan suna jan jiki daga daki zuwa kicin don kula da gyada da ake soyawa a kan wuta. Cikin sauki za a gane cewa magidancin ya gina gidansa ne a kan tushe mai karfi na jajircewa, kirkira, da tallafawa juna.

Kaltume wadda ke kwararriya ce a sana’o’i daban-daban ta shaida wa wakilinmu cikin farin ciki cewa, “Na kware wajen yin kitso, kuma duk Asabar, mata suna taruwa a nan gida in yi musu kitso su biya ni. Ina kuma hada turaruka da sabulai na gargajiya, wadanda nake sayarwa a shagunan kayan masarufi, har da na mijina.”

Ko da yake cewa sauran matan Murtala sun ki yin magana da wakilinmu, amma Kaltume, ta ce kowacce daga cikinsu na da nata sana’ar.

“Mu uku muka kware wajen suyar gyada, yayin da matar gida ta hudu ke sayar da kayan lambu. Muna aiki tare don tallafa wa juna da kuma inganta walwalar iyalinmu,” in ji ta.

Malam Murtala Abubakar ya ce, shi da iyalinsa suna cikin farin ciki a yanzu, amma ba koyaushe ake samun hakan ba.

Yadda na daina bara

A cikin yanayi mai cike na damuwa bayan ya tuna rayuwarsa ta baya, Malam Murtala ya ce ya tashi yana yin bara tun yana yaro, duk da cewa yana kin bara kuma yana kuka yana rokon iyayensa.

Ya ce, “Na san cewa duk sadaka da nake samu a kan tituna yana taimaka musu, amma suk da hakan ban taba jin dadinsa ba.”

Murtala ya ce a yayin da yake tasowa ya yi tafiya har zuwa Enugu da Aba da Fatakwal a Kudancin kasar nan don yin bara. Sai dai, a hankali ya gane cewa ba ta da tabbas, sai ya zabi neman hanyar halal ta rayuwa.

Magidancin ya ce, “Daina bara na da matukar wahala, amma na yanke shawarar neman sana’a, duk da cewa ba ni da jari.

“Na yi tafiye-tafiye daga wuri zuwa wuri don neman hanyar samun abin rayuwa, amma ban samu jari ba, kuma ba na son ci gaba da bara. Da taimakon Allah, bayan shan wahalhalu da dama, na sami damar kafa karamin shago na kayan masarufi. Duk da cewa kasuwancin ba ya da isasshen jari, na gudanar da shi tsawon shekaru fiye da 20,” in ji shi.

Yadda yake rayuwa

A yanzu da yake da mutane 20 a karkashinsa, ya ce yana biyan kudin makarantar ’ya’yansa daga dan kudin da yake samu daga sana’arsa.

Ya ce, a cikin yaran “Wasu sun kammala firamare, wasu kuma sun gama sakandare. Na aurar da ’ya’yana mata guda biyar. Ga ’ya’ya maza kuwa, na saka su a sana’o’i daban-daban saboda ba zan iya daukar nauyin karatunsu nan gaba ba.”

Dattijon ya bayana cewa yana cikin farin ciki da kwanciyar hankali da ya daina dogaro da bara kumam yana alfahari da kadan din da yake samu daga shagonsa.

Sai dai ya ce, a baya-bayan nan, bara ta so ta ja shi a lokacin da ya gobara ta kone shagon nasa kurmus. Amma duk da jarabar barar da ta addabe shi, jajircewarsa ta yi galaba, ba tare da ya mika wuya ba.

Ya ce, “Na san irin illar da bara ke yi ga darajar mutum,” yana mai bayyana cewa abokan arziki da masu fatan alheri a tashar mota sun taimaka masa wajen tara kudin sake gina shagonsa da ci gaba da kasuwanci. “Ina gode wa Allah bisa ci gaban da aka samu zuwa yanzu,” in ji shi.

Na kusa komawa ruwa

Bayan da ya kwace daga bara, yanzu haka yana cikin masu kira kan guje ta. Ya bayyana rayuwar mabaraci a matsayin mai cike da bakin ciki, wadda babu wani mai hankali, ko mai nakasa ko lafiyayye, da ya kamata ya so yin ta. Sai dai, ya ce mutane da dama suna yi ne saboda rashin damar tara jari don fara kananan sana’o’i. Ya jaddada cewa, “Ni dai na yi sa’ar tsira daga bara. Babu wata kima ko daraja a cikinta.”

Kaltume, ta bayyana cewa bai kamata nakasa ta kashe wa mutum zuciya ba. Ta shawarci nakasassu da ke yin bara da cewa “Ba yana nufin ka rasa duk jikinka ba ne. Ka nemi sana’a ka ci gaba da rayuwa kamar kowa. Ka fara wani abu ka roki Allah Ya sa albarka; za ka ga ka samu nasara.” Ta kara da cewa masu bara a kan titi suna fuskantar mummunar yanayi wanda ke sa su kamuwa da cututtuka daban-daban.

Yayin da yake hawa babur dinsa mai kafa hudu da aka kera masa na musamman, Malam Murtala ya ce ana iya shawo kan masu bara su bar kan tituna idan kowa zai ba da gudummawar da ta dace.

A karshe ya yi kira ga gwamnati da ta gane cewa nakasassu suna da muhimmanci a cikin al’umma, ta kuma tallafa musu da sana’o’i. “Ba duk masu nakasa ne ke son kashe rayuwarsu a kan tituna suna bara ba. Nakasasshe mai hankali zai so ya daina bara,” in ji shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: bayyana cewa

এছাড়াও পড়ুন:

Kissoshin Rayuwa: Imam Hassan (a) 115

115-Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka barkammu da sake saduwa a cikin shirimmu na kissoshin rayuwa shiri wanda yake kawo maku kissiso da suka zo cikin alkur’ani mai girma ko kuma cikin wasu littafan wadanda suka hada da littafin dastane rastan, ko kum littafin mathnawi na maulana Jalaluddeen rumi. Ko kuma cikin wasu littafan da fatan masu sauraro zasu kasance tare da mu a cikin shirimmu na yau.

///… Masu sauraro idan kuna tare da mu a cikin shirimmu da ya gabata, a kuma cikin sirar Imam Al-hassan limami na biyu daga cikin limamai masu tsarki daga iyalan gidan manzon All..(s), kuma da na farko ga Fatimah(s) diyar manzon All..(s), sannan jikansa na farko.

A cikin shirimmu da ya gabata, mun ji yadda wasu malaman tarihi suka kawo wasu hadisai wadanda basu inganta ba suka jinginawa Imam Alhassan Almujtaba (a) dangane da son da yakewa khalifa na ukku wasu Uthman bin Affan, mun gudanar da bincike cikin daya daga cikin hadisan a sanadi da kuma mataninsa inda muka tabbatar da cewa , Mada’ini wanda aka ruwaito wannan hadisin, nasibi ne, wato wata jama’a wacce ta ke addini da kiyayya ga iyalan gidan manzon All..(s), har’ila yau yana kirkiro hadisan na kariya ya jinganawa manzon All..(s) na muzantasu da kuma kirkiro wasu hadisan daga manzon All..(s) na yabon banu umayya.

Sannan a matanin hadisin mun bayyana kariyar zance mai cewa Imam Hassan yana zargin babansa Imam Ali (a) da hannu a kashe Uthman dan Affan, sannan yana tare da mahaifinsa, manya-manyan yake-yake guda biyu da yayi a lokacin khalifancinsa, da wadanda  suke tuhumarsa da zubar da jinin Khalifa Uthman.

Wato yake-yaken Jamal da Siffin. Imam Hassan (a) ya yaki wadannan makiyan mahaifinsa wadanda suke zarginsa da hannu a kissan Uthman. Kuma bamu taba sanin akwai sabani tsakanin Imam Ali (a) da yayansa Alhassan da Alhussain (a).

Daga karshen mun kawo maku yadda manyamanayn sahabban manzon All..(s) da suka rage a Madina suka rubuta wasi ku zuwa sauran sahabbansa a sauran yankuna na daular musulunci suna neman taimakonsu don kauda Khalifa uthman daga khalifanci, saboda ya sabawa littafin All..da sunnar manzon All..da kuma siran khalifofin da suka gabata. Sun koka kan yadda ya mika al-amuran daular musulunci ga danginsa banu Umayya suna satar dukiyar al-umma sannan sun barsu da talauci.

Mun bayyana cewa akwai abubun lura a cikin wannan wasikar kamar haka,

1-Sunan zarginsa na kin amfani da littafin All..

02-Sauya sunnan manzon All..(s) da kuma, yayi watsi da ita,

03-yayi watsi ga hanyar khalifofin biyu da suka gabace shi wato Abubakar da Umar

04- Ya kauda ma’anar khalifancin manzon All..(s) daga yadda yakamata ta kasance,

5-Kwace dukkan duniyar Al-ammu da kuka sarrafata a wasu wurare kebantattu, wato kashe ta kan dangin khalifa wato Banu Umayya.

Malaman tarihi sun bayyana cewa, wadannan al-amura sun girgiza daular musulunci, kuma sun kusan su rusata.

Sannan mun bayyana cewa wadanda suke sukan shugabancin Khalifa Uthman sun rubuta wata wasika ga murabiduna, wato wadanda suke kula da kan iyakokin daular musulunci daga cikin sahabbai, sun bukacesu su dawo madina don tsada khalifancin manzon All..(a), don tabbatar da khaifancin ya dawo kan yadda yakamata ya kasanci.

Ga kuma matanin wasikar kamar haka.

{Lalle ku, kun fita ne don ku yi jihadi a kan tafarkin All..mai girma da daukaka, kuna neman kare addinin Muhammad (s) to lalle khalifanku ya lalata addnin Muhammadu, ku dawo ku tsaida shi,…}.

Banda haka a lokacinda wasikun nan suka isa yankuna da dama na daular musulunci sun yi ta aika tawaga don ganin abinda yake faruwa a Madina, sannan tawagogi da suka isa Madina don ganewa idanunsu abubuwan da suke faruwa, da kuma tattauna matsalolin da kuma yadda za’a magance su, sun hada da.

Tawaga daga kasar Masar, kafin haka akwai mutane 700 da suka tura tun farko bayan da suka kama wani bawan Khalifa Uthman wanda ake kira warsh dauke da wasikar Khalifa zuwa dan uwansa gwamnan Masar Abdullahi ibn Abisharkh, na ya kashe sui dan sun isa da sabon kwamna Muhammad dan Abubakar.

A wannan karon mutanen masar sun aiki mutane 400. Tare da jagorancin Muhammad dan Abubakar wanda dama yana manina, da Abdrrahman dan Udais Al-balawi.

2-sai tawagar Kufa wanda ya hada da Malik dan Ashtar, Zaidu dan Sauhan Al-Abdi, da Ziyad dan Annadhir Al-harithy. Da abdullahi dan Asam Al-Amuri da shugabansu gaba daya, Amru dan Ah-tham .

03-sai tawagar Basra wacce ta hada da Hakin dan Jibilah, tere da wasu mutane 100. Bayan haka wasu khamsin sun bisu. A cikinsu akwai Zarih dan Abidi Al-Abdi, da bishru dan shuraih Alkaisi, da dan Mahrash, da wasunsu daga cikin fitattun mutane kuma sanannu na Basra.

A lokacinda wadannan tawagogi suka isa Madina an yi maraba da su, kuma nag ode masu da karban kiran da aka yi masu, sannan sun tattauna da sauran sahabbai da kuma musulmai dan al-amuran da suka faru, da kuma irin mummunan halin da musulmi suka shiga ciki saboda yadda Khalifa Uthman ya sauya al-amura da dama, daga cikin ya hanasu dukiyoyinsu, wadanda suka saba samu a zamanin khalifofin da suka gabata. Ko kuma ya fita daga tsarin da manzon All..(s) yake raba dukiya a cikin al-umma.

Bayan yan kwanaki sai mutanen kasar masar sun ga cewa kafin ko me da farko a rubutawa khalifa Usman  wasika, a yi masa nisiha kan ya dawo kan tafarkin da ya dace ga kuma kadan daga cikin abinda wasikar ta kunsa.

Bayan Basmala da salati ga manzon All..(s) da kuma godiya ga All..sai suka ce

(bayan haka, ka sani kan cewa, {Lalle All..baya sauya halin da mutane suke ciki sai sai sun sauya halinsu, muna hadaka da All..kuma muna sake hadaka da All..Lalle kai kana cikin duniya mai gucewa, … .. kuma kada ka manta da rabon a lahira, kada duniya ta rudeka, kuma ka san cewa mu don All..muke yi, kuma don All…muke fushi. Kuma muna neman yardarm All.. ne, kuma lalle ba zamu dauke takubbammu daga wuyoyimmu ba saika tuba daga abubuwan da ka aikata mana, tuba mai tsanani kuma a fili, wannan shi ne maganarmu da kai, sannan bukatarmu a gareka, All..ne mai karban uzurimmu dangane da kai..wassalam…}.

A lokacinda Khalifa Uthman ya karanta sai ya ji tsoro. Sai Mughira ya nemi izininsa yayi Magana da mutane, sai ya bashi izini, a lokacinda suka ganshi sai suka daga murya suna cewa: Ya makaho  koma ya Fajiri koma ya fasiki koma.ya koma ya kasa Magana da su.

Sai Uthman ya kira Amru dan Asi, ya bukaci yayi Magana da su, ya amince, amma a lokacinda suka ganshi, sai yayi masu, sallama ba wanda ya amsa daga cikinsu,  suka daga murya suna cewa: Ko koma ya makiyin All.. ka kuma ya dan Nabigha. Kai ba amintecce ne a wajemmu ba kuma mai aminci ba.

A nan sai Khalifa Uthman ya fahinci cewa babu wanda zai taimaka masa sai Amirulminina Aliyu dan Abitalib (a), sai ya nemi taimakonsa, ya fada masa cewa, yayi kira ga mutane zuwa ga Alkur’ani mai girma da sunnar annabinsa.

Sai Imam ya amince, amma da sharudda kan cewa, ya yi masa alkawali tsakaninsa da All..zai yi aiki da abinda ya fada. Sai ya yi alkawali zai zai cika alkawalinsa, za iyi aiki da abinda ya fada.

Sai Imam (a) ya je wajen mutane, shima a lokacinda suka ganshi suka ce, koma , sai yace a’a na zo maku da cewa, za’a yi aiki da littafin All.., kuma za’a sauya duk abinda kuka yi fushi dominsa. Sai ya fada masu abinda khlifa ya bada.  Sai suka ce: Ka lamunce mana haka zai faru? Sai yace :ee. Sai suka ce mun yarda.   

Sai ya shigar da manya manya daga fitattun mutane  wajen Uthman, sai suka yi ta sukansa, sannan suka ce, ya Sanya abinda ya yi alkawali na aiki da littafin All..da kuma sunnar manzon All..(s) da kuma bawa musulmi hakkinsu da ake basu.

Sai ya amince ya rubuta ya basu sannan suka karbi takardan suka kama hanyar masar.

Wannan shi ne nassin abinda ya rubuta ya basu’

{Wannan rubutun daga bawan All..Uthman Amirulmuminina zuwa ga wadanda suke sukansa daga cikin muminai da musulmai, kan cewa hakkinsu ne in yi aiki da littafin All..da sunnar annabinsa a cikinu, za’a bawa talaka hakkinsa, wanda yake cikin tsoro a amintar da shi, wanda aka kora adawo da shi …kuma za’a samar da kudade ga musulmi. Sannan Aliyu dan Abitalib (a) shi ne mai lamuncewa muminai, kuma wajibi ne ga Uthman ya cika alkawalin da ya dauka cikin wannan rubutun}.

Banda haka Zubair dan Awwam, Talha dan Ubaidullahi,Sa’du dan Abi wallas, Abdullahi dan Umar, Zaidu dan Thabit, Sahal dan Hunaif,, Abu ayyuba Khalid dan zaid, kuma anyi wannan rubutun a cikin watan Zulkida shekara ta shekara 35.

Masu sauraro a nan zamu dasa aya a cikin shirimmu nay au sai kuma wata fitowa idan All..ya kaimu. Wassalau alaikum warahamatullahi wa barakathu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran ta sha alwashin ci gaba da aiwatar da manufofinta na raya dangantakarta da Nijar
  • Cinikayyar Hidima Ta Kasar Sin Ta Matukar Bunkasa A Rubu’in Farko Na Nana
  • Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci Na Iran Ya Ce: Maganar ‘Yan Sahayoniyya Rudu Ne Maras Amfani
  • Nijeriya Na Ke Yi Wa Biyayya Ba Wani Ko Jam’iyya Ba – El-Rufai
  • Shugaban Kasar Yana Maraba Da Masu Zuba Hannun Jari A Kasarsa Daga Kasashen Waje
  • Yadda matar gwamna ta sa mata gasar haihuwar ’yan uku
  • Falasdinu: Mahmud Abbas Ya Nada Magaji Da Kuma Mataimakasa
  • Ma’aikata 240 na karɓar albashi biyu, wasu 217 na amfani da lambar BVN ɗaya a Kano
  • Kissoshin Rayuwa: Imam Hassan (a) 115
  • Kissoshin Rayuwa: Imam Al-Hassan 114