‘Yan Majalisar Najeriya Sun Amince Da Karin Dala Miliyan 200 A Cikin Kasafin Kudin 2025
Published: 15th, February 2025 GMT
Amincewa da Karin kudin dai ya zo ne domin cike gibin da aka samu, bayan da Amurka ta yanke kudaden taimakon da take bayarwa a fagen kiwon lafiya.
A shekarar 2023 Kasar Najeriya mai mutane fiye da miliyan 200 tana cikin 10 na farko da su ka fi karbar tallafin hukumar Amurka na raya kasashe ( USAID). Sai dai a halin yanzu shugaban kasar Amurka Donald Trump ya dakatar da wannan taimakon na tsawon kwanaki 90.
Wani dan majalisar dattijan Najeriya Sen. Adeola Olamkilekan wanda ya yi Magana a yayin zaman majalisar na amincewa da Karin kasafin kudin ya ce; Kasar ta za ji jiki sosai saboda yadda Amurka ta yanke tallafin, musamman a fagen dakile cutuka.
Dala miliyan 200 da aka amince da su, suna cikin kasafin kudin kasar ne na dala biliyan 36.6.
Za a yi amfani da mafi yawancin kudaden ne dai domin samar da magungunan riga-kafi da kuma magance cututtuka na annoba.
A shekarar 2023 Amerika ta bai wa Najeirya dala miliyan 600, domin amfani da su a fagen kiwon lafiya. Ofishin jakadancin Amurka a Najeriya ya ce, an bayar da wadancan kudaden ne dai domin riga-kafin zazzabin Malariya, da kuma rika-kafin cutar HIV da magungunanta.
Bugu da kari, yanke taimakon na Amurka zai iya shafar fagen ayyukan jin kai, musamman a yankin Arewa maso gabashin kasar da ake fama da matsalar masu dauke da makamai dake kashe mutane tun 2009 da ya haddasa kwararar ‘yan gudun hijira masu yawa.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
NAJERIYA A YAU: Dalilin karyewar farashin shinkafa a kasuwannin Najeriya
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
Rahotanni suna nuna cewa farashin shinkafa, ɗaya daga cikin nau’ukan abincin da ’yan Najeriya suka fi ci, ya karye a wasu sassan ƙasar.
Sauyin farashin ya sa ana tambayoyi — shin me ya haifar da wannan sauyi? Kuma me hakan ke iya haifarwa a rayuwar talaka?
NAJERIYA A YAU: “Dalilin da muke sauya sheƙa zuwa jam’iyya mai mulki” DAGA LARABA: Dalilan Rashin Wutar Lantarki A Wasu Jihohin ArewaA kan wannan sauyi da dalilansa ne shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi nazari.
Domin sauke shirin, latsa nan