Amincewa da Karin kudin dai ya zo ne domin cike gibin da aka samu, bayan da Amurka ta yanke kudaden taimakon da take bayarwa a fagen kiwon lafiya.

A shekarar 2023 Kasar Najeriya mai mutane fiye da miliyan 200 tana cikin 10 na farko da su ka fi karbar tallafin hukumar Amurka na raya kasashe ( USAID). Sai dai a halin yanzu shugaban kasar Amurka Donald Trump ya dakatar da wannan taimakon  na tsawon kwanaki 90.

Wani dan majalisar dattijan Najeriya Sen. Adeola Olamkilekan wanda ya yi Magana a yayin zaman majalisar na amincewa da Karin kasafin kudin ya ce; Kasar ta za ji jiki sosai saboda yadda Amurka ta yanke tallafin, musamman a fagen dakile cutuka.

Dala miliyan 200 da aka amince da su, suna cikin kasafin kudin kasar ne na dala biliyan 36.6.

Za a yi amfani da mafi yawancin kudaden ne dai domin samar da magungunan riga-kafi da kuma magance cututtuka na annoba.

A shekarar 2023 Amerika ta bai wa Najeirya dala miliyan 600, domin amfani da su a fagen kiwon lafiya. Ofishin jakadancin Amurka a Najeriya ya ce, an bayar da wadancan kudaden ne dai domin riga-kafin zazzabin Malariya, da kuma rika-kafin cutar HIV da magungunanta.

Bugu da kari,  yanke taimakon na Amurka zai iya shafar fagen ayyukan jin kai, musamman a yankin Arewa maso gabashin kasar da ake fama da matsalar masu dauke da makamai dake kashe mutane tun 2009 da ya haddasa kwararar ‘yan gudun hijira masu yawa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Dalilin karyewar farashin shinkafa a kasuwannin Najeriya

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Rahotanni suna nuna cewa farashin shinkafa, ɗaya daga cikin nau’ukan abincin da ’yan Najeriya suka fi ci, ya karye a wasu sassan ƙasar.

Sauyin farashin ya sa ana tambayoyi — shin me ya haifar da wannan sauyi? Kuma me hakan ke iya haifarwa a rayuwar talaka?

NAJERIYA A YAU: “Dalilin da muke sauya sheƙa zuwa jam’iyya mai mulki” DAGA LARABA: Dalilan Rashin Wutar Lantarki A Wasu Jihohin Arewa

A kan wannan sauyi da dalilansa ne shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi nazari.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Amurka ta sake laftawa wasu kamfaninin mai na Iran takunkumi
  • Gwamnan Sokoto Ya Amince Da Sauya Wa Manyan Sakatarori 25 Ma’aikatu A Jihar 
  • Dokta Bashir ya zama shugaban Majalisar Shari’ar Musulunci ta Nijeriya
  • Za A Yi Allurar Rigakafi Ga Dabbobi Sama Da Miliyan Daya A Babura
  • Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya
  • Shugaban Majalisar Ƙoli ta Shari’ar Musulunci a Najeriya ya rasu
  • NAJERIYA A YAU: Dalilin karyewar farashin shinkafa a kasuwannin Najeriya
  • Hajjin 2025: Jihar Kwara Ta Fara Allurar Rigakafi Ga Maniyyata
  • Sin Na Maraba Da Karin Abokai Daga Kasa Da Kasa Su Ziyarci Kasar
  • Iran Da Rasha Sun Jaddada Yin Aiki Tare A Fagen Kiwon Lafiya