An Kama Ɗan Nijeriya Mazaunin Indiya Bisa Zargin Damfarar Kamfani Dala 13,361
Published: 15th, February 2025 GMT
Rahoton ya ce an fara badakalar ne a ranar 10 ga watan Disamba a lokacin da kamfanin harhada magunguna ya samu sakon imel dake nuna wani mai sayar da shi, Accent Pharma, yana neman a biya shi wani sabon asusun ajiya na banki.
Ba tare da sanin sakon imel din na yaudara ne ba, ana zargin kamfanin harhada magunguna ya aika Rs 11.
Wakilinmu ya ruwaito cewa kamfanin ya gano cewa an yi kutse ne bayan an biya kudin da kuma tantancewa. Wannan ya haifar da kwakkwaran bincike daga sashin damfarar intanet na kasar.
Rahoton ya kara da cewa, “Masu bincike sun binciki email din da aka yi wa kutse zuwa Nijeriya inda suka bi diddigin kudaden a asusun bankin Manipur. Hotunan sa ido sun kai ga kama Ngomere.
“An same shi ba tare da ingantacciyar takardar biza ta Indiya ba kuma ana zarginsa da kasancewa wani babban jami’in kungiyar. An yi rajistar FIR a karkashin Bharatiya Nyaya Sanhita da Dokar Baki. Ana ci gaba da bincike.”
A watan Janairun 2025, jaridar PUNCH Metro ta ruwaito cewa Babban Sashen Binciken Laifuka na Kuwait a Jihar Ahmadi ya kama wasu ‘yan Nijeriya biyu da laifin fashi da makami.
An kama wadanda ake zargin ne cikin sa’o’i 24 bayan sun yi fashi a ofishin musayar kudi a Mahboula, wansu gundumomi a kudancin birnin Kuwait.
Ana zargin sun saci kudaden kasashen waje da suka kai Dinar Kuwaiti 4,600, kwatankwacin Dalar Amurka kusan 14,918.69 dangane da kudin musaya na currencyconbertonline.com.
কীওয়ার্ড: Damfara
এছাড়াও পড়ুন:
Ana zargin ɗa da kashe mahaifinsa a Kano saboda hana shi ƙara aure
Babbar Kotun Kano mai lamba 7 da ke zama a cikin birni ta bayar da umarnin tsare Aminu Ismail, mazaunin Unguwar Bai a Karamar Hukumar Ajingi ta jihar, bisa zarginsa da kashe mahaifinsa, Malam Dahiru Ahmad, ta hanyar caka masa wuƙa har lahira.
Lamarin ya faru ne bayan samun sabani tsakaninsu kan aniyar Aminu ta ƙara aure, wadda mahaifinsa ya ƙi goyon baya saboda abin da ya kira halin tattalin arzikin da ake fama da shi a kasa.
Babu wani uzuri da za a yi wa sabbin hafsoshi kan matsalar tsaron Nijeriya — Tinubu Borno ta fara fitar da kayan robobi zuwa ƙasashen waje – ZulumA cewar lauyan masu ƙara, Barrista Lamido Abba Sorondinki, wanda ake tuhuma ya shaida wa mahaifinsa niyyarsa ta kara mata ta biyu, amma mahaifinsa ya ba shi shawarar kada ya yi hakan, yana mai danganta matsalar da halin tattalin arzikin ƙasa ke ciki.
Wannan sabani ya rikide zuwa faɗa, inda ake zargin Aminu da caccaka wa mahaifin nasa wuƙa a ƙirji, lamarin da ya jawo masa rauni mai tsanani har ya rasa ransa.
An gurfanar da Aminu da laifin kisan kai, wanda ya saba da Sashe na 221 na kundin penal code.
Ana ci gaba da shari’ar, kuma kotu ta bayar da umarnin tsare shi har zuwa lokacin da za a ci gaba da sauraron ƙarar.