Makwabta sun kai karar ma’aurata saboda carar zakaransu
Published: 15th, February 2025 GMT
Wasu magidanta da suka mallaki wani zakara (Ricco) jinsin Bantam daga Bourgoin-Jallieu a sashen Isère na kasar Faransa, sun karɓi sammaci domin bayyana a gaban kotu sakamakon korafin da wani makwabcinsu ya yi game da carar zakaran.
Korafin da suka yi ya hada da, rashin barci saboda karar zakaran yake yi a yayin carar, kamar yadda mai gabatar da ƙara ya ambata, wanda ya gayyaci masu zakara (Ricco) zuwa kotu a watan Janairun 2025.
Mutumin, wanda ya fi son a sakaya sunansa, yana daya daga cikin makwabtan masu ikirarin cewa, carar zakaran ba za a iya jure ta ba da daddare da rana.
Masu wannan zakaran mai shekaru 5 a koyaushe suna musanta wadannan ikirari, inda suka kafe a kan cewa, zakaran yana da tsarin sarrafa kansa wanda ya tsara yin carar daga karfe 8:30 na safe a lokacin hunturu da karfe 9:00 na safe a lokacin rani.
Sun dage cewa, zakara ya kan yi cara kamar sau 15 a cikin mintuna 15 da safe, sannan sai ya kara yin cara da rana.
“Akwai tsarin da yake bi, wanda yake nuna cewa, yana rufe yin carar daga karfe 8 na dare. Kuma yana farawa da karfe 9 na safe a lokacin rani, 8:30 na safe a cikin hunturu,” in ji Franck, mamallakin zakaran (Ricco).
Da muka kawo zakarar, sai muka cewa kanmu don kada ya damu makwabtanmu, sai muka tabbatar an bude kofar kejinsa daga karfe 8:30. Sai muka yanke shawarar buɗe shi da karfe 9:00 na safe.
“Mun fahimci cewa, lokacin sanyi, kaji ba sa yin kwai don suna bukatar haske.
“Don haka a lokacin sanyi, muna bude shi da karfe 8:30, kuma a lokacin rani muna bude shi daga karfe 9:00 na safe.”
Ma’auratan sun koma garin Bourgoin-Jallieu da ke birnin shekaru 25 da suka gabata don yin rayuwa mai sauki kuma, inda suka yi mamakin matakin shari’a da makwabcinsu ya dauka.
Da farko sun yi kokarin sasantawa ta hanyar tattaunawa da makwabtan, amma hakan bai yuwu ba, kuma makwabcin ma’auratan ya yanke shawarar kai su kotu.
Franck ya yi ikirarin cewa, ya yi magana da kowanne daga cikin makwabtansu, kuma babu dayansu da ke da matsala da carar zakaran.
“Mun je wajen dukkan makwabtan, mun san wasu daga cikin matsalolinsu saboda mun zauna a nan tsawon shekaru 25,” in ji Franck.
“Mun tambaye su ko zakara yana damun su. Duk wadanda muka tuntuba cewa zakara ya dame su. Sai a samu akasin haka, suna son su ji carar zakara.”
A gefe guda, wacce ta shigar da karar, wanda ta koma Bourgoin Jallieu a cikin 2021, ta kafe a kan cewa carar da zakaran ke yi tana hana ta jin dadin lambunta da yin barci mai kyau, kuma suna son yanayin ya canza.
Rikicin shari’ar game da carar zakarar ya mayar da hankali ne kan dokar Faransa ta Janairu 29, 2021.
A gefe guda, masu zakaran sun yi imanin cewa, suna zaune a cikin yankin da ya kasance yankunan karkara ce, yayin da makwabcinsu ya yi imanin cewa, gundumar Boussieu ba ta kasance a cikin karkara ba.
A wannan shekarar ce alkali zai yanke hukunci kan wannan batu. Abin farin ciki ga zakara Ricco, yana da goyon bayan shafukan sada zumunta na zamani.
An kirkiro masa wani shafi a Fesbuk na goyon bayansa, inda mutane ke karfafa masa gwiwa ya ci gaba da yin cara da kuma gayyatar masu sukar zakaran da su yi kaura idan ba sa son “cararsa”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Carar Zakara Faransa Zakara carar zakaran carar zakara
এছাড়াও পড়ুন:
Mahara sun kashe ’yan ɗaurin aure 12 daga Zariya a Filato
An yi wa wasu matafiya ɗaurin aure 12 kisan gilla bayan wasu mutane sun kai musu hari a yankin Mangu ta Jihar Filato sun kai musu hari.
Rahotanni sun bayyana cewa mutum 11 daga cikin matafiya suna samun kulawa a asibiti, bayan raunukan da suka samu a harin da aka kai musu a yankin Ƙaramar Hukumar Mangu a ranar Juma’a.
Aminiya ta samu labarin cewar an kai wa matafiya hari ne da misalin ƙarfe 8 na dare, a lokacin da su mutum 31, ciki har da mata da ƙananan yara, a cikin wata bas mallakin Jami’ar Ahmadu Bello (ABU) ta Zariya.
Ayarin ’yan daurin auren da aka kai wa harin sun fito ne daga yankin Basawa da ke Zariya a Jihar Kaduna, lokacin da maharan suka tare su a kusa da yankin Ƙaramar Hukumar Qu’an Pan, suka kashe mutum 12, ciki har da direban motar, wanda ma’aikacin jami’ar ne.
Najeriya ta tura sojoji domin samar da zaman lafiya a Gambia Yadda Iran ta lalata cibiyar kimiyya mafi muhimmanci a Isra’ilaBabban Limamin Masallacin Juma’a na Jama’atu Izalatil Bid’a Wa’ikamatis Sunnah (JIBWIS), da ke Mangu, Sheikh Suleiman Haruna, ya tabbatar da faruwar lamarin, da cewa an ajiye gawarwakin a Babban Asibitin Mangu.
Sheikh Suleiman Haruna, ya ce, “Matafiya 31 ne a motar. Mun samu gawarwakin mutum takwas, amma mun roƙi jami’an tsaro su taimaka wajen kawo ragowar gawarwaki huɗu da suka rage.
“Muna tare da Shugaban Ƙaramar Hukumar Mangu kuma yana iya bakin ƙoƙarinsa a kan lamarin.”
Wani wanda ya tsallake rijiya da baya a harin, Ibrahim Umar, ya ce, “Mun kusa kaiwa Qu’an Pan bikin ɗaurin auren ɗan uwanmu, amma muka yi ɓatan kai saboda ba mu san hanyar ba.
“Mun tsaya tambayar wasu mutane kwatance, kafin mu farga har sun yi mana ƙawanya sun zagaye motar ta kowace kusurwa, suna ihu cewa a kashe mu, mu Hausawa ne.
“Daga nan suka fara duka suna kawo mana hari da muggan makamai. Direban suka fara kashewa kafin sauranmu, suka ƙona motar da gawarwakin mutane a ciki. Yanzu muna asibiti ana jinyar mu.”
Wakilimmu ya tuntuɓi kakakin ’yan sanda na Jihar Filato, DSP Alfred Altau, kuma jami’in ya shaida masa cewa yana sane da lamarin, amma sai nan gaba zai fitar da sanarwa a hukumance bayan tantance haƙiƙanin abin da ya faru.