Babu Tattaunawa Karkashin Takunkuman Tattalin Arziki: Aragchi
Published: 10th, February 2025 GMT
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya bayyana cewa, kasar Iran ba zata taba zama don tattaunawa da kasar Amurka ba a dai-dai lokacin take kara takurawa kasar da takunkuman tattalin arziki ba.
Tashar talabijin ta Presstva nan Tehran ta nakalto ministan yana fadar haka bikin ciki shekaru 46 da samun nasarar juyin juya halin musulunci a kasar a yau litinin, a birnin Hamedan.
Imam Khumaini (q) ne ya jagoranci kasar zuwa ga nasara a shekara 1979, Juyin juya halin da ya kawo karshen Sarautar Muhammad Reza sha Pahlavi.
Ministan ya kara da cewa Jagoran juyin juya halin musulunci ya rika ya bayyana matsayin gwamnatin kasar Iran kan wannan batun, sannan abinda ya fada shi ne duk wani mai hankali zai koma gareshi.
Ministan ya kara da cewa, gwamnatocin Amurka ba abinda amincewa bane, kuma an jarrabesu an gani, a baya an tattauna da su, basu cika alkawalinsu, kuma ko a yanzun aka shiga wata sabuwar tattaunawa da su, ba bu tabbacin za su yi aiki da abinda aka cimma tsakanin bangarorin biyu ba.
Aragchi ya kammala da cewa. mai hankali ba zai taba amincewa da gwamnatin Amurka ba. Banda haka mutanen Iran sun yi juyinjuya halin musulunci ne don yanke hannun kasashen ketare daga al-amuran kasar. Don haka a halin yanzu ma ba zamu amince da wata kasa ta tilasta mana bin ra’ayinta ba.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Oman ta tabbatar da soke tattaunawar Iran da Amurka zagaye na shida
Ministan harkokin wajen Omani Badr Albusaidi ya sanar da cewa, ba za a gudanar da zagaye na shida na tattaunawar nukiliya tsakanin Iran da Amurka ba.
Yau Lahadi ne aka shirya gudanar da zagaye na gaba na shawarwari a Muscat babban birnin kasar Oman.
A cikin wani sakon da ya wallafa a kan X (tsohon Twitter), Albusaidi ya tabbatar da sokewar, yayin da ya jaddada cewa “diflomasiyya da tattaunawa sun kasance hanya daya tilo ta samun zaman lafiya mai dorewa.”
“Tattaunawar Iran da Amurka, wadda aka shirya gudanar da ita a birnin Muscat ranar Lahadin nan, ba za ta gudana a yanzu ba.
Tattaunawar diflomasiyyar da aka faro kan shirin nukiliyar Iran, a watan Afrilu a shiga tsakanin masarautar Oman, ta wargaje biyo bayan mummunan harin da Isra’ila ta kai kan Jamhuriyar Musulunci ta Iran.
Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi, a wata tattaunawa ta wayar tarho da shugabar harkokin wajen kungiyar EU Kaja Kalas a ranar Asabar, ya ce ci gaba da tattaunawa da Amurka a cikin danyen aikin da Isra’ila ke yi bai da wata fa’ida.
Babban jami’in diflomasiyyar na Iran ya ce kalaman shugaban Amurka sun tabbatar da cewa matakin da Isra’ila ta dauka kan Iran ya samo asali ne daga goyon bayan da Washington ke baiwa gwamnatin Tel-Aviv kai tsaye.