Al’umar Iran Suna Gudanar Da Bukukuwan Zagayowar Nasarar Juyin Juya Halin Musulunci Yau Shekaru 46
Published: 10th, February 2025 GMT
Iran tana gudanar da bukukuwan zagayowar nasarar juyin juya halin Musulunci yau tsawon shekaru 46 tare da samun nasarori da kalubale
A yau Litinin ne, al’ummar Iran suke gudanar da bukukuwan tunawa da cika shekaru 46 da samun nasarar juyin juya halin Musulunci a kasar, wanda marigayi Imam Ruhollah Khomeini (Yardan Allah ta tabbata a gare shi) ya jagoranta, a cikin wadannan shekaru da dama, juyin juya halin Musulunci ya fuskanci makirce-makirce masu yawa da cikas, kuma ya samu gagarumar nasara, mafi muhimmanci daga cikinsu shi ne hambarar da gwamnatin sarki Shah da kasashen yammacin duniya suke goya masa baya, kamar yadda Iran bayan samun nasarar juyin juya halin Musulunci ta yi nasarar kafa gwamnati da samar da ginshikanta da samun gagarumar nasarori da ci gaba a dukkanin fannonin kimiyya da fasaha, kuma Iran ta zama daya daga cikin kasashen da suka ci gaba a duniya.
A shekara ta 1979 ne duniya ta shaida wani lamari na juyin juya hali na duniya wanda ya sauya fasalin duniya tare da bai wa Imam Ayatullah Ruhollah Khomeini (amincin Allah ya tabbata a gare shi) nasarar kifar da gwamnatin kama karya mafi zalunci mai karfin alaka ta kud da kud da kasashen yammacin Turai ta Sarki Shah Mohammad Reza Pahlavi da ya dauki matakin gudu daga Iran zuwa abokansa musamman Amurka sannan ya yi gudun hijira zuwa kasar Masar bayan da ya fuskancin juya baya ga iyayen gijinsa na yammaci Turai.
Juyin juya halin Musulunci ya samar da sabon daidaito ta hanyar kafa ma’auni na kasa da kasa tare da kafa kasa mai cin gashin kanta da ta ‘yantar da kanta daga wadanda suke juya akalar duniya a wancan lokacin wato Amurka da Tarayyar Soviet.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: nasarar juyin juya halin Musulunci juyin juya halin Musulunci ya
এছাড়াও পড়ুন:
Iran tana da hakkin mayar da martani ga Isra’ila : Sanarwar Ma’aikatar harkokin waje
Ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ta ce mayar da martani ga gwamnatin Isra’ila hakki ne na shari’a ga Iran kamar yadda doka ta 51 ta kundin tsarin mulkin MDD ta tanada.
Da farko dai ma’aikatar ta mika ta’aziyyar shahadar wasu kwamandoji da jami’an kasar Iran a harin da Isra’ila ta kai wa kasar.
“Hare-haren da gwamnatin sahyoniyawan ta kai wa Iran sun sabawa doka ta 4 sakin layi na 2 na kundin tsarin mulkin majalisar dinkin duniya a matsayin wani mataki na wuce gona da iri kan Jamhuriyar Musulunci ta Iran, kuma Iran tana da hakki na shari’a na halal ta mayar da martani kan wannan zalunci kamar yadda yake a cikin sashe na 51 na kundin tsarin mulkin majalisar dinkin duniya.
Sojojin Jamhuriyar Musulunci ta Iran ba za su yi kasa a gwiwa ba wajen kare al’ummar Iran da dukkan karfinsu.”
“Jamhuriyar Musulunci ta Iran a matsayinta na mamba a Majalisar Dinkin Duniya, tana mai jaddada wajibcin kwamitin sulhu na majalisar dinkin duniya na daukar matakin da ya dace wajen tunkarar matsalar zaman lafiya da tsaro na kasa da kasa, sakamakon wuce gona da iri da gwamnatin sahyoniyawan take yi wa Iran.
“Dukkan kasashe mambobin Majalisar Dinkin Duniya, musamman na shiyya da na Musulunci, da ‘yan gwagwarmaya, da dukkan duniya ana sa ran nan take za su yi Allah-wadai da wannan aika-aika da kuma daukar matakin gaggawa da hadin gwiwa don tinkarar wannan kasada mai hatsarin gaske wadda ko shakka babu ta nuna yadda zaman lafiya da tsaro a duniya ke cikin wata babbar barazana da ba a taba ganin irinsa ba.”
Iran, ta kuma babu shakka wannan danyen aikin da Isra’ila ta aikata ya samu sahalewar Amurka, don haka a cewar Tehran, Amurka na da hannu a wannan hare haren na Isra’ila.