Kwamandan dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran ya jaddada cewa: Kungiyar Hamas duk da iyakantaccen kayan yakinta ta kalubalanci gwamnatin ‘yan sahayoniyya

Kwamandan dakarun kasa na Dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran Birgediya Janar Morteza Miryan ya jaddada cewa: Kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hamas ta kalubalanci gwamnatin mamayar ‘yan sahayoniyya da suke samun goyon bayan Amurka da kasashen Yamma duk da iyakantaccen kayan yakin da ta mallaka na kare kai.

Birgediya Janar Miryan ya ce a cikin jawabinsa a wajen bikin tunawa da shahidan harin “Wal-Fajir 8” da aka gudanar a lokacin tunawa da shahidan lardin Alborz da ke yammacin birnin Tehran: A lokacin yakin da aka yi na shekara ta 1980 zuwa shekara ta 1988), yana cewa; A lokacin yakin sun ga yadda gwamnatin Saddam na Iraki ta mallaki dukkan nau’o’in makamai, amma kuma al’ummar Iran suka tsaya tsayin daka wajen yaki da ta’addanci.

Yayin da yake nuni da laifuffukan da yahudawan sahayoniyya suke yi a yankunan Falastinu da suka mamaye, Birgediya Janar Miryan ya ce: Duniya ta taimaka wa ‘yan sahayoniyya ‘yan mamaya, kuma dukkanin tsarin makaman sararin samaniyya suna hannunsu, amma kungiyar Hamas ta tsaya tsayin daka da karfinta.

Janar Miryan ya kara da cewa: A yayin harin daukan fansa na “Alkawarin Gaskiya na 1 da na 2, Iran ta tabbatar da cewa: Kashi 85 cikin 100 na makamai masu linzaminta sun kai ga inda aka saita su.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Yi Allah Wadai Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Mata

Ma’aikatar harkokin wajen Iran ta yi kakkausar suka ga sabbin takunkuman da Amurka ta kakabawa kasarta

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Ismail Baqa’i, ya yi kakkausar suka kan matakin da Amurka ta dauka na kakabawa wasu gungun mutane, hukumomin shari’a da jiragen ruwa masu alaka da makamashi da man fetur na Iran sabbin takunkumi.

Baqa’i ya gwada rashin amincewar Iran da bakar siyasar Amurka da na ‘yan sahayoniyya musamman farmakin da Amurka da gwamnatin sahayoniyya suka kaddamar na baya-bayan nan kan kasar Iran, yana mai bayyana kakaba takunkumin a matsayin baya da wani harumi na doka kawai matakin zalunci ne kan Iran lamarin da ke fayyace kiyayyar Amurka karara kan Iran.

Baqa’i ya kara da cewa: Al’ummar Iran suna sane da mummunar manufar wadannan tsauraran takunkumin da suke da nufin raunana Iran da neman take mata kowane irin hakki, za su tsaya da dukkan karfinsu wajen kalubalantarsu domin kare mutunci da muradunsu.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar ta Iran ya jaddada cewa: Dabi’ar da Amurka take gudanarwa na nuna son kai da kuma bin hanyar da ba ta dace ba da tilastawa wajen cimma haramtattun manufofinta a matakin kasa da kasa, da kuma rashin mutunta tsarin doka da ‘yancin bil Adama, sun yi hannun riga da tushen dokokin kasa da kasa, gami da ka’idar mutunta ‘yancin kasashe da ‘yancin cinikayya tsakanin kasashe, da kuma daukan matakan nuna barazana ga duniya da ba a taba gani ba.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Tawagar Iran Ta Fice A Taron Majalisun Dokokin Kasashen Duniya A Lokacin Jawabin Wakilin Isra’ila July 31, 2025 Kasar Iran Ta Bayyana Gushewar Hasashen Raunin Karfin Sojinta Kuma Ba Zai Dawo Ba July 31, 2025 Sojan Amurka Ya Bada Ruwayar Yadda Sojojin Sahayoniyya Suka Kashe Wani Yaro Balasdine July 31, 2025 Sojojin Yemen Sun Kai Zafafan Hare-Hare Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila Guda Uku   July 31, 2025 Qolibaf: Barin HKI Ta Yi Abinda Taga Dama Ne Yana Karfafa Mata Giwa July 30, 2025 Yunwa Ta Kashe Karin Falasdinawa 7 A Gaza July 30, 2025 Malta Zata Amince da Samuwar Falasdinu a Cikin Watan Satumba Mai Zuwa July 30, 2025 Amurka Ta Ce HKI Ba Zata Fice Daga Kasar Lebanon Ba Sai An Kwance Damarar Hizbullah July 30, 2025 Siriya Da HKI Zasu Gudanar Da Taro A Baku July 30, 2025  Girgizar Kasa Mai Karfi Ta Kada Yankin Kamtashatka Na Kasar Rasha July 30, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Ziyarci Jama’a, Ya Daina Sauraron Gwamnoni — ADC
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Yi Allah Wadai Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Mata
  • Tawagar Iran Ta Fice A Taron Majalisun Dokokin Kasashen Duniya A Lokacin Jawabin Wakilin Isra’ila
  • Jagora: Iran Ta Bayyana Karfinta Da Jajircewarta A Yakin Kwanaki 12 Ga Duniya
  • Xi Ya Yi Kira Da A Yi Azamar Kare Rayukan Al’umma Yayin Da Ake Fuskantar Ibtila’in Ambaliya A Wasu Sassan Kasar Sin
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 5 a sabon hari a Alkaleri
  • Manjo Janar Musawi: Ko Kadan Ba Mu Yarda Da Amurka Ba
  • Araqchi: Iran Zata Mayar Da Martanin Da Ba Zai Yiwu A Boye Ba  Kan Duk Wani Harin Wuce Gona Da Iri Kanta
  • Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa
  • Hamas: HKI Da Amurka Sun Janye Daga Tattaunawa Ne Don Sake Damarar Yaki