HausaTv:
2025-08-15@09:20:30 GMT

Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Shugabannin Hamas A Ziyararsa Doha

Published: 31st, January 2025 GMT

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi da ke ziyara a Qatar ya gana da shugabannin Hamas a inda suka tattauna batun sake gina Gaza.

Tattaunawar a birnin Doha ta hada fitattun jami’an kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas da suka hada da Mohammed Darwish shugaban majalisar tuntuba ta Shura da Khalil al-Hayya babban mai shiga tsakani na kungiyar.

A yayin ganawar, Darwish ya bayyana Operation Al-Aqsa Storm a matsayin wani sabon salo a gwagwarmayar da al’ummar Palastinu ke yi da gwamnatin mamaya.

Ya jaddada cewa yunkurin gwamnatin Isra’ila na raba al’ummar Falasdinu da kasarsu ta hanyar yakin kisan kare dangi da sauran hanyoyi ya ci tura.

Ya nanata cewa al’ummar Falastinu sun ci gaba da dagewa wajen kare hakkinsu da kuma wurare masu tsarki na kasarsu ciki har da masallacin Al-Aqsa.

A nasa banagre ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya jaddada irin goyon bayan da Jamhuriyar Musulunci ta Iran take ba wa gwagwarmayar al’ummar Palastinu, sannan ya yaba da irin jaruntakar da al’ummar Gaza suka yi, lamarin da ya ce ya tona a fili gazawar gwamnatin Isra’ila.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Allah Zai Kunyata Masu Ɗaukar Nauyin ’Yan Ta’adda – Gwaman Zamfara

A yayin ziyarar, Gwamna Lawal ya jajantawa iyalan waɗanda suka rasa ‘yan uwansu tare da tabbatar wa al’ummar yankin ƙudurinsa na tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyi.

 

A nasa jawabin, gwamnan ya yi kakkausar suka ga hare-haren da ’yan bindiga ke kai wa a baya-bayan nan, yana mai cewa da gangan maƙiya ke nufin waɗannan munanan ayyuka don yaɗa tsoro a tsakanin al’umma.

 

“Na ziyarci garin Banga ne domin jajanta wa jama’a game da harin da ‘yan bindiga suka kai a kwanakin baya.

 

“Lokacin da abin takaicin ya faru, na kasance ba na kusa, amma daga samun labarin, na umarci mataimakin gwamna da ya jagoranci wata babbar tawaga domin ziyarar jaje.

 

“A jiya ne na dawo Gusau bayan tafiya, kuma na ga ya dace na fifita ziyarar al’ummar da abin ya shafa a yau.

 

“Ina so in jaddada kudirin gwamnatina na ƙara ƙoƙari wajen yaƙi da ’yan bindiga.”

 

“Allah ya tona asirin waɗanda suke da hannu wajen kai waɗannan munanan hare-hare da kashe-kashen rashin hankali, ya kuma kunyata su. Ina kira ga kowa da kowa da ya dage da addu’a domin kawo ƙarshen duk wani nau’in ta’addanci a jiharmu mai albarka.”

 

Mai Martaba Sarkin Kauran Namoda, Dakta Sunusi Ahmad, a madadin jama’a, ya yaba wa ƙoƙarin Gwamna Lawal na ɗaukar matakan gaggawa kan matsalolin da suka shafi tsaro.

 

“Waɗannan ziyarce-ziyarcen abin yabo ne ga al’ummar da abin ya shafa da kuma ƙaramar hukumar Kauran Namoda, kuma muna godiya, Allah ya ci gaba da yi maka jagora.”

 

Gwamnan ya kuma yi alƙawarin inganta ababen more rayuwa kamar hanyoyin sadarwa, wutar lantarki, ruwan sha, da ayyukan wayar salula a cikin al’ummomin da abin ya shafa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Yi Tsokaci Kan Furucin Netanyahu Game Da Kafa “Babbar Kasar Isra’ila’
  • Allah Zai Kunyata Masu Ɗaukar Nauyin ’Yan Ta’adda – Gwaman Zamfara
  • Ministan Harkokin Wajen Masar Ya sake Ganawa da Aragchi Da Kuma Gorossy
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Lokaci Ya Yi Da Za A Daina Kakaka Takunkumi Da Ba Dace Ba Kan Kasashe
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: A Lokaci Ya Yi Da Za A Daina Kakaka Takunkumi Da Ba Dace Ba Kan Kasashe
  • Kungiyar SSANU Ta Ba Gwamnatin Taraba Wa’adin Sati Biyu Akan Kudaden Albashin Da Ba A Biya Ba.
  • Ministocin Harkokin Wajen Kasashe 27 Ne Sun Bukaci HKI Ta Kawo Karshen Hana Abinci Shiga Gaza
  • Iran Tace Ma’aikatar Harkokin Waje Kasarce Take Kula Da Lamuran Makamacin Nukliyar Kasar
  • Nijeriya ta sake ƙulla alaƙar tsaro da Isra’ila
  • Ministan Harkokin Wajen Iraki Ya Bukaci Zaman Tattaunawa Tsakanin Kungiyar Larabawan Yankin Tekun Gulf Da Iraki Da Kuma Iran