HausaTv:
2025-05-01@02:28:21 GMT

Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Shugabannin Hamas A Ziyararsa Doha

Published: 31st, January 2025 GMT

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi da ke ziyara a Qatar ya gana da shugabannin Hamas a inda suka tattauna batun sake gina Gaza.

Tattaunawar a birnin Doha ta hada fitattun jami’an kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas da suka hada da Mohammed Darwish shugaban majalisar tuntuba ta Shura da Khalil al-Hayya babban mai shiga tsakani na kungiyar.

A yayin ganawar, Darwish ya bayyana Operation Al-Aqsa Storm a matsayin wani sabon salo a gwagwarmayar da al’ummar Palastinu ke yi da gwamnatin mamaya.

Ya jaddada cewa yunkurin gwamnatin Isra’ila na raba al’ummar Falasdinu da kasarsu ta hanyar yakin kisan kare dangi da sauran hanyoyi ya ci tura.

Ya nanata cewa al’ummar Falastinu sun ci gaba da dagewa wajen kare hakkinsu da kuma wurare masu tsarki na kasarsu ciki har da masallacin Al-Aqsa.

A nasa banagre ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya jaddada irin goyon bayan da Jamhuriyar Musulunci ta Iran take ba wa gwagwarmayar al’ummar Palastinu, sannan ya yaba da irin jaruntakar da al’ummar Gaza suka yi, lamarin da ya ce ya tona a fili gazawar gwamnatin Isra’ila.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnati Ta ƙaddamar Da Sabon Shafin Intanet Don Inganta Sayayya A Tsakanin Ma’aikatunta 

Ministan ya ce sabon gidan yanar na intanet zai taimaka wajen shawo kan matsalolin da suka daɗe suna dagula harkokin sayayya a gwamnati, kamar yadda ake fama da rashin ingantattun tsare-tsare, ƙarancin ƙwararru da rashin tsarin horaswa na dindindin.

 

Ya ce: “Ƙaddamar da wannan sabon shafin ba kawai cigaba ba ne a fannin fasaha; wata babbar hanya ce ta sauya fasalin aiki gaba ɗaya wadda ke magance manyan ƙalubale a tsarin sayen kaya na gwamnati, irin su cikas da ke yawan faruwa, rashin ingantattun hanyoyin sayayya, ƙarancin ma’aikatan da suka dace, da kuma rashin ingantaccen tsarin gina ƙwarewa.

 

“Waɗannan matsaloli sun daɗe suna hana a yi amfani da dukiyoyin gwamnati yadda ya kamata tare da kawo cikas ga cigaban tattalin arziki gaba ɗaya a ƙasar nan.”

 

Ya ce wannan sabon tsari zai bai wa jami’an sayayya damar samun horo, takardun shaida, da kuma damar yin aiki da ƙwarewa, daidai da matakin duniya.

 

Idris ya ce: “Za a tabbatar da cewa mu jami’an gwamnati muna sayen kaya ba kawai bisa doka ba, har ma ƙwararru ne kuma masu iya gogayya a matakin duniya.”

 

Idris ya yaba wa Darakta-Janar na BPP, Dakta Adebowale Adedokun, bisa jajircewa da hangen nesan sa wajen inganta tsarin sayayya a Nijeriya.

 

Ya ce wannan gidan yana hujja ce ta jajircewar sa wajen ganin an sabunta tsarin sayayya a ƙasar nan.

 

Ministan ya kuma buƙaci ‘yan ƙasa da su fahimci cewa sabon gidan yanar ba kawai don gwamnati ba ne, har ma wata hanya ce da za su iya amfani da ita wajen neman ingantattun ayyuka da gaskiya.

 

“Don haka ina kira ga dukkan hukumomi da jami’an gwamnati da su rungumi wannan shiri gaba ɗaya, kuma ina kira ga kafafen yaɗa labarai, musamman, da su taimaka wajen yaɗa amfanin sa da kuma sa ido kan yadda ake aiwatar da shi,” inji shi.

 

Cikin waɗanda suka halarci taron akwai Shugabar Ma’aikatan Gwamnatin Tarayya, Misis Didi Esther Walson-Jack; Ministan Kuɗi kuma Ministan Tsare-tsaren Tattalin Arziki, Mista Wale Edun; Ministan Ilimi, Dakta Tunji Alausa; Ministar Harkokin Mata, Hajiya Imaan Sulaiman-Ibrahim; Shugaban NDLEA, Birgediya Janar Buba Marwa (rtd); da Darakta-Janar na FRCN da NTA, Dakta Mohammed Bulama da Kwamared Abdulhamid Dembos.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati Ta ƙaddamar Da Sabon Shafin Intanet Don Inganta Sayayya A Tsakanin Ma’aikatunta 
  • Amurka ta sake laftawa wasu kamfaninin mai na Iran takunkumi
  • Nazarin CGTN: Ana Kara Bayyana Rashin Gamsuwa Da Sabuwar Gwamnatin Amurka Daga Ciki Da Wajen Kasar
  • Rashin tsaro: Gwamnan AbdulRahman Ya Gana Da Sarakuna Masu Daraja Ta Daya A Jihar Kwara 
  • An Fara Baje Kolin Kayakin Da Ake Kerawa A Iran Tare Da Taron Iran Da Afirka Karo Na Uku
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jadadda Cewa: Duk Wani Harin Wuce Gona Da Iri Kan Iran Zai Fuskanci Mayar Da Martani
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Ci Gaba Da Killace Gaza Da Kashe Mutane, Laifi Ne Da Ba A Taba Yin Irinsa Ba
  • Tawagar Jami’ai Da ‘Yan Kasuwar Ta Tunusiya Ta Gana Da Mataimakin Shugaban kasar Iran
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Tattauana Da Shugaban Hukumar IAEA
  • Takht Ravanji: Iran Ba Za Ta Taba Yin Tattaunawa Akan Dakatar Da Tace Sanadarin Uranium Ba