Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Jaddada Bukatar Bunkasa Alakarta Da Kasar Qatar
Published: 31st, January 2025 GMT
Ministan harkokin wajen Iran ya jaddada aniyar Iran na bunkasa alaka da kasar Qatar a dukkan fannoni
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya yi nuni da kyakkyawar alakar da ke tsakanin Iran da Qatar, yana mai jaddada aniyar gwamnatin Jamhuriyar Musulunci ta Iran na bunkasa alaka da kasar Qatar a fannoni daban daban.
Wannan ya zo ne a yayin ganawar da ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya yi a birnin Doha a jiya Alhamis, tare da fira ministan Qatar kuma ministan harkokin wajen kasar Sheikh Mohammed bin Abdulrahman Al- Thani.
Taron ya tattauna batutuwa da dama da suka shafi bangarorin biyu, da suka hada da ci gaban huldar dake tsakanin kasashen biyu, da kuma ci gaban yankin, musamman a fagen Falasdinawa bayan yarjejeniyar tsagaita bude wuta, da kuma yanayin siyasar kasar Lebanon bayan zaben shugaban kasa da fira minista.
Tattaunawar ta ta’allaka ne kan keta yarjejeniyar tsagaita bude wuta da yahudawan sahayoniyya suka yi, da kuma abubuwan da suke faruwa a kasar Siriya, sun kuma tattauna tare da yin musayar ra’ayi kan yadda kasashen biyu ke ba da goyon baya ga ‘yancin kai, kwanciyar hankali da kuma ‘yancin yankin kasar Siriya.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: harkokin wajen
এছাড়াও পড়ুন:
An Yi Wa Yara Sama Da Miliyan Biyu Allurar Rigakafin Mashaƙo Da Sankarau A Zamfara
A cewar Salahudeen, Ranar Yaƙi da Cutar Polio ta Duniya muhimmiyar dama ce ta faɗakar da jama’a kan barazanar da cutar shan-inna ke haifarwa ga rayuwar al’umma da tattalin arziki, tare da sake duba nasarori da kalubalen da ake fuskanta.
Ya ce haɗin kai tsakanin gwamnatin jihar da kungiyoyin bunkasa lafiya — musamman Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) — ya taimaka matuƙa wajen cimma wannan gagarumar nasara.
“Gwamna Dauda Lawal ya ayyana dokar ta-baci a bangaren lafiya, kuma hakan ya zame ginshiqin da ya taimaka wajen samun tallafi, goyon baya da isassun ma’aikata don tabbatar da an kai rigakafi ko’ina,” inji shi.
Dekta Salahudeen ya kara da cewa WHO, UNICEF, Chigari, Sultan Foundation da Salina Foundation sun taka rawar gani wajen taimakawa jihar ta isa ga dukkan al’ummomi, ciki har da yankunan da ke da wahalar kaiwa.
Ya ce, waɗannan ƙungiyoyi sun samar da tallafin kudi, kayan aiki, horo ga ma’aikatan lafiya, da kuma goyon baya wajen aiwatar da rigakafi a kananan hukumomi 14 na jihar.
Daga cikin manyan nasarorin da aka samu, a cewar shi, akwai damar kai rigakafi har ma zuwa yankunan Fulani makiyaya da wuraren da ake gani a matsayin “hard-to-reach”, baya ga tallafin jami’an tsaro da ya taimaka wajen baje kolin ayyukan rigakafi cikin kwanciyar hankali.
“An samu damar ziyarar dukkan yankuna, har da na noma da kiwo, inda muka ga cewa ba zai yuwu mu bar kowane yaro a baya ba,” inji Salahudeen.
Ya ce gwamnatin jihar za ta ci gaba da hada karfi da kungiyoyin hadaka, domin tabbatar da kawar da shan-inna baki daya, tare da cigaba da karfafa wayar da kan jama’a kan muhimmancin rigakafi.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA