HausaTv:
2025-06-15@06:34:00 GMT

Iran Za Ta Kara Bunkasa Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Kasashen Eurasia

Published: 31st, January 2025 GMT

Mataimakin shugaban kasar Iran na farko Mohammad Reza Aref ya jaddada muhimmancin karfafa hadin gwiwar tattalin arziki da kasuwanci da kasar Kazakhstan a wata ganawa da firaministan kasar Kazakhstan Olzhas Bektenov.

A yayin taron na ranar Alhamis, Aref ya bayyana bukatar samar da karin kwamitocin hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu.

Bayan goron gayyata day a samu a hukumance daga Bektenov, mataimakin shugaban kasar Iran na farko ya isa kasar Kazakhstan a ranar Alhamis domin halartar taron koli na shugabannin gwamnatoci mambobi a kungiyar tattalin arzikin Eurasia (EAEU) da taron Almaty Digital Summit 2025, wanda aka shirya gudanarwa daga ranar 31 ga watan Janairu zuwa 1 ga Fabrairu.

Iran wadda a baya-bayan nan ta samu matsayin mamba mai sanya ido a kungiyar EAEU, na neman kara zurfafa alaka da kungiyar a bangarori na tattalin arziki.

EAEU, wacce aka kafa a cikin 2015, ta ƙunshi Rasha, Belarus, Kazakhstan, Kyrgyzstan, da Armeniya, kuma tana da niyyar habaka haɗin gwiwar tattalin arziki ta hanyar hadaddiyar kasuwa don musayar kayayyaki, ayyuka a bangaren gine-gine da sauransu.

Aref ya jaddada dangantakar al’adu tsakanin Iran da Kazakhstan, yana mai nuni da yuwuwar fadada hadin gwiwa a fannin yawon bude ido da mu’amalar al’adu.

Ya kuma mika goron gayyata ga Bektenov don halartar taron kolin Caspian mai zuwa, wanda aka shirya gudanarwa a Tehran a karshen watan Fabrairu.

Da yake bayyana ci gaban da Iran ta samu a fannin fasahar sadarwa, Aref ya bayyana shirye-shiryen Tehran na raba gwaninta kan fasahohin da ke tasowa tare da kasashe makwabta.

A nasa bangaren, Bektenov ya taya Iran murnar zagayowar ranar juyin juya halin Musulunci tare da jaddada aniyar kasar Kazakhstan na karfafa alakar kasashen biyu ta hanyar inganta kwamitocin hadin gwiwa.

Iran da Kazakhstan a tarihi sun kulla alaka mai karfi, tare da moriyar makamashi, sufuri, da kasuwanci.

Matsakaicin yanayin ƙasa na Iran yana ba Kazakhstan damar shiga tashar jiragen ruwa na kudanci, yana sauƙaƙe hanyoyin kasuwanci kamar Hanyar Sufuri ta Arewa-Kudanci. Sabanin haka, zama memba na EAEU na Kazakhstan yana baiwa Iran kofar shiga kasuwannin tsakiyar Asiya.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasar Kazakhstan

এছাড়াও পড়ুন:

Mulkin Tinubu ya fi kowane muni tun bayan dawowar mulkin farar hula — Dalung

Tsohon Ministan Matasa da Wasanni, Solomon Dalung, ya ce shekara biyu da Bola Ahmed Tinubu ya yi a matsayin shugaban ƙasa sun fi kowane lokaci muni tun bayan dawowar mulkin dimokuraɗiyya a ƙasar.

Yayin da yake magana da BBC a ranar Dimokuraɗiyya da Najeriya ke cika shekaru 26 tana mulkin farar hula, Dalung ya ce ba wani abin arziƙi da talaka ya amfana da shi daga wannan gwamnati.

An kama ’yar Najeriya da laifin safarar ɗalibai 15 a Australia Abin da muke da shi a Najeriya ba cikakkiyar dimokuraɗiyya ba ce — Fayemi

Ya ce: “Kawai abin da talaka ya samu daga gwamnatin Tinubu shi ne tsadar rayuwa, yunwa, wahala da matsalar tsaro.”

Ya zargi gwamnatin da cewa cire tallafin man fetur ba tare da shiri ba, kuma hakan ya jefa mutane cikin ƙuncin rayuwa.

“Talakawa na mutuwa saboda yunwa, amma idan an tambayi Shugaba Tinubu, sai ya ce bai yi nadamar cire tallafin ba,” in ji Dalung.

Gwamnatin Tinubu dai ta ce ta cire tallafin ne domin hana wasu tsiraru ci gaba da cin gajiyarsa da kuma bunƙasa tattalin arziƙin ƙasa.

Amma Dalung ya ce gwamnatin ba ta talaka ta ke ba: “Idan ba canza motoci da jirage da gina sabon gida ga mataimaki ba, to babu wani abu da talaka ya gani.”

Dalung ya ce dimokuraɗiyya na cikin mawuyacin hali tun zuwan Tinubu, ya zargi gwamnati da kama waɗanda ke sukar ta da kuma sayen abokan hamayya wajen komawa APC.

“Mun ga yadda ake kama ‘yan gwagwarmaya saboda kawai sun faɗi ra’ayinsu. Kuma wasu na komawa jam’iyyar APC bayan an saye su,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa gwamnati na barazana ga ci gaban ƙasa idan ba a gyara lamarin ba.

Dalung, ya ce duk da rahoton Bankin Duniya da ke cewa tattalin arziƙin Najeriya na bunƙasa, bai yarda ba.

“Ta yaya za ku ce tattalin arziƙin da ke cikin matsin lamba yanzu yana bunƙasa? Wannan fa ba gaskiya ba ce.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Shaida Gamsuwa Da Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya
  • An Samu Babban Canji Kan Tsarin Ciniki A Tsakanin Sin Da Afirka
  • Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Na Kara Habaka Daga Manyan Tsare-Tsare Zuwa Matakai Na Ainihi
  • Taron Koli Na Sin Da Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu Zai Ingiza Manufar Kara Dunkulewar Sassan Yankin
  • Nijeriya Na Kan Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arziki Da Dawo Da Martabar Ƙasa — Ministan Yaɗa Labarai
  • Bin Hanya Daya Da Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Muhimmin Mataki Ne Na Ba Da Tabbaci Ga Huldar Ciniki Da Tattalin Arzikin Sin Da Amurka
  • Mulkin Tinubu ya fi kowane muni tun bayan dawowar mulkin farar hula — Dalung
  • Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN: An Yi Kira Ga Amurka Da Ta Cimma Daidaito Da Sin Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya
  • Iran ta caccaki kudurin IAEA wanda ta ce yana cike da siyasa
  • An Bude Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Afirka A Changsha