Na farko, manufofi da ka’idojin kundin mulkin MDD su kasance tushen ka’idojin dangantakar kasa da kasa, kuma jigon tsarin shari’a na duniya.

Na biyu, dole ne dokokin duniya su mutunta bambancin al’adu da tsare-tsaren shari’a na kasashen duniya, tare da tabbatar da cewa dukkannin kasashe na da matsayi iri daya, kuma ya zama dole a karfafawa kasashe masu tasowa gwiwar yin magana.

Na uku, daidaiton ‘yancin kai ya kasance tushen shari’a ta zamani a duniya.

Na hudu, nuna biyayya ga yarjejeniyoyin kasa da kasa, wata babbar ka’ida ce wajen aiwatar da shari’a a duniya, kuma dole ne dukkannin kasashe su cika alkawuransu bisa aminci da gaskiya.

Na biyar, dole ne kasashe su gaggauta tsara dokoki a sabbin fannonin da sabbin bangarorin tsaro, don samar da tsarin hadin gwiwa da shugabancin duniya a wadannan bangarori, ta yadda za su biya bukatu da kuma magance matsalolin da suka dace da bukatun kasashe.

Na shida, warware rikice-rikice ta hanyar zaman lafiya wata babbar ka’ida ce ta shari’ar duniya, kuma neman sulhu daya ne daga cikin hanyoyin da kundin mulkin MDD ta kayyade na magance rikice-rikice. (Amina Xu)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Xi Ya Taya Kim Jong Un Murnar Cikar Jam’iyyar WPK Shekaru 80 Da Kafuwa October 10, 2025 Daga Birnin Sin An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal October 9, 2025 Daga Birnin Sin Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025 October 9, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Mutuwar Sheikh Dahiru Bauchi Babban Rashi Ne Ga Kasa Baki Daya- Shugaba Tinubu

Daga Bello Wakili

Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya karɓi labarin rasuwar Sheikh Dahiru Usman Bauchi cikin alhini da jimami.

Fitaccen malamin da ke Bauchi ya rasu ne a ranar Alhamis 27 ga watan Nuwamban 2026, yana da shekaru 101.

Shugaban Ƙasan ya yi jimamin rasuwar jagoran Darikar Tijjaniyya, yana bayyana shi a matsayin ginshiƙin ɗabi’a wanda ya sadaukar da rayuwarsa wajen koyarwa da wa’azi.

Shugaba Tinubu ya ce rashinsa babban rashi ne ba ga iyalansa da dimbin mabiyansa kaɗai ba, har ma ga ƙasa baki ɗaya.

Shugaban Ƙasa ya tuna da albarka da goyon bayan da ya samu daga marigayi Sheikh Dahiru Bauchi a lokacin yakin zaɓen 2023.

“Sheikh Dahiru Bauchi malami ne, uba, mai cike da natsuwa da hikima. A matsayinaa na mai wa’azi kuma masani kan tafsirin Alƙur’ani Mai Girma, yana da’awar zaman lafiya da tsoron Allah. Rasuwarsa ta bar babban gibi,” in ji Shugaban Ƙasa.

Shugaba Tinubu ya yi ta’aziyya ga mabiyan Shehun a ci da wajen ƙasa  bisa wannan babban rashi.

Haka kuma ya ja hankalinsu da su girmama sunansa ta hanyar bin koyarwarsa ta zaman lafiya, ƙarfafa dangantakarsu da Allah, da kuma kasancewa masu taushin zuciya ga jama’a.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mutuwar Sheikh Dahiru Bauchi Babban Rashi Ne Ga Kasa Baki Daya- Shugaba Tinubu
  • Mutuwar Sheikh Dahiru Bauchi Babban Rashi Ne Ga Kasa Baki Daya
  • An Zabi JMI A Cikin Majalisar Zartarwan Ta Hukumar Yaki Da Makaman Guba Ta Duniya CWC
  • Andrea Thompson ta zama mace mafi ƙarfi a duniya
  • Aljeriya Tayi Kira Da A Dakatar Da Israila Game Da Hare-haren Da Take Kaiwa
  • Tukur Mamu ya karbi N50m daga kuɗin fansar harin jirgin kasan Kaduna – DSS
  • Aljeriya Ta Bukaci Kasashen Duniya Su Dauki Mataki Don Kawo Karshen Ta’asan HKI A Yankin Asiya Ta Kudu
  • Faduwar Darajar Kuɗi Na Kara Tsananta Kalubale Ga Kotunan Shari’a — CJN
  • Gwamna Namadi Ya Gabatar da Kasafin Naira Biliyan 900 ga Majalisa
  • Abbas Arakci Ya Yi Gargadi Akan Abin Zai Biyo Bayan Keta Dokokin Duniya Da “Isra’ila” Take Yi A Cikin Wannan Yankin