Na farko, manufofi da ka’idojin kundin mulkin MDD su kasance tushen ka’idojin dangantakar kasa da kasa, kuma jigon tsarin shari’a na duniya.

Na biyu, dole ne dokokin duniya su mutunta bambancin al’adu da tsare-tsaren shari’a na kasashen duniya, tare da tabbatar da cewa dukkannin kasashe na da matsayi iri daya, kuma ya zama dole a karfafawa kasashe masu tasowa gwiwar yin magana.

Na uku, daidaiton ‘yancin kai ya kasance tushen shari’a ta zamani a duniya.

Na hudu, nuna biyayya ga yarjejeniyoyin kasa da kasa, wata babbar ka’ida ce wajen aiwatar da shari’a a duniya, kuma dole ne dukkannin kasashe su cika alkawuransu bisa aminci da gaskiya.

Na biyar, dole ne kasashe su gaggauta tsara dokoki a sabbin fannonin da sabbin bangarorin tsaro, don samar da tsarin hadin gwiwa da shugabancin duniya a wadannan bangarori, ta yadda za su biya bukatu da kuma magance matsalolin da suka dace da bukatun kasashe.

Na shida, warware rikice-rikice ta hanyar zaman lafiya wata babbar ka’ida ce ta shari’ar duniya, kuma neman sulhu daya ne daga cikin hanyoyin da kundin mulkin MDD ta kayyade na magance rikice-rikice. (Amina Xu)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Xi Ya Taya Kim Jong Un Murnar Cikar Jam’iyyar WPK Shekaru 80 Da Kafuwa October 10, 2025 Daga Birnin Sin An Jinjinawa Tallafin Kamfanonin Sin Ga Tsarin Bunkasa Masana’antun Senegal October 9, 2025 Daga Birnin Sin Masu Kallon Fina-Finai Na Sin Sun Gamsu Da Fina-Finan Da Aka Gabatar A Lokacin Hutun Bikin Murnar Ranar Kafuwar Sabuwar Kasar Sin Ta 2025 October 9, 2025

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

AIG Zubairu Ya Umurci ‘Yan Sanda a Kwara Su Ninka Kokarinsu Don Karfafa Tsaro

Daga Ali Muhammad Rabi’u 

Babban Mataimakin Sufeton ‘Yan Sanda mai kula da shiyya ta 8, da ke Lokoja, AIG Abubakar Zubairu, ya bukaci jami’an ‘yan sanda a Jihar Kwara da su ninka kokarinsu wajen karfafa hadin kai da kuma zurfafa dangantaka tsakanin ‘yan sanda da al’umma.

A wata sanarwa da jami’ar hulda da jama’a ta rundunar ‘yan sanda, SP Adetoun Ejinre-Adeyemi ta fitar, ta ce AIG Zubairu  ya yi wannan kira yayin ziyarar aiki da ya kai hedikwatar rundunar ‘yan sanda ta Jihar Kwara da ke Ilorin.

Sanarwar ta yaba wa Gwamna AbdulRahman AbdulRazaq bisa goyon bayan da yake bai wa rundunar ‘yan sanda da kuma kudaden da gwamnatinsa ke fitarwa domin inganta tsaro.

Haka kuma, ta yi kira da a ci gaba da hadin kai, musamman ta fuskar tallafin kayayyakin aiki da kuma karfafa hulda da al’umma, domin kara inganta ayyukan rundunar.

Sanarwar ta kuma yaba wa jami’ai da ma’aikatan rundunar bisa kwarewa, ladabi da jajircewarsu wajen gudanar da ayyuka.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Babban Taron Kawancen Sin Da Afirka Ya Nuna Hadin Gwiwa Kan Gudanar Da Tsarin Shugabancin Duniya Na Bai-Daya
  • Adadin Ma’adanin “Colbat” Da DRC Ta Bai Wa Duniya Ya Kai Ton 1,000
  • Kalubalantar Ka’idar “Kasar Sin Daya Tak A Duniya” Tamkar Wasa Da Wuta Ne
  • Wasu kasashen duniya sun nuna damuwa game da tsarin mulkin bayan yakin Gaza
  • Kotu Ta Yanke Wa Mutum 4 Hukuncin Kisa Kan Kashe Wani Makanike A Kano
  • An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu
  • Faransa: An Fara Shari’ar Shugaban ‘Yan Tawayen DRC Bisa Laifuna Akan Bil’adama
  • Almayadin Ta Sami Rahoton Hukumar Makamashin Ta Duniya  ( IEA)  Aka Cewa Iran Tana Aiki Da Dukkanin Ka’idoji
  • MDD ta yi gargadi game da hadarin yunwa a wasu sassa na duniya
  • AIG Zubairu Ya Umurci ‘Yan Sanda a Kwara Su Ninka Kokarinsu Don Karfafa Tsaro