Aminiya:
2025-10-13@13:33:05 GMT

’Yan Najeriya miliyan 60 na fama da taɓin hankali – Likita

Published: 10th, October 2025 GMT

Wani Likitan ƙwaƙwalwa a Asibitin Neuropsychiatric Aro, a Abeokuta, Jihar Ogun, Dokta Emmanuel Abayomi ya ce kimanin mutane miliyan 60 ne ke fama da taɓin hankali a halin yanzu.

Ya yi wannan jawabin ne a ranar Juma’a a Abeokuta a wajen wani taron ƙarawa juna sani da Ƙungiyar likitoci ta NAS ƙarƙashin Ƙungiyar masu ruwa da tsaki ta ƙasa ta shirya domin tunawa da ranar kiwon lafiyar ƙwaƙwalwa ta duniya ta bana.

Ɗan Majalisa ya nemi ɗaukar mataki kan dorinar ruwa a Gombe ’Yan sanda sun ceto mutum 3 da aka sace a Kano da Kaduna

Shirin da Ash Montana Deck tare da haɗin gwiwar Atlantis, Americana 1 da Longhorn Deck suka yi wanda ya ja hankalin ‘yan sanda da sauran jami’an tsaro a jihar.

Da yake bayani game da “Samar da kayan kiwon lafiyar ƙwaƙwalwa a cikin yanayin agajin gaggawa,” Abayomi ya bayyana damuwa game da ƙaruwar matsalolin ciwon taɓin hankali a tsakanin ‘yan Najeriya.

Da yake ambaton Ƙididdigar Hukumar Lafiya ta Duniya WHO, masanin likitancin ya ce ɗaya daga cikin mutane takwas na fama da matsalar taɓin hankali.

Sai dai a Najeriya Abayomi ya ce adadin ya fi haka inda aka ƙiyasta kimanin ‘yan ƙasar miliyan 60 ne ke fama da matsalar taɓin hankali.

“A Najeriya, adadin ya haura, a gaskiya kimanin ’yan Najeriya miliyan 60, bisa ga ƙididdigar baya-bayan nan, suna fama da matsalar taɓin hankali.

Kuma idan aka dubi adadin ƙidayar ’yan ƙasar zuwa miliyan 200 ko miliyan 240, wannan  na nuna ɗaya cikin mutum biyar ko ɗaya cikin mutane shida da ke da matsalar lafiyar ƙwaƙwalwa.

“Don haka, yana da yawa kuma abin damuwa ne a Najeriya,” in ji shi.

Wadanda suka halarci taron tare da likitan kwakwalwa

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Likitan ƙwaƙwalwa taɓin hankali da matsalar

এছাড়াও পড়ুন:

Haramcin Haƙar Ma’adanai: Majalisa Za Ta Kawo Ƙarshen Asarar Dala Biliyan 9 Duk Shekara

Bugu da kari, an rufe shafukan hakar ma’adanai haramtacce 98 a fadin kasar.

 

“An kiyasta cewa Nijeriya na asarar kusan Dala biliyan 9 a kowace shekara sakamakon haramtacciyar hakar ma’adanai. Wannan sata ta albarkatunmu da ya kamata ta bunkasa kasarmu ta wuce kima, kuma lokaci ya yi da za a kawo karshensa,” in ji Abdulraheem.

 

A cewar sa, kwamitin na da alhakin hana asarar kudaden shiga, tabbatar da gaskiya da adalci a harkokin hakar ma’adanai, da tabbatar da cewa dukiyoyin ma’adanin kasar suna ba da cikakken gudunmawa ga ci gaban tattalin arziki.

 

“Yayin da muke ci gaba, daya daga cikin manyan manufofin wannan kwamitin shi ne hana asarar kudaden shiga da haramtacciyar hakar ma’adanai da ayyukanta ke haifarwa, wanda ba wai kawai ke satar kudaden asusun kasa ba, har ma yana hana bunkasar ayyukan hakar ma’adanai na halal wadanda za su iya ba da gudunmawa mai yawa ga cikakken kudin shiga na cikin gida na kasa (IGR).

 

“Ta hanyar tsauraran kulawa da tsare-tsare, za mu karfafa hanyoyin bibiyar kudaden shiga kuma mu tabbatar cewa duk fa’idojin da ke tattare da bangaren hakar ma’adanai na Nijeriya sun shiga asusun gwamnati kai tsaye, ba tare da a sata ta hanyar haramtacciyar hakar ma’adanai ba.

 

“Haka kuma, batun laifuka da lalacewar muhalli da ke da alaka da haramtacciyar hakar ma’adanai yana da muhimmanci. Wadannan ayyuka ba kawai suna kara rashin tsaro ba ne, har ma suna haifar da gurbatar hanyoyin ruwa, lalata dazuzzukanmu, da tilasta kwashe al’ummomi masu rauni daga gidajensu. Wannan lamari ne na gaggawa na kasa wanda ya zama dole a tunkare shi kai tsaye,” in ji shi kari.

Yana mai jaddada cewa majalisar kasa za ta yi duk mai yiwuwa ba tare da wasa ba, ya ce kwamitin yana tsaye kafada da kafada kan ikonsa na kundin tsarin mulki da ‘yan Nijeriya suka ba shi.

Yayin da yake tabbatar da shirin majalisar wajen daukar mataki mai karfi kan duk wanda aka same shi da hannu a haramtacciyar hakar ma’adanai, Shugaban Kwamitin ya yi kira ga ‘yan kasa da su bayyana masu laifi a cikin al’ummominsu don amfanin kasa baki daya.

“Mun kuduri aniyar cika wajibcinmu na sa ido kamar yadda kundin tsarin mulkin Tarayyar Nijeriya ya tanadar, wajen fallasa cin hanci da rashawa a kowace hanya, dakile miyagun ayyuka, da tabbatar da cewa albarkatunmu ana amfani da su ne domin amfanin duk ‘yan Nijeriya.

“Ta hanyar wannan tsauraran sa ido ne za mu kawar da cutar haramtacciyar hakar ma’adanai daga kasarmu, mu kare muhalli, da kuma tabbatar da jin dadin ‘yan kasa. Ta amfani da ikon da aka ba mu, za mu gudanar da bincike, tattara hujjoji, da bayar da shawarwarin da za su dawo da hankali da gaskiya a bangaren hakar ma’adanai na Nijeriya,” in ji shi kari.

Game da Kamfanin Karafa na Ajaokuta (Ajaokuta Steel Company), ya tabbatar cewa gwamnatin Tinubu ta nuna jagoranci da kuma shirin farfado da wannan dukiyar kasa.

“Tsawon shekaru da dama, Kamfanin Karafa na Ajaokuta ya kasance alamar bai cika burinsa ba. Ko ma dai yaya, ina alfahari da cewa yanzu yana kan hanyar cika ainihin burinsa. Gwamnatin yanzu ta nuna kwazo na siyasa da ba a taba gani ba wajen farfado da wannan muhimmin dukiyar kasa.”

“Wannan yana bayyana ne a cikin nadin wani kwararren dan kasa domin jagorantar farfado da kamfanin, mataki da ke ba mu fata ga makomar masana’antar karfe ta Nijeriya.

Tare da shirye-shiryen Ajaokuta na samun nasara, muna kallon hakan ba kawai a matsayin sauyin tattalin arziki ba, har ma a matsayin ginshiki ga masana’antu, samar da ayyukan yi, da dogon lokacin bunkasar tattalin arziki,” in ji shi.

Wakilin (NSCDC), Kwamandan Ma’aikatan Tsaron Hakar Ma’adanai, Attah Onoja, ya tabbatar wa kwamitin da cikakken hadin kai daga jami’ai.

Onoja ya bayyana cewa tun bayan kaddamar da aikin Mining Marshals a watan Maris 2024, NSCDC ta kama masu hakar ma’adanai haramtacce sama da 500, inda kimanin 270 daga cikinsu ke fuskantar shari’a a halin yanzu.

“Ina so in bayyana cikin gaggawa cewa sama da masu hakar ma’adanai 500 an kama su a lokacin wannan aikin. Kuma daga cikin wannan adadi, kimanin 270 suna fuskantar shari’a a yanzu kamar yadda muke magana a yau.

“Jami’an NSCDC, a matsayin hukuma, tana tabbatar wa wannan Kwamitin girmamawa da cikakken hadin kai da goyon baya a duk inda ya zama dole domin tabbatar da cewa an cimma wannan muhimmin burin tattalin arziki,” in ji shi.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano October 10, 2025 Labarai Yadda Za A Magance Yawaitar Malaman Da Ba Su Cancanta Ba A Nijeriya – TRCN October 10, 2025 Labarai ACF Ta Yi Zargin Shiri Na Musamman Don Rusa Matatar Man Dangote October 10, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Soja ya kashe matarsa, ya hallaka kansa a Jihar Neja
  • Kungiyar Malaman Jami’o’in Najeriya ASUU ta Shiga Yajin Aiki
  • Shugaban Kasar Najeriya Ya Yi  Afuwa Ga Wasu Mutanen Da Kotuna Su Ka Hukunta
  • Maryam Sanda na cikin waɗanda Tinubu ya yi wa afuwa
  • ’Yan sanda sun ceto mutum 10 daga hannun ’yan bindiga a Kaduna
  • Tarihin Hassan Usman Katsina (1)
  • Wasu Daga Cikin Muhimman Alamomin Ciwon Kansa
  • Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 9, Sun Ƙwato Naira Miliyan 5 A Borno
  • Haramcin Haƙar Ma’adanai: Majalisa Za Ta Kawo Ƙarshen Asarar Dala Biliyan 9 Duk Shekara