Aminiya:
2025-10-13@13:37:50 GMT

Ma’aikatan jami’a sun yi zanga-zanga a Jami’ar Bayero

Published: 9th, October 2025 GMT

Mambobin Ƙungiyar Manyan Ma’aikatan Jami’o’i ta Najeriya (SSANU) da Ƙungiyar Ma’aikatan da ba Malamai ba (NASU) reshen Jami’ar Bayero Kano (BUK), sun gudanar da zanga-zangar lumana.

Mambobin sun yi zanga-zangar ne a ranar Alhamis kan riƙe wasu haƙƙokinsu da suka zargi gwamnatin tarayya da yi.

Zanga-zangar da aka gudanar a cikin harabar jami’ar ta biyo bayan umarnin shugabannin ƙasa na ƙungiyoyin biyu, bayan ƙarewar wa’adin mako guda da ƙarin makonni biyu da suka ba gwamnatin tarayya.

Masarautar Nafada ta ƙaddamar da dokar rage tsadar aure Najeriya ta tafka asarar tiriliyan 14.5 sakamakon rikicin Boko Haram – UNICEF

Da yake jawabi ga manema labarai yayin zanga-zangar, Mataimakin Shugaban SSANU na Ƙasa shiyyar Arewa maso Yamma, Kwamared Sabo Balarabe Wudil, ya ce matakin ya zama dole sakamakon gazawar gwamnatin tarayya wajen cika alkawuran da suka dade ana jira.

“Mun fito zanga-zanga ne saboda an yi watsi da bukatunmu na tsawon lokaci. Gwamnatin tarayya ta hana mu albashin watanni biyu da aka dakatar a lokacin yajin aikin 2022, ta gaza aiwatar da yarjejeniyar da muka cimma da ita a 2009, sannan ta yi watsi da biyan bashin albashinmu daga watan Janairu zuwa Disamban 2023,” in ji shi.

Wudil ya kuma koka kan rashin sakin Naira biliyan 40 na alawus-alawus ɗin da suke bi, inda ya ce gwamnati ta biya biliyan 10 ne kacal daga cikin biliyan 50 da aka amince da su tun 2022.

Ya ƙara da cewa, duk da yarjejeniyoyin fahimtar juna da aka rattaba hannu da gwamnati, ba a aiwatar da ko ɗaya daga cikinsu ba.

“Mu ƙungiyoyi ne masu son zaman lafiya. Muna so zaman lafiya ya wanzu, amma muna bukatar a yi mana adalci. Wannan zanga-zangar mataki ne na farko. Idan gwamnati ta gaza ɗaukar mataki ta hanyar share mana hawaye, shugabannin ƙasa na ƙungiyoyinmu za su yanke shawarar mataki na gaba,” in ji shi.

Da take karɓar takardar ƙorafin ma’aikatan a madadin Shugaban Jami’ar, Mataimakiyar Shugaban Jami’ar mai kula da Bincike da Ci gaba, Farfesa Amina Mustapha, ta tabbatar wa da ƙungiyoyin goyon bayan jami’ar.

“Ina so in tabbatar muku cewa Shugaban Jami’ar yana tare da ku a wannan fafutukar. Za mu isar da ƙorafinku ga hukumomin da suka dace,” in ji ta.

Aminiya ta rawaito cewa masu zanga-zangar na ɗauke da alluna masu rubuce-rubuce daban-daban kamar “Ku girmama ma’aikatan da ba malamai ba”, “Mun yi aiki, kun ki biyan mu. Ku saki albashin watanni biyu”, “Bashin albashi na 25%/35% haƙƙinmu ne” da “Ba ma son wani alkawari, a dauki mataki yanzu”, da sauransu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jami ar Bayero Kano zanga zangar

এছাড়াও পড়ুন:

Ɗan Majalisa ya nemi ɗaukar mataki kan dorinar ruwa a Gombe

A yayin da ake yawan samun ɓarnar dorinar ruwa a garuruwan Daɗin Kowa da Kupto da Malleri da Wade a yankunan Ƙananan hukumomin Kwami da Yamaltu Deba a Jihar Gombe ta kai ga samun asarar amfanin gona da rayuka.

Hakan ne ya sa Ɗan majalisar tarayya mai wakiltar mazaɓar Yamaltu/ Deba a Jihar Gombe Inuwa Garba ya gabatar da ƙudiri a gaban zauren Majalisar Wakilai ta tarayya domin neman ɗaukar matakin gaggawa kan ɓarnar dorinar ruwa.

’Yan sanda sun ceto mutum 3 da aka sace a Kano da Kaduna Kwastam ta kama buhunan lalatacciyar fulawa 10,000 ana ƙoƙarin shigo da ita Najeriya

Inda ya ce dorinar na yi wa manoma ɓarna sosai da ke janyo asarar rayuka, dukiyoyi da lalacewar amfanin gona a yankunan da abin ya shafa.

Inuwa Garba ya bayyana hakan ne, a shafinsa na Facebook cewa, dorinar ruwan ta zama babbar matsala ga manoma da al’ummomin waɗannan yankuna inda ake samun girgizar tattalin arziki sakamakon lalacewar gonaki, lalata hanyoyi da kuma rasa muhallin zama.

Ya ce, wannan ƙudiri na da nufin kawo mafita ta dindindin domin kare rayukan mutane, kiyaye dukiyoyin su da kuma tabbatar da ci gaban noman rani da damina, wanda shi ne tushen rayuwar yawancin mazauna yankin.

Ya buƙaci Gwamnatin Tarayya da ta Jihar Gombe, tare da hukumomin kula da ruwa da su kai ɗauki cikin hanzari ta hanyar bayar da tallafi, gyaran madatsun ruwa da kuma samar da hanyoyin rage haɗarin dorinar a nan gaba.

A ƙarshe, ya miƙa saƙon ta’aziyya ga iyalai da ‘yan uwa na waɗanda suka rasa rayukansu a ibtila’in dorinar ruwa yana roƙon Allah Ya jikan mamatan da rahama, tare da ba iyalansu haƙuri, juriya na rashin da suka yi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ASUU ta tsunduma yajin aikin mako 2
  • Jami’ar MDD: Taron Kolin Matan Duniya Ya Zo Daidai Lokacin Da Ya Dace
  • Kungiyar Malaman Jami’o’in Najeriya ASUU ta Shiga Yajin Aiki
  • ASUU za ta fara yajin aikin mako 2 daga ranar Litinin
  • Sarkin Morocco Ya yi Magana Tun Bayan Barkewar Zanga-zanga A Kasar .
  • Wakiliyar CMG Ta Zanta Da Farfesa Jeffrey Sachs Na Jami’ar Columbia
  • Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci’ Yan Nijeriya Su Rika Sayen Kayan Da Aka Sarrafa A Gida
  • ’Yan bindiga sun kashe Civilian JTF 8 a Zamfara
  • Guguwar Ritaya Na Barazana Ga Ayyukan Hukumar Kwastam Yayin Da Jami’ai 825 Za Su Yi Ritaya
  • Ɗan Majalisa ya nemi ɗaukar mataki kan dorinar ruwa a Gombe