Aminiya:
2025-10-13@13:35:11 GMT

Najeriya ta tafka asarar tiriliyan 14.5 sakamakon rikicin Boko Haram – UNICEF

Published: 9th, October 2025 GMT

Asusun Kula da Yara na Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF) ya kiyasta cewa Najeriya ta yi asarar kimanin dala biliyan 10, kwatankwacin Naira tiriliyan 14.5 sakamakon rikicin Boko Haram a yankin Arewa maso Gabas. Wakiliyar UNICEF a Najeriya, Wafaa Saeed, ta bayyana hakan a Maiduguri ranar Laraba yayin ƙaddamar da wani shirin farfaɗo da rayuwar yara da rikici ya shafa ta hanyar ba su horo da tallafi.

Falasdinawa na murna da tsagaita wutar hare-haren Isra’ila a Gaza Majalisa ta yi watsi da zargin Amurka na yi wa Kiristoci kisan gilla a Najeriya An wakilta Saeed ta hannun Manajan Kare Yara na UNICEF, Shah Mohammad Khan, inda ta ce rikicin da ya daɗe ya rage girman tattalin arzikin ƙasar, ya kuma lalata samun kuɗin shigar iyalai da matasa a yankin. Ta ce, “A cewar wani bincike da UNICEF ta gudanar a shekarar 2024, asarar tattalin arzikin da rikici ya haifar a Arewa maso Gabas ya kai dala biliyan 10 cikin shekaru goma da suka gabata. “Rikici ba wai kawai ya raunana tattalin arzikin ƙasa ba ne, har ma ya durƙusar da samun kuɗin shiga da damar aiki ga iyalai da matasa. “Tsawon lokaci, yara da matasa da dama, musamman ’yan mata, ba su samu damar koyon sana’o’i ko cika burinsu ba,” in ji ta. Wakiliyar ta UNICEF ta kuma nuna damuwa kan yadda shekaru da dama na rikici a yankin suka kasance da munanan laifuka kan yara, ciki har da sace-sace da cin zarafi ta hanyar jima’i, tare da cewa rasa damar samun abin dogaro da kai ya shafi ci gaban ɗan adam sosai. A cewarta, sabon shirin farfaɗo da rayuwa da aka ƙaddamar yana da nufin tallafa wa yaran da rikicin ya shafa ta hanyar koyar da su sana’o’i da kuma ba su kariya ta musamman. “Yanzu haka, yara 1,033, maza 567 da mata 466, na amfana da horon sana’o’i a cibiyoyi daban-daban a Maiduguri, Bama, Biu, Damboa da Konduga,” in ji ta. Saeed ta bayyana cewa ana koyar da yaran sana’o’in da za su iya amfani da su a rayuwa kamar dinki, fasahar sadarwa, gyaran motoci, ƙera takalma da sana’ar kafinta. Wafa Saeed ta kuma ce fiye da yara 1,000 ana sa ran za su amfana da shirin a kowace shekara, inda za su samu ƙwarewar da za ta buɗe musu ƙofofin aiki da rayuwa mai ɗorewa. Kwamishinan Ilimi, Kimiyya da Fasaha na Jihar Borno, Abba Wakilbe, ya yaba wa UNICEF da sauran abokan hulɗarta irin su UNDP, IOM da UNODC, kan goyon bayan da suka bayar a shirin. “Ina so in gode wa UNICEF musamman bisa taimakon da ta ba mu a lokutan da muka shiga mawuyacin hali,” in ji Wakilbe.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Arewa maso Gabas Boko Haram

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan Najeriya miliyan 60 na fama da taɓin hankali – Likita

Wani Likitan ƙwaƙwalwa a Asibitin Neuropsychiatric Aro, a Abeokuta, Jihar Ogun, Dokta Emmanuel Abayomi ya ce kimanin mutane miliyan 60 ne ke fama da taɓin hankali a halin yanzu.

Ya yi wannan jawabin ne a ranar Juma’a a Abeokuta a wajen wani taron ƙarawa juna sani da Ƙungiyar likitoci ta NAS ƙarƙashin Ƙungiyar masu ruwa da tsaki ta ƙasa ta shirya domin tunawa da ranar kiwon lafiyar ƙwaƙwalwa ta duniya ta bana.

Ɗan Majalisa ya nemi ɗaukar mataki kan dorinar ruwa a Gombe ’Yan sanda sun ceto mutum 3 da aka sace a Kano da Kaduna

Shirin da Ash Montana Deck tare da haɗin gwiwar Atlantis, Americana 1 da Longhorn Deck suka yi wanda ya ja hankalin ‘yan sanda da sauran jami’an tsaro a jihar.

Da yake bayani game da “Samar da kayan kiwon lafiyar ƙwaƙwalwa a cikin yanayin agajin gaggawa,” Abayomi ya bayyana damuwa game da ƙaruwar matsalolin ciwon taɓin hankali a tsakanin ‘yan Najeriya.

Da yake ambaton Ƙididdigar Hukumar Lafiya ta Duniya WHO, masanin likitancin ya ce ɗaya daga cikin mutane takwas na fama da matsalar taɓin hankali.

Sai dai a Najeriya Abayomi ya ce adadin ya fi haka inda aka ƙiyasta kimanin ‘yan ƙasar miliyan 60 ne ke fama da matsalar taɓin hankali.

“A Najeriya, adadin ya haura, a gaskiya kimanin ’yan Najeriya miliyan 60, bisa ga ƙididdigar baya-bayan nan, suna fama da matsalar taɓin hankali.

Kuma idan aka dubi adadin ƙidayar ’yan ƙasar zuwa miliyan 200 ko miliyan 240, wannan  na nuna ɗaya cikin mutum biyar ko ɗaya cikin mutane shida da ke da matsalar lafiyar ƙwaƙwalwa.

“Don haka, yana da yawa kuma abin damuwa ne a Najeriya,” in ji shi.

Wadanda suka halarci taron tare da likitan kwakwalwa

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rikicin kabilanci: Mutane 2 sun mutu, wasu 7 sun jikkata a Jigawa
  • Ta’addanci: Ana Fuskantar Ƙarancin Man Fetur A Mali Sakamakon Datse Hanyoyin Shiga Bamako
  • Kungiyar Malaman Jami’o’in Najeriya ASUU ta Shiga Yajin Aiki
  • Yaƙi Da Boko Haram: An Kashe Sojoji 2,700 A Shekara 12 – Janar Irabor
  • Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya
  • Dalilin IFAD Na Zuba Naira Biliyan 16 A Fannin Noma A Benuwe
  • Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci’ Yan Nijeriya Su Rika Sayen Kayan Da Aka Sarrafa A Gida
  • ’Yan Najeriya miliyan 60 na fama da taɓin hankali – Likita
  • Sojoji sun mutu yayin da Boko Haram ta kai hari sansanin soji a Borno
  • Haramcin Haƙar Ma’adanai: Majalisa Za Ta Kawo Ƙarshen Asarar Dala Biliyan 9 Duk Shekara