Aminiya:
2025-11-27@21:57:40 GMT

Najeriya ta tafka asarar tiriliyan 14.5 sakamakon rikicin Boko Haram – UNICEF

Published: 9th, October 2025 GMT

Asusun Kula da Yara na Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF) ya kiyasta cewa Najeriya ta yi asarar kimanin dala biliyan 10, kwatankwacin Naira tiriliyan 14.5 sakamakon rikicin Boko Haram a yankin Arewa maso Gabas. Wakiliyar UNICEF a Najeriya, Wafaa Saeed, ta bayyana hakan a Maiduguri ranar Laraba yayin ƙaddamar da wani shirin farfaɗo da rayuwar yara da rikici ya shafa ta hanyar ba su horo da tallafi.

Falasdinawa na murna da tsagaita wutar hare-haren Isra’ila a Gaza Majalisa ta yi watsi da zargin Amurka na yi wa Kiristoci kisan gilla a Najeriya An wakilta Saeed ta hannun Manajan Kare Yara na UNICEF, Shah Mohammad Khan, inda ta ce rikicin da ya daɗe ya rage girman tattalin arzikin ƙasar, ya kuma lalata samun kuɗin shigar iyalai da matasa a yankin. Ta ce, “A cewar wani bincike da UNICEF ta gudanar a shekarar 2024, asarar tattalin arzikin da rikici ya haifar a Arewa maso Gabas ya kai dala biliyan 10 cikin shekaru goma da suka gabata. “Rikici ba wai kawai ya raunana tattalin arzikin ƙasa ba ne, har ma ya durƙusar da samun kuɗin shiga da damar aiki ga iyalai da matasa. “Tsawon lokaci, yara da matasa da dama, musamman ’yan mata, ba su samu damar koyon sana’o’i ko cika burinsu ba,” in ji ta. Wakiliyar ta UNICEF ta kuma nuna damuwa kan yadda shekaru da dama na rikici a yankin suka kasance da munanan laifuka kan yara, ciki har da sace-sace da cin zarafi ta hanyar jima’i, tare da cewa rasa damar samun abin dogaro da kai ya shafi ci gaban ɗan adam sosai. A cewarta, sabon shirin farfaɗo da rayuwa da aka ƙaddamar yana da nufin tallafa wa yaran da rikicin ya shafa ta hanyar koyar da su sana’o’i da kuma ba su kariya ta musamman. “Yanzu haka, yara 1,033, maza 567 da mata 466, na amfana da horon sana’o’i a cibiyoyi daban-daban a Maiduguri, Bama, Biu, Damboa da Konduga,” in ji ta. Saeed ta bayyana cewa ana koyar da yaran sana’o’in da za su iya amfani da su a rayuwa kamar dinki, fasahar sadarwa, gyaran motoci, ƙera takalma da sana’ar kafinta. Wafa Saeed ta kuma ce fiye da yara 1,000 ana sa ran za su amfana da shirin a kowace shekara, inda za su samu ƙwarewar da za ta buɗe musu ƙofofin aiki da rayuwa mai ɗorewa. Kwamishinan Ilimi, Kimiyya da Fasaha na Jihar Borno, Abba Wakilbe, ya yaba wa UNICEF da sauran abokan hulɗarta irin su UNDP, IOM da UNODC, kan goyon bayan da suka bayar a shirin. “Ina so in gode wa UNICEF musamman bisa taimakon da ta ba mu a lokutan da muka shiga mawuyacin hali,” in ji Wakilbe.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Arewa maso Gabas Boko Haram

এছাড়াও পড়ুন:

Babban Kwamandan Sojojin Sudan Ya Yi Watsi Da Shirin Trump Na Zaman Lafiya

Shugaban kasar Sudan kuma babban kwamandan sojojin kasar Janar Abdulfattah Alburhan, ya yi watsi da shawarar Amurka ta kawo karshen yaki a kasarsa wanda ya lakume rayukan mutane da dama, ya kuma raba kasar gida biyu a cikin watanni kimani 30 da suka gabata.

Shafin yanar gizo na labarai ‘AfricaNews’ ya nakalto Burhan yana fadar haka a ranar Lahadi jim kadan bayan ganawarsa da tawagar kasar Amurka wacce ta gabatar masa da shawarar, ya kuma bayyana ta a matsayin mafi munin shawarar tsagaita budewa juna wuta da aka gabatar masa ya zuwa yanzun.   Burhan ya zargi Massad Boulos mai bawa shugaban kasar Amurka a kan al-amuran nahiyar Afirka da da kokarin rusa sojojin kasar Sudan da kuma bawa yan tawaye karkashin jagorancin Amity damar ci gaba da iko da wani daga bangaren kasar.

Burhan ya zargi Amurka da goyon bayan yan tawayen a cikin shawarar da ta gabatar, kuma shawarar ba irin zaman lafiyan da mutanen sudan suke so ba.   Masana suna ganin gwamnatin Amurka da kawayenta wadanda suke goyon bayan yantawaye a duniya musamman a cikin kasashen Larabawa suna son sake raba kasar Sudan ne, kuma sun gabatar da wannan shawarar ce a dai-dai lokacinda suka fahinci cewa gwamnatin kasar tana samun nasara a kan yan tawaye wadanda suke iko da yankin Darfur na yammacin kasar ta Sudan.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka An Gudanar Da Jana’izar Shahidai 300 A Dai-Dai Ranar Shahadar Zahra (s) A Jiya Litinin November 25, 2025 Amurka Da HKI Sun Kawo Karshen Hukumar GHF Mai Raba Abinci A Gaza November 25, 2025 Hamas Ta Ce Keta Hurumin Tsagaita Wutan Da HKI Take Yi Zai Iya Kawo Karshen Tsagaita Wutar November 25, 2025 Gwamnonin Kudu Maso Yammacin Najeriya Sun Ce Lokacin Kafa Yansandan Jihohi Ya Yi November 25, 2025 Hizbullah Ta na Juyayin shahadar Babban Kwamanda Haitham Ali Da Isra’ila Ta Kashe. November 24, 2025 Dubban Alummar Kasar Tunisia Ne Suka Gudanar Da Zanga-zangar Adawa Da Mulkin Kama Karya A Kasar November 24, 2025 Mutane 6 Ne Suka Mutu Sakamakon Harin Kunar Bakin Wake Da Aka Kai A Peshavar Na Kasar Pakistan November 24, 2025 Hamas Tayi Gargadi Game Da Rushewar Yarjejeniyar Bude Wuta Idan Israila Ta ci Gaba Da Kai Hare-Hare   November 24, 2025 Amnesty International Ta Zargi Najeriya Da Gazawa Wajen Kare Rayukan Al’ummarta November 24, 2025 Wakilin MDD Ya Bukaci Goyon Bayan Iran Wajen Tabbatar Da Zaman Lafiya A Yamen November 24, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Faransa, Jamus, Italiya, da Burtaniya sun yi tir da “karuwar rikici” a yammacin kogon jodan
  • Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Kashe Sama da Naira Miliyan 5 Don Tallafawa Shirin AGILE
  • Rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi ta bar babban gibi a Najeriya – Tinubu
  • Rasha A Shirye Take Ta Taimaka Wa Najeriya A Fada Da Ta’addanci
  • Tinubu ya aike wa Majalisar Dattawa sunayen jakadu
  • Jami’an tsaro sun ƙaddamar da shirin murƙushe ’yan bindiga a Kaduna
  • Shugaban Iran: Kasuwar jarin cikin gida sirrin nasarorin gwamnati na tattalin arziki
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Yi Wa Yara Miliyan 1.5 Rigakafin Cutar Shan Inna
  • An ceto ’yan mata 24 d aka yi garkuwa da su a makaranta a Kebbi
  • Babban Kwamandan Sojojin Sudan Ya Yi Watsi Da Shirin Trump Na Zaman Lafiya