Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-11-27@20:36:11 GMT

Za a Yi Aikin Hadin Gwiwa Tsakan KNUPDA Da NSCDC A Kano

Published: 9th, October 2025 GMT

Za a Yi Aikin Hadin Gwiwa Tsakan KNUPDA Da NSCDC A Kano

Hukumar Tsare-tsare da Cigaban Birane ta Jihar Kano (KNUPDA) ta jaddada aniyar ta na karfafa hadin gwiwa tsakanin hukumomi da inganta ci gaban birane ta hanyar hadin gwiwa da hukumar tsaro ta NSCDC.

 

Tawaga daga KNUPDA, karkashin jagorancin Manajan Darakta, Arc. Hauwa Hassan T/Wada, ta kai ziyarar gani da ido hedikwatar hukumar NSCDC da ke Kano a wani bangare na kokarin fahimtar juna da hadin gwiwa tsakanin hukumomi.

 

Da yake jawabi yayin ziyarar, Arc. Hauwa ta bayyana cewa ingantaccen tsare-tsare da ci gaban birane na bukatar hada karfi da karfe da manyan jami’an tsaro domin tabbatar da kare kadarorin gwamnati, tabbatar da doka da oda a cikin babban birni.

 

Ta bayyana irin shirye-shiryen KNUPDA da ke ci gaba da bita da aiwatar da tsare-tsare da nufin inganta tsarin birane, da magance haramtattun gine-gine, da kuma inganta kyawun birnin Kano.

 

Ta kuma bayyana cewa yin aiki da hukumar NSCDC zai kara karfafa bin doka da oda da kuma taimakawa wajen kare ayyukan ci gaba a fadin jihar.

 

A nasa martani, kwamandan hukumar NSCDC na jihar Kano, Mista B. B. Bodinga, ya bayyana jin dadinsa da ziyarar tare da yabawa KNUPDA bisa kokarin da take yi na samar da hadin kai tsakanin hukumomin.

 

Ya kuma ba da tabbacin hukumar ta NSCDC a shirye ta ke na bayar da tallafin tsaro da ya dace da kuma yin aiki tare da KNUPDA domin cimma burin gwamnatin jihar na samar da ci gaban birane cikin tsari da dorewa.

 

Taron ya kuma gabatar da wani zaman tattaunawa inda bangarorin biyu suka tattauna batutuwan da suka dace da juna, da suka hada da kare kadarorin jama’a, aiwatar da ka’idojin tsare-tsare, da dabarun inganta tsaro da bin ka’ida a birane.

 

Rel/Khadijah Aliyu

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: tsare tsare

এছাড়াও পড়ুন:

An buɗe wasu makarantu domin ci gaba da jarawaba a Katsina

Hukumar kula da makarantun firamare da sakandare ta Jihar Katsina ta sanar da sake buɗe wasu makarantu domin ci gaba da jarabawar zangon farko na shekarar karatu.

A wata sanarwa da Jami’in Hulɗa da Jama’a na hukumar, Sani Danjuma Suleman, ya fitar a madadin Shugaban hukumar, ta ce makarantun firamare, sakandiren je-ka-ka-dawo da kuma makarantu masu zaman kansu za su buɗe daga yau Talata domin ci gaba da jarabawar zangon farko.

Sanarwar ta ƙara da cewa, sauran makarantun kwana za su ci gaba da kasancewa a rufe har sai lokacin da hali ya ba da dama.

Aminiya ta ruwaito cewa, a bayan nan ne Gwamnatin Katsina ta rufe makarantun bayan ƙaruwar hare-haren sace ɗalibai da masu garkuwa da mutane suka sake farfaɗowa da su a wasu yankuna.

Gwamnatin ta ce ta ɗauki matakin ne da nufin daƙile matsalar tsaro da kuma sa ido a kan al’amura.

A ƙarshe, hukumar ta roƙi haɗin kan iyaye da masu kula da ɗalibai domin su ci gaba da ba wa shirin goyon baya tare da ƙarfafa ɗaliban su dage da karatu wajen rubuta jarabawar da suke yi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Najeriya : Ana ci gaba da alhinin rasuwar Sheikh Dahiru Usman Bauchi
  • An rantsar da sabon shugaban kasa a Guinea-Bissau bayan juyin mulkin sojoji
  • Gwamna Kefas Ya Bayyana Alhininsa Bisa Rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi
  • Jihar Jigawa Za Ta Rufe Karbar Kudaden Aikin Hajjin 2026 Ranar 24 Ga Watan Disamba
  • Larijani: Hadin gwiwar Iran da Pakistan na taimaka wa zaman lafiya a yankin
  • Kano Pillars ta kawo ƙarshen wasanni 8 ba tare da nasara ba
  • An buɗe wasu makarantu domin ci gaba da jarawaba a Katsina
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 8 a Kano
  • Mali: An Dakatar Da  Aikin Kafafen Watsa Labarun Faransa Biyu A Cikin Kasar Mali
  • Gobarar tankar mai ta ƙone gidaje a Jihar Neja