Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-10-13@13:38:02 GMT

Za a Yi Aikin Hadin Gwiwa Tsakan KNUPDA Da NSCDC A Kano

Published: 9th, October 2025 GMT

Za a Yi Aikin Hadin Gwiwa Tsakan KNUPDA Da NSCDC A Kano

Hukumar Tsare-tsare da Cigaban Birane ta Jihar Kano (KNUPDA) ta jaddada aniyar ta na karfafa hadin gwiwa tsakanin hukumomi da inganta ci gaban birane ta hanyar hadin gwiwa da hukumar tsaro ta NSCDC.

 

Tawaga daga KNUPDA, karkashin jagorancin Manajan Darakta, Arc. Hauwa Hassan T/Wada, ta kai ziyarar gani da ido hedikwatar hukumar NSCDC da ke Kano a wani bangare na kokarin fahimtar juna da hadin gwiwa tsakanin hukumomi.

 

Da yake jawabi yayin ziyarar, Arc. Hauwa ta bayyana cewa ingantaccen tsare-tsare da ci gaban birane na bukatar hada karfi da karfe da manyan jami’an tsaro domin tabbatar da kare kadarorin gwamnati, tabbatar da doka da oda a cikin babban birni.

 

Ta bayyana irin shirye-shiryen KNUPDA da ke ci gaba da bita da aiwatar da tsare-tsare da nufin inganta tsarin birane, da magance haramtattun gine-gine, da kuma inganta kyawun birnin Kano.

 

Ta kuma bayyana cewa yin aiki da hukumar NSCDC zai kara karfafa bin doka da oda da kuma taimakawa wajen kare ayyukan ci gaba a fadin jihar.

 

A nasa martani, kwamandan hukumar NSCDC na jihar Kano, Mista B. B. Bodinga, ya bayyana jin dadinsa da ziyarar tare da yabawa KNUPDA bisa kokarin da take yi na samar da hadin kai tsakanin hukumomin.

 

Ya kuma ba da tabbacin hukumar ta NSCDC a shirye ta ke na bayar da tallafin tsaro da ya dace da kuma yin aiki tare da KNUPDA domin cimma burin gwamnatin jihar na samar da ci gaban birane cikin tsari da dorewa.

 

Taron ya kuma gabatar da wani zaman tattaunawa inda bangarorin biyu suka tattauna batutuwan da suka dace da juna, da suka hada da kare kadarorin jama’a, aiwatar da ka’idojin tsare-tsare, da dabarun inganta tsaro da bin ka’ida a birane.

 

Rel/Khadijah Aliyu

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: tsare tsare

এছাড়াও পড়ুন:

Yanayin Sashen Samar Da Gidaje Na Sin Ya Kara Inganta Tsakanin 2021 Zuwa 2025

Ministan gidaje da raya birane da karkara na kasar Sin Ni Hong, ya ce yanayin sashen samar da gidaje na Sin ya kara inganta tsakanin shekarar 2021 zuwa 2025, yayin aiwatar da manufar raya kasa karo na 14, inda jimillar adadin sayar da sabbin gidaje na kasuwa ya kai fadin sakwaya mita biliyan biyar.

 

Ni Hong, ya bayyana hakan ne a yau Asabar, yayin wani taron manema labarai. A cewarsa, sama da Sinawa miliyan 110 sun amfana daga babban tsarin gyaran tsofaffin gidaje cikin shekarun biyar. Kazalika, tsofaffin gidaje dake unguwanni sama da 240,000 a sassan biranen Sin, sun mori shirin gyaran fuska cikin wa’adin. Don haka gaba daya, yanayin ingancin muhallin biranen Sin ya kara inganta yadda ya kamata. (Mai fassara: Saminu Alhassan)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Tarihin Hassan Usman Katsina (1) October 11, 2025 Daga Birnin Sin An Gudanar Da Taron Hadin Kai Na Raya Albarkatun Kasa Tsakanin Sin Da Mozambique October 11, 2025 Daga Birnin Sin Wakiliyar CMG Ta Zanta Da Farfesa Jeffrey Sachs Na Jami’ar Columbia October 11, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano
  • Ahmed Musa Ya Nemi Afuwar Ƙungiyar 3SC Akan Abinda Ya Faru Da ‘Yan Wasansu A Kano
  • Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Da Shawarwari Hudu A Taron Kolin Mata Na Duniya
  • Yanayin Sashen Samar Da Gidaje Na Sin Ya Kara Inganta Tsakanin 2021 Zuwa 2025
  • An Gudanar Da Taron Hadin Kai Na Raya Albarkatun Kasa Tsakanin Sin Da Mozambique
  • Wakiliyar CMG Ta Zanta Da Farfesa Jeffrey Sachs Na Jami’ar Columbia
  • Li Qiang Ya Halarci Bikin Murnar Cika Shekaru 80 Da Kafuwar Jam’iyyar WPK Ta Koriya Ta Arewa
  • Kungiyoyin Falasdinawa Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Kan Tsagaita Bude Wuta A Gaza
  • Sibil Difens ta cafke mutum 3 kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi a Kano
  • CMG Ya Kaddamar Da Shirin “Dabarun Tallata Kayayyakin Sin” A Tafarkin Gina Kasa Bisa Hadin Gwiwa